Sunday, August 24, 2014

Shugaba Goodluck Jonathan


SHUGABAN KASA GOODLUCK JONATHAN

Shugaban Kasa Dr. Goodluck Jonathan shugaba ne da wata rana zamu tuna shi ta fuskar hakuri da juriya da kuma rauninsa da muke cin moriya a Arewa da Najeriya baki daya. Idan muka yi nazarin yadda karfin mulki na zamani yake tafiya ba'a taba samun shugaba a Najeriya mai juriyar hakuri da sallamawa bangarorin kasa irin Jonathan ba.

Babbar matsalar sa itace Najeriya ta yiwa kwakwalwarsa yawa, kuma bashi da kwarewar tafiyar da mulki sosai, sannan yana da sakaci kan tsaro, da bada damar a hukunta masu laifi. Haka kuma,  wadan da ke kewaye dashi sun fishi wayewa da sanin Shugabanci dan haka suka karkata mulkin kasar zuwa ga bukatar su.

Da zan baiwa Shugaban kasa Shawara da sai nace kada ya tsaya zabe a 2015, ya marawa dan Arewa baya a zaben da yake tafe, amman ya tabbatar Mulki bai kufcewa PDP ba.

YASIR RAMADAN GWALE
24-08-2014

No comments:

Post a Comment