Sunday, January 31, 2016

Ya Kamata Gwamnatin Nigeria Da Jihohi Suyi Doka Kan Amfani Da Amsa Kuwwa


YA KAMATA GWAMNATIN NIGERIA DA JIHOHI SU YI DOKAR AMFANI DA LASIFIKA (AMSA KUWWA)

A gaskiya d'armu yayi yawa matuk'a ta yadda muke amfani da sunan Addini Sana'a domin cutar da al'. Zance na gaskiya yadda mutane ke amfani da Amsa Kuwwa barkatai babu wata doka abin ba tsari. A tsari na zamantakewa da Addinin Musulunci ya koya mana, bai ce muyi amfani da addini ko hanyar neman abinci wajen cutar da abokan zaman mu ba.

Haka kurum da sunan neman Abinci mutum ya mak'alawa motarsa k'atuwar Amsa Kuwwa ya shigo cikin aunguwa yana tallar magani. Wani abin damuwa shi ne, galibi tallan da ake na maganin gargajiya da Amsa Kuwwa batsa ce tsagwaron ta, masu tallar ke yi. Ba shakka akwai bambancin tarbiyyar magana tsakanin garuruwanmu, maganganun mu sun bambanta, wata maganar da Bakatsine zai fad'a a garinsu ba wanda zai kalle shi, a Kano idan ya fada sai ta zama abin takaici.

Haka nan, wata maganar da Basakkwace zai fad'a a garinsu a jinjina masa, idan yazo Kano ya fad' sai kaji magana ce me nauyin gaske da bata kamata mutum mai hankali ya fad'a ba. Duk da haka yana da kyau, idan mutumin Katsina ko Sokoto zai yi talla a Kano to ya kamata ya kiyaye da Kalmomi irin na mutan Kano. Wannan na daga cikin neman ilimin yin sana'a kafin yinta.

Zaka ji takaici matuk'a a lokacin da kake zaune da iyalanka da safe ko da daddare wani mai tallar magani daga Katsina ko Sokoto yazo unguwar ku ya tsmotarsa watakila kusa da gidan, yana ta bayanin maganin karfin mazakuta. Suna maganganu gatsal babu sayawa babu sakaye, a sanya mutum jin kunya cikin yaransa.

Lallai ya kamata hukumomi su yi doka kan irin wad'annan masu tallar maganin masu yawo da katuwar Amsa Kuwwa cikin unguwanni da sunan Sana'a. Ba daidai bane dan mutum na saida magani sai ya dinga fad'a yana kwatanta yadda Al'aurar Namiji take idan yasha maganinsa, abin sam babu dad'in ji wallahi. Kuma ya kamata duk wani bako da zai shigo wa mutane unguwa yana irin wannan tallar a taka masa birki.

Ita kuma hukuma wajibi ne ta samar da dokokin da zasu baiwa mutane ikon walwala a gidajensu tare da iyalansu ba tare da wani ya cutar da jin su ba, da sunan sana'a yasa su ji abinda zai kunyata su cikin 'ya 'yansu, ko damun su a lokacin da suke bukatar hutawa cikin iyalansu.

In sha Allah, a gaba zan yi magana kan yadda ake amfani da Amsa Kuwwa da sunan Addini ana cutar da mutane. Allah ya bamu ikon kiyayewa ya bamu ikon gyarawa.

Yasir Ramadan Gwale
31-01-2016

Saturday, January 23, 2016

KANO: Gwamna Ganduje Yana Ta Gyada


KANO: GWAMNA GANDUJE YANA TA GYA'DA
Irin nad'e nad'en da Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje yake yi abin yayi yawa. A daidai lokacin da tattalin arzikin Kasa ya shiga wani irin mawuyacin halin ha'ula'i, arzikin man da k'asarnan ta Dogara gare shi kullum komawa baya yake yi. Farashin manfetur ya karye ya zube kasa warwas, kasuwanci ya durkushe, harkokin masanata'antu kullum suna komawa baya a guje. Kuma alumma na kara yawaita. Amma Gwamna ba ruwansa, sai bayar da muk'amai yake yi barkatai kamar kayan gadon gidansu, kullum ana karawa Laftawa Gwamnati hanyoyin zurarewar kud'i ba gaira babu dalili.
Ya kamata Gwamna ya maida hankali wajen ayyukan da ya gada wajen gwamnatocin da suka shud'e wajen yaga ya kammala su, ba kara dorawa Gwamnati nauyi ba. A makotanmu, Kaduna, Gwamna Nassir el-Rufai har ya zuwa yanzu nad'e nad'en SA da yayi basu kai goma ba. Amma mu Kano sabida watakila kirarinmu na cewa ko da me kazo mun fika, sai barna da ta'adi Gwamna yake yi da dukiyar al'ummah da sunan mukamin SA. Ya kamata Gwamna ya san ina gabas take, ya tsaya ya fuskanci kalubalen da yake kansa na tattalin arziki dan ciyar da Kano gaba, ba irin wannan nad'e nad'e marasa kan gado ba.
Ina amfanin Gwamnati ta tursasa mutane biyan haraji, daga karshe kuma ta rabawa SA's a matsayin Albashi da Alawus? Bama yiwa duk wanda Gwamnati ta baiwa muk'ami Hassada kan abinda aka bashi, hasalima muna fatan ayi mulki lafiya. Amma ba daidai bane, lokacin da ya bayyana karara cewar Gwamnatin kasarnan na fama da matsalar kud'i, amma Gwamna ba ruwansa, sai kirkiro hanyoyin kashe kudi yake da ba zasu amfanawa al'umma komai ba, domin da wadannan mukamai da babu su za ai Gwamnati ba tare da wata matsala ba, kamar yadda muke gani a Kaduna.
A dan haka, ya kamata Gwamna ya samu nutsuwa ya maida hankali wajen ganin yabi sahihan hanyoyin da zai ciyar da Kano gaba, ba rabon mukamai barkatai ba. Abin kunyar ma da yawan wadan da ake nadawa ko sunan mukamin da aka basu basa iya rubutawa daidai. Ace Gwamna ya dinga diban tantagaryar jahilai ana basu mukamai ba gaira ba dalili. Wannan wace irin Gwamnati ce haka? Ya kamata Gwamna ya sani yanzu karni na Ashirin da d'aya muke, aikin mutum goma mutum daya tak zai iya yi kuma a samu Nasara. Wannan lokaci ne da duniya ke samun koma baya ta fuskar tattalin arziki. Kullum Gwamnatocin da suka san me suke suna tsuke bakin aljihun Gwamnati ne ba wargaje shi ga mutane haka kurum ba.
Yasir Ramadan Gwale 
22-01-2016

Saturday, January 2, 2016

A Gaban Khadimul Islam Ake Barna Da Kudi?


A GABAN KHADIMUL ISLAM AKE BARNA DA KUDI?
Jiya Gwamnatin Kano karkashin Jagorancin Gwamna Abdullahi Ganduje ta shirya bakin sabuwar shekara inda mawaka suka sha ruwan Nerori. A irin wannan lokacin da ake cewa tattalin arzikin kasa ya shiga mawuyacin hali, Gwamnatin tarayya da na jihohi na ta batun tsuke bakin aljihu, amma abin mamaki a gaban Gwamna wasu mutane suka dinga yiwa mawaka da makada ruwan kudi, wannan abin takaici ne kwarai da gaske. Domin bayan tozarta ita kanta dukiya sam bai kamata a ce a gaban Gwamna ana irin wannan dabdalar yana gani bai tsawatar ba.
Yana da kyau mutanan da Allah ya baiwa arziki su nuna godiya ga Allah ta hanyar taimakawa mabukata da yin Zakkah akan kari domin ragewa al'umma radadin talauci. Zan ce na gaskiya naji takaici matuka ace har yanzu irin wannan cibayan ta'ada tana tare da al'ummar mu har yanzu ta yin liki da kudi a bainar Jama'ah. Yana da kyau Gwamnan da ake kira da Hadimi ga Addinin Islama a same shi da kwatanta bin addini a lamuransa, hakkin Gwamna ne ya tsawatar a lokacin da mutane suka tozarta dukiya irin haka. Allah ya kyauta.
Yasir Ramadan Gwale 
01-01-2016