Wednesday, January 29, 2014

Naka Shi Ke Bada Kai

NAKA SHI KE BADA KAI!!!

Naka sai naka, a wani azancin zance da Bahaushe kan yi. Babu shakka abinda Bahaushe ya ce da arziki a garin wasu gara a naku, wannan ya kusa kama da daidai, amma abin fata shi ne a tara arzikin na halal a kuma kashe ta halal. Sau da dama mu 'yan Arewa ko kudu mukan so namu ya samu wani babban mukami a gwamnatin Tarayya tundaga sha'anin Mulki da Tsaro da harkar tattalin arziki da sauransu, ta haka ne kadai muke zaton indararon arziki na iya kwaranyowa zuwa garemu ko ga wasunmu. Ba komai ya sanya da dama yin wannan tunani ko fata ba, face RASHIN ADALCI da ya game ko ina, kasancewar Adalci ya yi karanci a sha'anin tafiyar da mulki, ya sanya yanzu a Najeriya kowa nasa yake fatan ya samu tsakanin Kudu da Arewa ko tsakanin Musulmi da Kirista.

Mun wayi gari, a wani irin mawuyacin lokaci, inda Musulmi basa yin Adalcin da ya kamata akan kansu balle ga wanda ba Musulmi ba, kiristoci basa yin adalci ga Musulmi; haka kuma, 'yan Kudu basa yin Adalci ga 'yan Arewa, suma 'yan Arewan basa yin abinda ya dace ga 'yan kudu. Bisa irin wannan dalili ne ya sanya da dama muke hannu baka hannu kwarya wajen kankane dukkan wasu Madafun iko tsakanin Kudu da Arewa ko tsakanin Musulmi da Kirista a Najeriya. Sau da dama, jama'a, basu cika son ayi adalci a zamantakewa ba, illa a dadada musu ko da za'a cutar da abokin zamansu, babu abinda ya damesu.

A mafi yawancin lokuta, mu 'yan Arewa mukan yi addu'ah da fatan inama ace namu ne ya samu, wasu na yin fatan haka ne dan suna zaton alal akalla zasu samu damar cin moriyar wani arziki wanda nasu yake da ikon tasarrufin akansa. Misali akan hakan, shi ne munyi fatan ace namu ne suka samu Manyan mukamai da suka shafi bangaren harkar Tsaro, dan fatan watakila zamu iya fita daga cikin halin da muke ciki, musamman a yankin Arewa maso Gabas, saboda munyi Imani wadan da suke rike da mukamin a yanzu suna ko in kula da aikinsu, saboda ba al'ummarsu ce ke shiga cikin garari ba, wani abin mamaki akan haka shi ne, bayan rikita rikitar tsaro da ta addabi Arewa maso Gabas, shi ne kuma, wani abin mamaki da ban takaici da kusan ya fi yin kamari a jihar Zamfara sama da kowace jiha, ba komai bane face satar shanu da kashe mutane masu yawan gaske a lokaci guda da kuma ribace mata da kananan yara, da sunan cewa 'yan fashi ne suka aikata.

Wannan abin ya faru a jihar Zamafara ba karo daya ba, ba kuma karo biyu ba. Abin mamaki shi ne shugaban 'Yan Sandan Najeriya gaba daya dan Asalin jihar Zamfara ne, amma duk abinda yake faruwa na daure kai a mahaifarsa yake ta faruwa. Zai zama abin mamaki kwarai da gaske ace 'yan fashi su shiga kauye su kashe mutane 50 ko fiye, su kore shanu wajen dubu goma, amma a kasa ganin koda kurar inda suka shiga balle a kama su! Babu shakka wannan abu ne wanda hankali ba zai dauka ba, babu yadda za'a yi irin wannan shegantakar da sunan fashi da makami amma ace an kasa sanin inda barayin suka shiga da shanun, balle kuma a kama barayin a hukuntasu. Dan Allah wace rana Sufetan 'yan sanda ya yiwa Mahaifarsa a wannan batu?

Irin wannan misalin abin haushin yana da yawa ainun a Arewa. Sau da dama mutanan da muke ganin zasu kare mana martabarmu da mutuncinmu sukan bada mu, ta hanyar yin shakaulatun bangaro da batunmu, babu ruwansu da kulawa da bukatun mutanan da kullum suke yi musu fatan samun wani mukami wanda zasu taimaki al'ummarsu da addininsu da habaka tattalin arzikinsu, tunda yanayin kasar ya nuna cewa babu wani wanda zai iya kare maka mutuncinka da muradunka face sai wanda yake da iko ya kasance naka ne. Duk da haka ba mu yi kasa a guiwa ba, kuma bamu yanke tsammani ba, cewa 'yan Arewa zasu taimakawa yankin Arewa wajen farfadowa nan kusa ko nan gaba. Bama kira ko fatan a dauki hakkin wani a bamu, fatanmu shi ne a yiwa kowane dan kasa Adalci, dan wani wanda baya cikinmu ya samu iko akanmu ya zalunce mu, wannan ba shi ne dalilin da zai bamu damar zalintar wadan da ba mu ba, idan mun sami iko akansu.

Yasir Ramadan Gwale
29-01-2014

Monday, January 27, 2014

Hattara Dai APC Hangen Dala Ba Shiga Birni Bane!!!

HATTARA DAI APC  HANGEN DALA BA SHIGA BIRNI BANE!!!

Kusan yana daya daga cikin abinda da dama suka dinga shakkar faruwarsa, shi ne cewar, wasu Jam’iyyu zasu iya dunkulewa su zama guda daya. Bayan zaben 2011 da jam’iyyun Hamayya, suka sha kashi a hannun jam’iyyar PDP mai mulki, aka shiga fadi tashin ganin hanyar da zata zamewa ‘yan hamayya mafita, domin darkake PDP a Mulkin Najeriya. Lokacin da aka fara batun cewa jam’iyyun ACN da ANPP da CPC zasu cure su dunkule su zama abu guda daya domin a kalubalanci jam’iyyar PDP mai mulki, da dama suka dinga ganin hakan ba abu bane mai yuwuwa, saboda mabanbamtan mutanen da suke cikin jam’iyyun. Amma cikin ikon Allah, wannan al’amari ya tabbata gaskiya, inda duk ‘yan wadancan jam’iyyu suka hakura da bambance bambancen da ke tsakaninsu suka dunkule kowa ya yarda jam’iyyarsa ta saraya domin samar da jam’iyyar Hamayya/Adawa guda daya wadda zata iya kalubanatar PDP a babban zaben badi mai zuwa.

Bayan da aka yi nasarar yin waccan Hadaka da ta samar da Jam’iyyar APC, wacce ake cewa irinta ce karo na farko a tarihin siyasar Najeriya, al’ummar Najeriya ciki da waje suka dinga nuna farin cikinsu da nuna goyon bayansu domin a zahiri ta bayyana cewa da gaske jam’iyyun Hamayya suke don kalubalantar PDP a zaben 2015. Shugabannin APC na riko da kuma jagororin wannan Hadaka sun bazama jihohi inda suka dinga kaiwa ‘yan siyasa da dama caffa domin tafiya tare dan a kauda PDP daga kan karagar Mulkin Najeriya. Wannan ta sanya sabuwar Jam’iyyar APC ta farauci wasu daga cikin Gwamnonin PDP da suke da matsala da jam’iyyarsu ta PDP, aka kuma yi dacen wafto wasu daga cikin ‘ya ‘yan PDP din da suke tayar da kayar baya a cikin jam’iyyar tasu.

Abinda tun farko APC suka kasa yi, ko kuma suka yi sake da shin shi ne batun hada kawunan Sabbin ‘ya ‘yan Jam’iyyar da ko dai suke da ra’ayoyi mabanbamta ko kuma suke tsananin Hamayya da juna. Tunda har wadannan jam’iyyu suka iya yarda su sarayar da Jam’iyyunsu su samar da APC babu shakka abu ne mai sauki su iya zama a kan tebur domin su warware matsalolinsu musamman da wadan da ake ganin akwai Hamayya tsakaninsu, wannan wani janibi ne mai muhimmanci da APC ya kamata ta baiwa kulawa ta musamman tun fil azal, amma sai aka yi shakulatun bangaro da al’amarin har Baraka ta bayyana kamar wata daren sha biyar.

Tun ran-gini tun ran-zane, inji Bahaushe, a lokacin da APC suka fara zawarcin Gwamnonin PDP, suna sane da cewar akwai hamayya tsakanin wadan da aka kafa APC da su, da kuma, wadan da ake kokarin yin zawarci. Sanin kowa ne a Kano akwai Hamayya tsakanin Gwamna Rabiu Kwankwaso da Malam Ibrahim Shekarau; a Sokoto akwai Hamayya tsakanin Gwamna Aliyu Magatakarda Wammako da tsohon Gwamna Attahiru Bafarawa; da kuma Adamawa inda Gen. Buba Marwa ke Hamayya da Gwamna Murtala Nyakko. Duk jagororin APC suna da masaniyar wannan hamayyar, wanda abinda ya kamata a yi tun farko shi ne a san hanyoyin da za’a bi wajen dinke wannan barakar kafin zabarin wadannan Gwamnoni. Amma sai idon jagororin APC ya rufe, inda sun san a jihohin da na fada a sama Akwai Bafarawa da Shekarau da Marwa, amma aka zabi wasu aka kaiwa gwamnonin wadannan jihohi ziyarar zawarci ba tare da ko da sanar da wadannan mutane ba, babu shakka, a Magana ta gaskiya, dole ko waye zaiji babu dadi ace jam’iyyar da kuka bata lokaci  wajen kafawa to zo har jiharka wajen zabarin mutane ba tare da wani ya sanar da kai ba! Abin akwai damuwa da rashin jin dadi, wannan ko da wanda za’a zawarta ba sa hamayya das hi.

Bayan da duk aka yi abinda aka yi, daga baya APC suka fahimci cewar sunyi kuskure, har suka kafa kwamitin da zai zagaya jihohin Kano, Sokoto da Adamawa domin baiwa Malam Shekarau, Bafarawa da Buba Marwa hakuri kan abinda aka yi musu na rashin sanar da su zuwan tawagar APC jihohinsu. Babu shakka, wannan abu ne mai kyau da APC ta yi. Amma kuma daga hakan ba’a yi komai ba, sai aka tsaya a wajen, maimakon a yi amfani da wannan damar wajen tuntubar wadannan mutane wajen ganin yadda zasu iya zama inuwa daya da abokan hamayyarsu a siyasa cikin jam’iyya daya, sai aka yi biris da zancen. Gwamnonin Kano da Sokoto da Adamawa suka ayyana komawa APC ba tare da APC din tana da wani shiri mai karfi a kasa ba wajen ganin ta sasanta ‘ya ‘yanta masu hamayya da juna.

Haka nan, wadannan Gwamnoni suka shigo APC ta sama ba tare da yin wani shiri na karbarsu ba a jihohinsu, da kuma kokarin zaunar da su da abokan hamayyarsu a sasanta su ba, kai kace daman da su aka kafa APC din. Aka yi ta rade-radi game da shigowar wadannan gwamnoni, shugabancin uwar jam’iyyar APC yana ji bai ce ko “bihim” ba akan lamarin, tun kan ya kazance. Aka yi ta turka-turka akan waye ya kamata ya zama jagora ko ba waye ba a wadannan jihohi amma shugabancin jam’iyya yaki yin katabus akai. Har aka zo kan wani mataki da ka iya zamarwa APC mai matukar hadarin gaske a 2015.

A makon da ya gabata Bafarawa wanda daya ne daga cikin jiga-jigan ANPP da suka sarayar da jam’iyyarsu ta ANPP wajen ganin kafuwar APC ya bayyana ficewarsa, amma maimakon a nuna rashin jindadi da damuwa, sai ya zama abin murna ga wasu, ana cewar Allah ya raka taki gona. Da dama suna fadin Da Bafarawa da Shekarau da Buba Marwa ko da su ko babu su APC zata iya cin zabe a jihohin Kano, Sokoto da Adamawa, wannan kam gaskiya ne. Ko babu wadannan Mutane APC tana da yakinin cin zaben shugaban kasa a jihohin, amma abinda akan manta shi ne, tun da aka fara wannan sabani jam’iyya mai Mulki PDP tayi amfani da wannan Baraka wajen kaiwa Malam Shekarau da Bafarawa da Marwa bara, inda take neman su shigo jam’iyyar dan basu damar da aka hanasu a APC. Abinda da dama daga cikin ‘yan APC suke ganin tafi nono fari idan Shekarau da Bafarawa da Marwa har ma da Bolgore suka koma PDP.

Yana da kyau mu sani, ita APC, it ace jam’iyyar Hamayya/Adawa burinta, fatanta, begenta shi ne ta ci zabe. Dan haka duk wata dama da zata iya kawo nakasu daga samun Nasarar APC ya kamata kar a bata kofa ko wace iri ba. Haka kuma, yana da kyau mu sani cewa, ita PDP ba yanzu suka saba cin zabe ba, dan haka duk wasu dabaru na sarari da na boye sun jima da tanadin kayansu. Ita PDP ba sai ta cinye Kano da Sokoto ko Adamawa kanan ta ci zabe ba, kawai abinda suke da bukata shi ne kashi ashirin da biyar (25%) da hukumar zabe ta ce sai jam’iyyar da ta samu a jihohi 23 sannan zata iya cin zaben shugaban kasa. Masu cewar Ko da Shekarau, Bafarawa, Marwa ko babu su APC zata iya cin jihohinsu, amma kuma sun manta cewar wadannan mutane zasu iya kawowa PDP 25% a jihohinsu! Anan matsalar take, domin a 2011 lokacin da ake Murna cewa Buhari ya samu kuri’u Miliyan Biyu a Kano an manta cewa PDP ta samu kashi 25 a kanon. To amma saboda doki da hangen dala, sai wasu suke ganin cewar ficewar Bafarawa da Shekarau da Marwa alheri ce ga APC.

Babu shakka idan APC ta cigaba da kame hannu, ‘ya ‘yanta na halak malak suna zurarewa ba tare da ta rufe bakin daurin ba, to tabbas a zaben 2015 za su sha mamaki. Domin mai gishiri ai baya wasan shiga ruwa da mai goro. Su PDP da yake da gaske suke son tabbata akan Dimokaradiyya, lokacin da Atiku Abubakar da Marigayi Abubakar Rimi suka yi zuciya suka bar jam’iyyar suna zaginta tare da yi mata jafa’I, uwar jam’iyyar bata barsu haka ba, sai da ta kafa kwamati akai ta rarrashinsu har suka hakura suka dawo domin sun tabbatar tafiya da Baraka ba zai zamar musu alheri wajen cin zabe ba. Yana da kyau mu waiwayi baya mu kalli yadda al’amura suka faro da yadda suka karke.

Amma saboda saurin mantuwa da rashin yin karatun ta nutsu sai wasu ke fatan da Shekarau da Bafarawa da Marwa har addu’ah ake musu Allah ya raka taki gona, shin masu addu’ar basa tunanin Allah ya amshi addu’arsu Taki ya isa gona lafiya, ayi shuka tayi yabanya har aci amfaninta? Sannan kuma, tsakanin APC da PDP wa yafi bukatar cin zaben shugaban kasa ido rufe? Na tabbata mai karatu zai yarda da ni cewa APC su ke da bukatar cin zabe ido rufe, shin ya dace su yarda da duk wata Baraka da ka iya nakasta samun nasararsu?

Ni a fahimtata, yanzu ta bayyana cewa babu wata jam’iyya mai tsarki da ta ke da mutanan kirki dari bisa dari, dan haka duk inda mutum ya tsinci kansa yayi kokarin kawo gyara da kyakykyawar niyya kuma gwargwadon ikonsa. Allah yana bamu ladan aikin da muka yi dominsa gwargwadon yadda muka kyautata niyya. Dan haka, yana da kyau APC su sani hangen dala daga nesa ba shi ke nuna an shigo biirni ba, kuma mai ma’di ai shi ke talla . . .!

Yasir Ramadan Gwale
27-01-2014

Saturday, January 25, 2014

Zuwa Ga Sani Aminu Yunusa (Bafille)

SANI AMINU YUNUSA: Ba zan manta lokacin da Sani Aminu Yunusa (Bafille) ya yi kokarin yin fasakwaurina zuwa Kwara House daga Kaduna House ba a lokacin da muke daukin yin Candy. Ba shakka yunkurin da Bafille ya yi na daukeni zuwa Kwara House bai yiwa abokan zamana dadi ba, musamman Umar Jafar (UJ) ya fito karara ya nuna min rashin jin-dadinsa akan yunkurin daukeni daga Kaduna House da Bafille da Malan (Aliyu Hasan) suka yi. Nakan kwana a Kwara House da safe na koma Kaduna House na cigaba da harkoki, Bafille ya nuna min kauna kwarai da gaske musamman a term dinmu na karshe a KARAYE.

Mukan je Kusalla tare mu yi wanki da wanka kuma mu debo ruwa. Ba kuma zan taba mantawa da tafiyar da muka yi ni da Bafille da Malan zuwa 'Yar-Medi zuwa Marori (Kabo) a kafa ba, ba shakka, a lokacin munyi tafiyar cikin jindadi da doki, duk kuwa da angaya mana cewa tafiyar tana da nisa. A garin 'Yar-Medi muka hadu da wani mafarauci inda ya bamu wata ciyawa da ake kira sugar-daji, yace mana indai wannan bawan bishiya yana bakinku kuna taunawa ba zaku gaji ba, daga "yar Medi har kuje Marori a karamar Hukumar Kabo. Bayan da ya bamu wani bararrakakken Zabon daji muka yi kalaci da shi, muka yi masa sallama muka kama hanya, muna tafe muna tauna sugar daji har Allah ya kaimu Marori.

A lokacin da muka je wani waje domin yin tambayar gidan wasu 'yan uwansu Malan, muka ga wani masallaci muka zauna mukai alwala muka yi sallah, a wannan lokacin duk mun manta mun yar da sugar daji. Bayan da muka je wata rumfa kusa da wata karamar tasha, muka samu wata yarinya mai sayar da Alala da Dan-wake, muka sayi ina zaton na Naira Talatin muka maida Yawu, muka ga dare zai yi mana ba tare da mun gane gidan 'yan uwansu Malan ba, mukai tunanin mu koma Kabo mu hau motar da zata maida mu Karaye, amma kuma duk cikinmu babu mai ko ficika, haka nan muke sake yanke shawarar Komawa ta 'Yar-Medi a kafa! Ba shakka mun dandana kudarmu da gajiya, mun koma makaranta a wahale bayan da muka dinga yin d'ane idan munga motar da zata bi hanya (Hitch-hike), haka har muka dawo makaranta bayan dare yayi sosai. Na tabbata Sani Aminu Yunusa (Bafille) da yake Angwancewa a wannan rana ta Asabar 25-01-2014 ba zai manta da wannan lokaci ba. Ina mai amfani da wannan dama wajen taya shi murna da fatan alheri. Ina kuma jan hankalinka ka rike 'yar mutane Amana kasancewarka dan KWANKWASIYYA na san ba zaka yi wasa da kalmar AMANA ba. Allah ya sanya alheri ya bada zaman lafiya.

Naka Yasir Ramadan Gwale
25-01-2014

Sunday, January 19, 2014

Mallam Ibrahim Shekarau: Jagora Na-gari Abin Koyi



MALLAM IBRAHIM SHEKARAU: JAGORA NA GARI ABIN KOYI

Malam Ibrahim Shekarau na daga cikin kalilan din mutane da Allah ya albarkaci 'yan Najeriya da su dan tsarkake dattin da ya gurbata koramar da ta ke gudana a Siyasar Najeriya musamman ta Arewa a wannan lokacin. Ba shakka tarbiyyar Siyasa irin wadda Malam Shekarau yake kokarin dora al'umma akai, ita ce siyasa ta gaskiya da ya kamata kafatanin al'umma su runguma domin fita daga halin kangi da wahala da radadin da ake fama da shi, da kuma maida al'umma cikin hayyacinsu, da saita mutane akan siyasar gaskiya da tsoron Allah. Al'umma, suna cikin halin kishirwar mutane nagari wadan da zasu daidaita musu sahu domin dora su akan hanya dodar wadda zata kaisu zuwa ga tudun mun-tsira, ta fidda A'i daga Rogo ta kuma raba yari da barawo, domin ceto su daga cikin mawuyacin halin da suke ciki na fatara da talauci da jahilci da kuncin tunani da koma baya.

Yana daga cikin bacin tafarkin siyasar wannan lokacin, kokarin tattabar da mugun nufi da cin-dunduniya da karya da yarfe a matsayin ginshikan samun ingatacciyar siyasa. Abinda Malam ke ta fadin tashin ganin an sauyawa al'umma tunani daga mummuna zuwa kyakykyawa, irin tsarin siyasar da su Malam Aminu Kano suka bar mana gado da wasu ke neman boye irin wannan muhimmin kayan gadon dan kada idon magada ya kai kansa, abar jama'a na ta funfum-fundum cikin mummunan tafarkin siyasa. Alhamdulillah, da Allah ya albarkaci wannan al'umma tamu da mutane irinsu Malam Ibrahim Shekarau domin saita tunanin mutane da shagaltar da su zuwaga Siyasa ingantacciya wadda idan akan yi katarin samun tsarkakkiyar niyya, na iya zamarwa mutum samun babban rabo a ranar sakamako.

A cikin shirin da ya gabatar kai-tsaye daga gidan Radiyan Tarayya Na Kaduna, ranar Lahadi 19 ga watan janairu, ya nunawa al'umma irin kwarewarsa wajen tafiya bisa tsarin siyasa na gaskiya, wadda ba ta dauke da wani mugun nufi ko bita da kulli. Malam yayi bayanai masu ratsa zukata da nuna kwarewa wajen sanin me ake nufi da siyasa ta gaskiya kamar yadda dumbin al'umma suka saurara. Ba shakka irin wadannan bayanai na tsage gaskiyar al'amura yadda suke ba tare da kari ko ragi ba, domin fitar da al'umma daga cikin rudun da wasu rudaddu suke neman jefa mutane a ciki. Irin wadannan bayanai da zasu kauda dukkan wasu shakku da jita-jita su ne irin bayanan da ya kamata managartan 'yan siyasar wannan zamanin su mayar da hankalinsu a kai.

Haka kuma, Malam Shekarau ya kunyata masu son assasa wutar gaba tsakaninsa da abokan Hamayyarsa a siyasa da son tabbatar da cewa lallai sai an tsananta gaba da kiyayya tsakaninsa da 'yan siyasa, Malam ya nuna shi dattijo ne, inda yaki baiwa wannan yunkuri gurbi a tsarin siyasarsa. Hakika, Malam Ibrahim Shekarau wata kyauta ce ta musamman da Allah ya yiwa al'ummar Najeriya da ita. Allah ya cigaba da yi masa jagora, ya kareshi da dukkan kariyarsa.

Yasir Ramadan Gwale
19-01-2014

Wednesday, January 15, 2014

Idan An Girma Asan An Girma!!!

IDAN AN GIRMA ASAN AN GIRMA

A shekarunsa yayi 'da da ni dan ba shakka ko bai haifeni ba, to, ya haifi kanina. Sau da dama idan na ga sakonsa ko comments dinsa yana zagina sai abin ya bani mamaki, domin mutum mai shekaru irin nasa ya tsaya yana zagin mutum kamar Yasir Ramadan Gwale mutumin da ya kusa haifa, zagi irin na batsa wanda ko yaro kaji yana yi ka kauda kanka dan kunya amma babba da shi a she babban kwabo ne shi, girma gareshi babu hankali da tunani irin na manyan mutane. Ko kusa zaginsa bai taba damuna ko ya bata min rai ba, domin dubunsa sun zageni a facebook ko tankawa banyi ba balle naji haushi, illa iyaka mamakin da nake yadda ya yasar da sheakrunsa a banza yana zagi da aibanta Yaron da ya kusan haifa. Ban taba mayar masa da martanin zagi ba kamar yadda yake yi min, saboda ko babu komai ni ina girmama farin gashi da tarin shekaru ko da kuwa na banza da wofi ne irin nasa, ballantana kuma mu AHLUSSUNNAH bamu da tarbiyyar duddurawa mutane ashariya. Duk da sanin cewa zagi ba shi da makaranta kowa zai iya yinsa idan yaga dama.

Amma idan na tuna yadda suke zagi da aibata Sahabbai da Matan Manzon Allah SAW, sai na ce to kuma waye Yasir idan ya zageni, mutumin da ya zagi mutanan da suka fi Ubansa da uwarsa da dukkan danginsa daraja! Dan haka, ni zai yi min dadi a raina ace iyayena yake zagi akan ya zagi Sahabbai da Matan Manzon Allah SAW.

Kamar yadda kowane mai hankali ya sani ne, zagi da cin mutunci da aibantawa ai na mutumin da ba shida wata hujja ne, ba shi da wata mafita illa ya yi zagi ya tayar da kura, wanda a ganinsa hakan ita ce dabara ta karshe da ta rage masa wadda zai karkatar da hankalinka daga zahirin gaskiya zuwa wani abu daban.

Wannan mutum ba kowa bane illa wani da ake kira Ashiru Nana. Ina masa fatan Allah ya shiryeshi ya ganar da shi hanya ta gaskiya. Allah ka nuna mana gaskiya gaskiya ce ka bamu ikon binta, ka nuna mana karya karya ce ka bamu ikon guje mata.

YASIR RAMADAN GWALE
15-01-2014