Friday, June 27, 2014

Jan Kunne Dangane Da Batun Mubarak Bala

JAN KUNNE DANGANE DA BATUN MUBARAK BALA

Na bibiyi yadda naga ‘yan uwa da dama suna yin tsinuwa tare da la’anta ga Mubarak Bala a saboda abinda ya faru da shi. Babu shakka wannan kuskure ne mai girma dan wani dan uwa Musulmi yayi abinda yake kuskure ne a dinga aibata shi maimakon yi masa addu’ar shiriya. Alal akalli duk wanda ba zai iya yiwa wannan bawan Allah addu’ar shiriya ba, to kamata ya yi mutum ya kame bakinsa daga fadin mummunar Magana akan shi. Duk cikinmu babu wani wanda yake da garantin shiga Al-Jannah, babu wanda aka rubata masa cewa shi dan al-jannah ne, illa kawai fata da kwadayin Rahamar Allah da muke yi a ko da yaushe. Naji takaicin irin kalaman da wasu suka dinga yi babu linzami kamar su din suna da wata masaniyar cewar an lamunce musu Al-Jannah.

Yana da kyau ‘yan uwa su sani, Annabin Allah Nuhu AlaihisSalam, shi ne Annabin farko da Allah ya aiko zuwa doron duniya domin ya shiryar da mutane zuwa ga hanyar Allah, amma Allah ya kaddara mutane kalilan ne suka yi Imani da Annabi Nuhu AS, daga cikin wadan da ba su yi imani da shi ba har da d’ansa na cikinsa, wannan kuma haka Allah ya hukunta, shiriya tana hannunsa Subhanahu Wata’ala. Namu kawai shi ne isar da sakon ga al’umma Allah kuma shi ne yake juya zukatan bayinsa.

Annabin Allah Lud AS shima daga cikin wadan da ba su yi Imani da shi ba har da matarsa (iyalinsa). Allah shi ne buwayi gagara misali kuma shi ne yake jujjuyawa zukatan bayinsa Subhanahu Wata’ala, haka ya kaddara duk da kafirci da mutakabbiranci irin na Fir’auna amma matarsa ta kasance ‘yar Al-jannah tsarki ya tabbata a gareshi.

Wata rana Manzon Allah SAW yana cikin taron Sahabbai sai aka kawo wani mutum ya sha giya, aka yi masa bulala, bayan wani lokaci aka sake kawo wannan mutum, aka kuma yi masa bulala akan laifin shan giya, an yi masa haka har sau uku, sai wasu daga cikin Sahabbai suka dinga aibatashi akan laifin da yake aikatawa! Manzon Allah SAW yace da su shin zaku taimakawa Shaidan akan dan uwanku ne, ko zaku taimakawa dan uwanku akan Shaidan! Manzon Allah SAW yace da su, idan kuka aibatashi kuka la’ance shi, Shaidan yaci nasara akansa, amma idan kuka yi masa addu’ar fatan shiriya, sai ku taimakeshi yaci Nasara akan Shaidan La’ananne.

Da yawa naga suna tuhumar Iyayan Mubarak Bala cewa laifinsu ne da basu bashi tarbiyya ba. Wanda duk wanda ya jingina laifin zuwa ga iyayansa hakika ya zalunce su, duk wanda yasan Dakta Bala Muhammad tsohon Darakta Janar na hukumar Adaidaita Sahu ta jihar Kano, yasan mutum ne mai cikakkiyar tarbiyya ta addini, mai kuma san dukkan wasu lamaura da suka shafi addinin Musulunci, Bala Muhammad tsohon ma’aikacin gidan Radiyon BBC ne, dan haka mutane su koma su tambayi me ya sa Bala Muhammad ya bar aikin BBC, ya bari ne a saboda kishinsa da kaunarsa da tarbiyya irin ta addinin Musulunci.

A baya-bayan nan kafin zamansa shugaban hukumar Adaidaita Sahu ta jihar Kano. Bala Muhammad mutum ne mai yawan halartar tarukan kungiyoyin addinin Musulunci a ciki da wajen Najeriya, duk wadan da suka yi harkar MSSN a Najeriya zasu shaidi Bala Muhammad da juriya da san taimawa addini ta kowanne fanni. Dan haka zai zama zalinci a zargi Bala Muhammad da cewa bai bawa iyalansa tarbiyya ta Musulunci ba.

Bahaushe yana cewa ka haifi Mutum ne baka haifi halinsa ba. Wannan abu da ya faru da shi kansa Mubarak Bala abu ne da kusan yake sabo a cikin al’ummarmu, ace mutum ya fito irin haka cewa ga wani yayi Ridda a bainar jama’a, sau da dama irin haka kan faru ba tare da ansani ba. Kuma abinda yafi wanda Mubarak Bala ya aikata yana faruwa a cikin birnin Kano.

Ansha samun mabiya wata darika na ikirarin cewa Shehunsu shi ne Allah Wal’Iyazubillah. Wasu da dama kan kira kansu da Alloli, wannan wata tsohuwar shirkace da anjima ana yinta a jihar Kano, duk kuwa da masu yi din suna ikirarin su Musulmai ne, amma zaka ji a lokuta da dama bayanansu ko wakokinsu suna kore samuwar Allah Subhanallah, mutane zasu iya tuna irin wannan da ya faru da wani mawaki wanda ta kai har Khalifa Isyaka Rabiu ya fito ya barrantar da kansu daga kalaman da mawakin yayi na shirka, wanda har yanzu mawakin ba’a jishi ya yi nadamar abinda ya aikata ko ya nuna cewa kuskure ya yi ba.

Dan haka, a halin da muke ciki bin sahihiyar koyarwar addinin Musulunci da ta kunshi Al-Qur’ani da Hadisan Manzon Allah SAW it ace kadai mafita a garemu wajen kaucewa fadawa hanyoyin shaidan La’ananne. Lallai ne mu lizimci wajen da ake yin karatun addini mu kuma lizimci tuntubar Malamai a duk lokacin da wasu al’amura suka shige mana duhu dan samun waraka.

Muna addu’ar Allah ya shiryi wannan bawa nasa Mubarak Bala ya dawo kan hanya madaidaiciya, ya ganar da shi kuskurensa, ya fahimtar dashi addinin Musulunci shi ne addini a wajen Allah. Allah ka shiriyi al’ummarmu shiriya ta addini, Allah ka tabbatar da duga-duganmu wajen yi maka da’a da bauta. Allah ka shiryemu shirin addini.

YASIR RAMADAN GWALE 
27-06-2014

Wednesday, June 25, 2014

Anya Za'a Iya Yiwa Mubarak Bala Hukunci A Dokar Kasa Kuwa?

ANYA ZA’A IYA YIWA MUBARAK BALA HUKUNCI A DOKAR KASA KUWA?

Matashin nan da rahotanni a jiya suka nuna cewar ya sauya addininsa daga Musulunci zuwa wani abin daban ya zo da sarkakiya a tsarin shari’ar kasarnan. Shi dai wannan matashin bayanai sun nuna cewar ba wai ya canza sheka daga Musulmi ne zuwa kirista ba, illa iyaka yace shi bai yadda da samuwar Ubgajinmu Mahaliccinmu ba, Babbar Magana! A kashin gaskiya irin wannan batu na Mubarak Bala ba wani sabon abu bane, domin wannan na daya daga cikin aqidar Dirwaniyanci (Darwinism) abinda kawai za’a iya zamewa mutane sabo shi ne, shi Mubarak Bala ya karanta sashin kimiyyar hada sinadarai ne (Chemistry), sabanin idan a ce ya karanta “Sociology” ne wanda amfi samun masu irin wannan ikirarin a cikin wadan da suka karanci tsantsar sociology babu karatun addini a tare da su.
Amma wannan abinda da Mubarak Bala ya aikata duk kuwa da cewar ana tuhumar hankalinsa, ko da gaske yake yi akan batunsa ko bad a gaske yake yi ba, to lallai mu sani Mubarak Bala yana da cikakkiyar kariya ta kundin tsarin mulki da ba za’a iya zartar masa da hukuncin kisa ba, ko da kuwa ya kekesa kasa akan batun da yake ikirari.

A kundin tsarin Mulkin Najeriya na 1999, sashi na 38 karamin kashi na daya (1) ya baiwa duk dan Najeriya damar yin addinin da yaga dama, sannan kuma ya canza addinin da yake bi a duk lokacin da yaga dama ba tare da an tuhumeshi da aikata wani laifi ba. Wannan na daya daga cikin sashin da ya baiwa wata baiwar Allah mai suna Aisha waddata ta koma Musulunci daga Kiristanci kwanakin baya a jihar Neja wadda batun ta ya janyo kace-nace.

Haka kuma, sashi na 36 karamin kashi na goma sha biyu (12) yace babu wani abu da mutum zai yi ace laifi ne har sai idan wannan abin ya kasance a rubuce cikin wata doka wacce Majalisar kasa ko ta jiha ta yi doka akansa. A dan haka, a bisa dogaro da kundin tsarin Mulkin Najeriya wanda dukkan masu Mulki sunyi rantsuwar tabbatar da zasu bashi kariya a kowanne irin hali, wannan matashi ba za’a iya zartar masa da hukuncin kisa ba ko da kuwa ta tabbata ridda ya yi.

Dan haka, wannan yana daya daga cikin inda aka samu tarnaki a kundin tsarin Mulki da ya sabawa koyarwar addinin Musulunci. Wannan kuma kalubale na babba ga majalisun dokokin da suke aiwatar da Shari’ar Musulunci. A dan haka, yana da kyau jama’a su sani, a dukkan wasu kundin dokokin Panel Code da aka samar a jihohin da suke aiki da Shari’ar Musulunci babu inda aka ayyana hukuncin kisa ga wanda ya bar addininsa zuwa wani addinin daban. Saboda haka, a tsarin da muke kai a Najeriya, babu wani alkali da zai iya yankewa Mubarak Bala hukuncin kisa a irin wannan lamari sai fa idan laifin ya kasance rubutacce ne a cikin dokar kasa, wanda wannan babu shi a rubuce.

Babu shakka wannan al’amari zai bude wani sabon babi a kundin tsarin Mulkin kasarnan, zai kuma janyo wani sabon cece-kuce na daban, Allah ya kiyaye. Gwamnati dai ba zata iya zartarwa da wannan matashi hukunci kisa ba matukar ba kotu ce ta sameshi da laifin abinda ya aikata bat a ce ga hukuncinsa.

Haka kuma, tsarin Mulkin Najeriya yace dukkan wata doka ko wani tsari da yaci karo da kundin tsarin Mulkin Najeriya, to “constitution” zai kasance a sama da wannan tsarin ko da kuwa koyarwar wani addini ne. Wannan kuma shi ne babban tarnakin da kundin tsarin Mulkin Najeriya ya yiwa koyarwar addinin Musulunci, wanda zamu iya komawa majalisun dokoki na jihohin dan yin wasu dokoki da suka dace da koyarwar addininmu na Musulunci.

Dan haka, yana da kyau al’umma su sani cewar babu yadda masu Mulkin da suka rantse domin kare kundin tsarin Mulki tare da yi masa biyayya zasu yi wani hukunci da ya saba masa, saboda haka, a kurkusa abinda za’a iya yi tunda ba zamu iya canza kundin Mulki a yanzu ba, shi ne, a samu Malamai da masana su zauna da wannan bawan Allah Mubarak Bala su yi masa wa’azi da Nasiha ko Allah zai karkato da hankalinsa ya fuskanci irin hadarin day a jefa rayuwarsa idan hart a tabbata cewa yana da lafiyayyan hankali ya dauki hukuncin day a zabawa kansa na kin amincewa da samuwar ubangiji.

Sannan kuma, ya zama dole a aiwatar da bincike na me ya sanya wannan bawan Allah ya bar Musulunci zuwa wani abin daban, dan a samu bakin zaren yiwa wannan tufkar hanci. Allah ya kare mana Imaninmu, ya sa mu mutu muna cikin Imani mu tashi muna masu imani da Allah da ManzonSa Sallallahu Alaihi Wasallam. A gaba kuma zamu zo da abinda Musulunci yace game da abinda Mubarak Bala ya aikata In Sha Allah.

YASIR RAMADAN GWALE
26-06-2014


Ridda A Sudan Da Kano

RIDDA A SUDAN DA KANO

A jiya muka ji labarin matarnan da ta yi ridda ta bar addinin Musulunci a kasar Sudan cewa ta haihu a gidan kaso inda kuma kotu ta bayar da umarnin a saketa bayan da matar  Mariam Ibrahim Yahya ta daukaka kara akan hukuncin da kotun farko ta yanke mata na haddin kisa ta hanyar rataya. Ita dai Mariam Yahya Ibrahim ta auri mijinta Daniel Wani dan kasar Amurka, inda daga bisani ta bar Musulunci ta koma Kiristanci bayan da suka yi aure. Har ya zuwa jiya da ta shafe kwanaki 21 a gidan yari ana tsare da ita, Mariam bata gamsu ta sauya addini daga kiristanci ta dawo Musulunci ba ta cigaba da kafewa akan addinin Kirista.

Kwatsam kuma, a wani labari mai kama da wannan, sai muka ji a Kano ma wani matashi Mubarak Bala ya yi ridda ya bar Musulunci, duk da bayanan da suka fito sun nuna cewar shi Mubarak Bala ya nuna bai yadda da samuwar ubangiji ba ne, Wal Iydhu Billah! Lallai wannan abu ne mai tayar da hankali ace mutane suna fita daga Musulunci suna komawa kiristanci a garuruwan da suke da kusan Musulmi dari bisa dari.

Sanin kowa ne Sudan kasa ce ta Musulunci kamar yadda Kano gari ne na Musulunci amma ace irin haka ta faru wadannan mutane sun bar Musulunci a garin Musulunci. Ba shakka akwai tashin hankali a cikin batun.

Dan haka,  Addinin Musulunci ya yi tanadi akan wadan da suka bar Musulunci suka koma wani addinin daban, Malamai zasu yi bayanin irin hukuncinsu, musamman shi Mubarak Bala In Sha Allah, haka kuma wajibin hukumomi ne su tabbatar da zartar musu da hukuncin da yake kansa a Musulunce.

A gefe guda kuma, daga cikin munafukan kungiyoyin Shaidan dake kasashen Turai da Amurka sun samu dama ta yin abida suke so wajen nuna dole a baiwa kowa 'yancin yin addinin da yaga dama, wanda ko muma a Najeriya kundin tsarin Mulkinmu ya yi tanadin baiwa kowa damar yin addinin da yaga dama, amma dai babu shakka idan har Mubarak Bala bai dawo daga wancan tunani ba, dole a jingine kundin tsarin Mulki a yi masa hukuncin da Musulunci ya tanada. Allah ya shiryi al'ummarmu.

YASIR RAMADAN GWALE
25-06-2014


Tuesday, June 24, 2014

Wasika Daga Mundubawa Gidan Sardaunan Kano

Malam Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano
WASIKA DAGA MUNDUBAWA GIDAN SARDAUNAN KANO

Bayan gaisuwa da fatan alheri ga al’ummar jihar Kano. A yanzu haka muna cikin wani lokaci da aka jarrabe mu da fitina da motsuwar zukata, muna cikin yanayi mara dadi, addu’ah da riko da sababin karbar addu’ah zasu yi tasiri matuka wajen fitarmu daga cikin halin da muke ciki, ta yiyu Allah ya dubi gajiyayyu daga cikinmu ko yaran da hankalinsu bai nuna ba ya kawo mana dauki ta inda bamu zata ba.

Kamar yadda kowannemu ya sani, a jiya Litinin al’ummar jihar Kano musamman wadan da ke yankin unguwar Kofar Nassarawa da unguwar bayan gidan Malamai (TSB) da sabuwar Kofa da Rumfa Kwaleji sun shiga dimuwa sakamakon wata fashewa mai karar gaske da ta faru a makarantar School of Hygiene, inda daga bisani bayanai suka tabbatar da cewar harin Bam ne aka kawo! Inna Lillahi Wa Inna Ilaihi Raji’un! Ba shakka dole hankula su dungunzuma, zuciya ta karaya, sakamakon abinda ya faru kuma ya zo da asarar rayuka.

Dan haka, ko a APC mutum yake, ko a PDP mutum yake, abu mafi muhimmanci shi ne, mu al’ummar Musulmai ne, kuma ba muda wani gari da ya wuce Kano. Wannan ta’addancin mu aka yiwa, al’ummar Musulmi ne suka shiga damuwa sakamakonsa, mutanan da suka mutu a dalilin wannan hari ‘yan uwanmu ne ‘yan jihar Kano Musulmi.

Ya ‘yan uwa masu girma, yana da kyau mu sani, idan masifa ta zo bata tambayar katin jam’iyya balle waye dan gari ko bako kafin ta afkawa mutum. Abinda ya fi dacewa mu yi a irin wannan lokaci shi ne addu’ah tare da komawa zuwa ga Allah, ba yin cece kuce da ba zai iya dawo da rayukan wadan da suka rasu ba. Lallai mu yawaita ambaton Allah, mu kuma rage aikata ayyukan sabo, muji tsoron Allah a cikin mu’amalolinmu na yau da kullum mu nemi agajin Allah a halin da muke ciki.

Allah ka tsare mana Imaninmu da mutuncinmu da rayukanmu. Ya Allah ka amintar da mu a cikin gidajenmu da garuruwanmu, Allah ka yaye mana wannan damuwa a cikin zukatanmu, iyalanmu da ‘yan uwanmu da abokanmu da dukkan al’ummarmu Allah ka zama gatanmu.

Muna kuma yin addu’ah ta musamman akan wadan da suka rasu, Allah kajikansu ka gafarta musu ka sa bakin wahalarsu kenan, masu aikata wannan aikin ta’addanci Ya Allah idan sun faku a garemu kai basu faku a gareka ba, Allah ka bi mana hakkinmu, Allah karka baiwa ‘yan ta’adda dama akan al’ummarmu. Allah ka wargaza shirinsu ka mayar musu da kaidinsu garesu.

Muna mika sakon jaje ga Gwamnatin Kano da al’ummar jihar Kano baki daya. Allah ya kare Jihar Kano da Najeriya baki daya. Wannan sako ne a madadin Mai Girma Sardaunan Kano Mallam (Dr.) Ibrahim Shekarau da dukkan Masoya da ‘yan uwa da abokan Mudubawa Avenue Kano.

ZABEN EKITI: Ekitawa Sun Guntulewa Bola Tinubu Yatsa Daya

Bola Tinubu Madugun APC

ZABEN EKITI: Ekitawa Sun Guntulewa Bola Tinubu Yatsa Daya

Zaben da aka yi a makon da ya gabata a jihar Ekiti, shi ne zabe na baya-bayan nan da hukumar zaben Najeriya karkashin jagorancin Farfesa Attahiru Jega ta bugi kirji da shi wajen cewa anyi tsantsar gaskiya da adalci a zaben, abinda ya kara gasgata hukumar zabe shi ne, sakon karbar kaddara da dan takarar APC kuma Gwamna me ci Kayode Fayemi ya fitar a ranar Lahadi, inda ya taya dan takarar PDP Ayo Fayose da ya samu nasara murna ya kuma yi masa fatan alheri.

Babu shakka Ekitawa sun zabawa kansu makomar da ita suke ganin ta fi zama a’ala a garesu. Gwamna Kayode Fayemi ya burgeni ainun akan abin da ya faru, inda ba tare da wani bata lokaci ba ya karbi sakamakon zaben ya kuma taya sabon Gwamna murnar samun nasara, irin wannan siyasar da muke gani a Amerika da sauran kasashen turawa muke fatan ‘yan siyasarmu su yi koyi wajen karbar kaddarar faduwa zabe ba tare da wani kunji-kunji ba, duk da cewa ba laifi bane wanda yake ganin an zalince shi ya je kotu dan a bi masa hakkinsa.

Sai dai wannan zabe ko shakka ba zai yiwa Madugun jam’iyyar APC Bola Tinubu dadi ba, domin daga cikin ‘yan yatsunsa guda biyar Ekitawa sun guntule masa daya a yankin da yake tunkaho da takama da shi, har ake yi masa kirarin mutum mafi buyawa a siyasar yankin Kudu maso yamma day a kunshi Yarabawa Zalla.

Amma ga duk wanda ya san tarihin siyasar sabon Gwamna Fayose ba zai yi mamaki da wannan nasara da ya samu ba. Domin ya yi gwamna a baya kuma ya nuna kwazo, gashi matashin manomi mai matukar kaunar Talakawa, mutum mai son shiga cikin jama’a yana mu’amala da su, wannan ta sanya talakawa suka saki jiki da shi sosai, mutane da dama sun bayar da shedar irin karamci da son jama’arsa da Fayose yake yi.

Yanzu kuma babu wani abu da ya rage illa mu tsumayi zaben jihar OSUN da shima yake tafe nan gaba a wannan shekarar ta 2014. Shin suma Osunawa zasu sake guntulewa Tinubu yatsa ko kuwa zai sake karfafa ikonsa a siyasar jihar, wannan lokaci ne kawai zai bayar da amsa, amma dai ba shakka Gwamna Rouf Aregbesola na daga cikin gwamnonin da suke kamanta gaskiya a tsakanin Gwamnonin yankin Yarabawa. Da alheri.

23-06-2014

Wednesday, June 11, 2014

Risala Zuwa Ga Mai Martaba Sarkin Kano Sanusi Lamido Sanusi


RISALA ZUWA GA MAI MARTABA SARKIN KANO MALAM SANUSI LAMIDO SANUSI

Bismillahir Rahmanir Rahim. Ina fara bude wannan Risala da sunan Allah, mai gamammiyar Rahama, mai gamamman jin 'kai, tsira da AmincinSa su 'kara tabbata ga fiyayyan halitta, Manzon tsira cikamakin Annabawa, Annabi Muhammad SAW da alayensa da Sahabbansa masu daraja da wadan da suka biyo bayansu da kyautatawa har yazuwa ranar sakamako. Dukkan wanda Allah ya shiryar da shi shi ne hakikanin shiryayye, wanda duk Allah ya batar babu mai iya shiryar da shi.

Da farko, ina mai yin amfani da wannan dama, wajen kara mika ta'aziyata ga sabon Sarkin Kano Mallam Sanusi Lamido Sanusi, a bisa rasuwar tsohon Sarkin Kano Alh. Ado Abdullahi Bayero, Allah ya jikansa ya gafarta masa, Allah ya kyauta bayansa. Ina kuma kara taya Mai Martaba Sarki murna da kuma alhini; ina taya Mai Martaba Sarki murnar zama sabon Sarkin Kano na 14 a dangin Sullubawa, na 57 a tarihin Masarautar Kano, ina kuma taya Mai Martaba Sarki jimamin abubuwan da suka faru yayin wannan nadi na shigar al'amuran siyasa da boren da wasu fusatattun matasa suke yi, babu shakka wannan abin bai yi dadi ba.

Haka kuma, ina amfani da wannan damar wajen yin kira ga sabon Sarkin Kano Malam Sanusi Lamido Sanusi, da ya yi watsi da dukkan al'amuran siyasa da suka faru a yayin wannan nad'in sarauta, ya rungumi al'ummar Kano da kasa baki daya dan samun zaman lafiyarsa da dorewar mulkinsa. Ya Mai Martaba Sarki, hakika shigar al'amuran siyasa cikin wannan abu bai yi mana dadi ba, domin dukkan masu mulkin siyasa wa'adi garesu takaitacce da baya wuce shekaru 8 a yayinda Sarki ke da wa'adin iyakar rayuwarsa.

Ya mai martaba sarki, a dan saboda a samu zaman lafiya da kwanciyar hankali da dorewar Mulkin sarautar jihar Kano, ina kira a gareka da ka rungumi dukkan masu mulkin siyasa daga ko wace jam'iyya suke dan hidimtawa al'umma. Abu ne mai muni, amfanin da 'yan siyasa suka yi da wannan kujera ta sarautar Kano dan biyan bukatunsu na siyasa, wanda a karshe babu wanda za'a bari a cikin al'amarin sai ita masarautar Kano. 

Ya Mai Martaba Sarki, adawa ko nuna tirjiya ga gwamnatin tarayya wadda it ace Gwamnatin koli a Najeriya babu abinda zai janyo mana face faduwar daraja da zubewar girma da gurbacewar al'amura, lallai ne, Mai Martaba Sarki ya yiwa Gwamnatin Tarayya da'a da biyayya wajen ciyar da rayuwar al'umma gaba, kin yin hakan babu abinda zai haifar face rashin nasara da rashin biyan bukatu.

Ya isa abin misali yadda marigayi Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Ado Bayero ya kame kansa daga shiga al'amuran siyasa da daukar bangare daya, tafiya da kowa tare da rashin nuna bambanci ko wariya na daga cikin sirrin nasarar mai martaba sarkin kano Allah ya kai rahama gareshi.
'Yan siyasa suna yin komai ne dan biyan bukatunsu na siyasa ba tare da la'akari da halin da al'umma ta ke ciki ba. Su wadannan 'yan siyasar da suka shigo cikin wannan al'amari ba sunyi abinda suka yi bane, dan nuna kishi ga al'ummar jihar kano, illah manufarsu ta siyasa ta bakantawa gwamnatin tarayya da suke hamayya da ita rai, tare da cimma nufinsu na siyasa, bayanan da suke fita daga bakunansu sun tabbatar da hakan.

A lokacin zaben 2011, Gwamnan jihar Nassarawa Aliyu Akwe Doma ya sanya sarakunan jihar a cikin al'amuran siyasa wanda hakan ya janyo musu zubewar kima da daraja da jefa su cikin wulakanci da kaskanci, sai da takai an fasa motar da Sarkin lafiya yake ciki, aka janyo rawaninsa ya fadi kasa, a dalilin halin da gwamnan jihar ya sanya shi na nuna adawarsa karara ga jam'iyyar Adawa ta Buhari, inda gwamnan ya umarce su da kada su sake su karbi tawagar Buhari da zata zo yakin neman zabe cikin fadarsu, wannan al'amari bai yi musu kyau ba, akan biyayyar da suka nunawa Gwamna ta yadda suka sanya kansu a cikin sha'anin siyasa, yanzu dai gwamna y agama wa'adinsa ya tafi su kuma suna nan a matsayin sarakuna, wanda wannan ba komai zai janyo ba sai da na-sani.

Ya Mai Martaba Sarki, kada ka saka kanka a cikin wani yanayi irin wannan, ta yadda Gwamnatin Kano da ke hamayya da gwamnatin tarayya zata sanyaka cikin sha'aninsu na siyasa, sanya kai cikin wannan al'amari babban koma baya ne ga masarautar Kano da kuma al'ummar kano, Mai Martaba Sarki uban kowa ne, dan siyasa da wanda ba d'an siyasa ba, talakawa da masu kudi. Kaucewa shiga sha'anin siyasa shi ne abinda zaifi zamarwa Mai Martaba Sarki alheri da mutunci a idan duniya. Sanin kanmu ne, shugabanni na siyasa sune a gaba, sune wadan da suke da Kotu da 'yan sanda da kuma uwa uba dukiyar al'umma ke karkashin kulawarsu, lallai tafiya tare dasu wajen ciyar da al'umma gaba shi ne yafi komai muhimmanci ga Mai Martaba sabon Sarkin Kano Malam Sanusi Lamido Sanusi, rashin hakan kuma ba zai haifar da d'a mai ido ba.

A dan haka, wannan ba yana nufin Sarkin Kano ya je ya kwantawa gwamnati ta taka shi irin yadda taga dama ba. Yana da kyau, Mai Martaba Sarki ya hada kai da gwamnati wajen ciyar da al'ummar kano gaba. Ita gwamnati ba zata taba kame hannu wani mahaluki ya zamar mata karfen kafa a sha'anin tafiyar da gwamnati ko Mulkinta ba! Ya isa abin misali, Sardaunan Sokoto tsohon Firimiyan Jihar Arewa, wanda shi ne mutanan Arewa suka rika a matsayin shugaba na kurkusa mafi Adalci a mulkinsa, amma kuma a gefe guda shi ne ya kawar da rawanin sarkin Kano Muhammadu Sanusi.

Mun ga yadda al'amuran siyasa suka mamaye Sarautar Sarkin Musulmi Dasuki wadan da basu yi dad'i ba, haka kuma, munga yadda siyasa ta shiga tayi awan gaba da Mai Martaba Sarkin Gwandu Almustapha Haruna Jakwalo, wadannan dukkansu siyasa ce ta shiga ta damalmala al'amuran sarautarsu ta nemi zubar da kimar masarautunsu.

Dan haka, kame kai daga shiga harkokin siyasa ga Mai Martaba Sarkin Kano Malam Sanusi Lamido Sanusi tare da rungumar kowa, shi ne abinda zai fi zama alheri a tsawon wa'adinsa, kuma zaifi jawo masa kima da mutunci a idan duk wata gwamnati da zata zo ta tafi, idan muka bari sarauta ta koma kamar mulkin siyasa, to haiba da muhibba da kwarjini na sarakuna ya gama zubewa kasa warwas, haka kuma masarautar Kano alkibla ce ta sauran dukkan masarautu da ke fadin tarayyar Najeriya.

Wadannan fitintinu da ke faruwa da wadan da ke shirin faruwa Allah ya tsagaita su, Allah ya kawar mana da dukkan wani abin 'ki da Alla-wadai. Ina kara jaddadawa Mai Martaba Sarki uban kowa ne ba tare da la'akari da siyasar da mutum ke bi ba. Allah ya taimaki Masarautar Kano da sauran masarautun Najeriya baki daya, Allah ya tabbatar mana da dawwamammen zaman lafiya. Allah ya warware wannan sabatta juyatta da ke faruwa.

11-06-2014

SABON SARKIN KANO: Kaddara Ta Riga Fata


SABON SARKIN KANO: KADDARA TA RIGA FATA

Ina mai amfani da wannan damar wajen sanar da al'umma musamman wadan da sukai ta turmin sakon Inbox wadan da hannuna yakai garesu da kuma wadan da hannuna bai kai garesu ba, da wadan da suka kirani a yawa tun jiya, cewar ni Yasir Ramadan Gwale ina taya sabon Sarkin Kano Alhaji Sanusi Lamido Sanusi murnar zama sarkin Kano da ya yi a jiya. Allah ya yi masa jagoranci, Allah ya yi riko da hannunsa wajen aiki da daidai.

Babu shakka, zuciyarmu ta kadu, rai ya sosu da muka ji cewar ba Chiroman Kano Alhaji Samusi Lamido Ado Bayero aka zaba ba a matsayin sabon Sarkin Kano. Wannan kuma ba shi ne yake nuna cewa bamu yarda da kaddara ba, ai akan yiwa mutum mutuwa yaji zafi har yayi kuka, daga karshe kuma ya mika lamarinsa ga Allah, kuma Allah ya bashi ladan hakuri, dan Allah shi ne yake hukuntawa. Idan sanmu ne Chiroman Kano ya zama Sabon Sarkin Kano, tunda kuma Allah bai hukunta masa ba, munji mun bi, sami'ina wa'ada'ana.

Allah ya jikan Marigayi Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero. Allah ya kai rahama gareshi. Ina kuma amfani da wannan damar wajen kara sanar da 'yan uwa kamar yadda Malaminmu Dr. Bashir Aliyu Umar ya sanar a shafinsa cewa, lallai Sabon Sarkin Kano ba dan Shi'ah bane. Ina kuma kira ga daukacin al'ummarmu da su yi hakuri da Abinda ya zo haka ba wanda aka zata ba, a Musulunci biyayya ga Shugabanni wajibi ne ko da kuwa ba akan daidai Shugabannin suke ba, matukar ba umarni suke yi da sabn Allah ba.

Allah ya ja zamanin Sabon Sarkin Kano Alhaji Sanusi Lamido Sanusi, ina kuma amfani da wannan dama har iala yau wajen yin kira ga sabon Sarkin Kano da ya nada Dakta Bashir Aliyu Umar a Matsayin Sabon Wazirin Kano, ina da yakinin hakan zai sanya Natsuwa a zukatan da dama wadan da suke jifansa da Shi'anci. Allah ya zaunar da kasarmu lafiya, ya zaunar da Kano lafiya, masu bore kuma ayi hakuri a karbi abbinda ya faru a matsayin kaddara. Daman Imani baya cika sai mun yarda da kaddara mai kyau da mara kyau. 

Daga Karshe ina mika Ta'aziya ta ta rasuwar tsohon Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero ga Mai Girma Sardaunan Kano Mallam Ibrahim Shekarau, ina kuma taya shi murnar nada abokinsa Dan Majen Kano a matsayin sabon Sarkin Kano. Na gode.

09-06-2014

Fatanmu Sanusi Lamido Sanusi Ya Gaji Mahaifinsa


FATANMU SANUSI LAMIDO SANUSI YA GAJI MAHAIFINSA

Malam Sanusi Lamido Sanusi tsohon tubabben Gwamnan Babban Banki Najeriya CBN. Yana daga cikin wadan da wasu ke fatan samun wannan Sarauta ta jihar Kano, da dama suna fadin haka ne saboda ganin irin kusancinsa da Mai Girma Gwamnan Jihar Kano injiniya Rabiu Musa Kwankwaso. Gwamna Kano shi ne zai yi zabi na karshe akan wanda zai zama sabon Sarkin Kano, bisa tattaunawa da shawarwari na manyan dattawa daga jihar Kano da kuma lura da inda ra'ayin al'umma ya karkata, kamar yadda a baya lokacin nadin Sarautar Wazirin Kano, Gwamna yace yabi ra'ayin al'umma wajen kin amincewa da Malam Nassir Muhd Nassir (LDC) a matsayin sabon Wazirin Kano.

Kamar yadda mafi rinjayen ra'ayin al'umma ya nuna, shi ne, suna fatan daga cikin 'ya 'yan Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero wai ya gajeshi, duba da irin yadda Sarkin ya shafe shekara da shekaru yana rike da sarautar Kano, wannan wasu na ganin ita ce karramawa da za'a iya yiwa Sarki bayan Ransa a baiwa Dansa wannan sarauta. Wanda kuma yafi cancanta kamar yadda daga cikin 'ya 'yan Sarki mutum Takwas (8) dake rike da Sarauta suke mika wuya da goyon baya ga babban Dan Sarki Muhammadu Sunusi Lamido Ado Bayero a matsayin wanda zai gaji mahaifinsu, muna fatan Gwamnati ta girmama wannan ra'ayi na al'umma.

Haka kuma, Malam Sanusi Lamido Sanusi da ake ganin hankalin Gwamnati yafi karkata gareshi, muna fatan shima zai gaji Mahaifinsa. Mahaifin Sanusi Alhaji Aminu Sunusi shi ne tsohon Chiroma Kano, ya rike wannan Sarauta har rasuwarsa, kuma d'a ne ga tsohon Sarkin Kano Muhammadu Sunusi, muna fatan, idan Allah ya baiwa Chiroman Kano sabuwar Sarautar Sarkin Kano, shi kuma zai nada Sanusi Lamido Sanusi a matsayin sabon Chiroman Kano Hakimin Gwale dan shima ya gaji mahaifinsa. Allah ya tabbatar mana da alheri. Sunusi Ado Bayero Allah ya amince maka.

YASIR RAMADAN GWALE 
08-06-2014

Chiroman Kano: Alhaji Sunusi Lamido Ado Bayero


CHIROMAN KANO: ALHAJI SUNUSI LAMIDO ADO BAYERO!

Mai Martaba Sarkin Kano Mai rasuwa, ya haifi babban dansa Sunusi wanda aka yiwa alkunya da Lamido yana da shekaru 26 a duniya. An haifi Sunisi a shekarar 1956 a unguwar Chiranchi a yankin karamar hukumar Gwale inda nan ne inda Marigayi Sarki ya fara zama da iyalinsa, kuma nan ne inda Chiroman yake zaune da iyalinsa yanzu haka. Babban dan Sarki Sunusi Ado Bayero ya yi karatu kamar sauran yaran al'umma da karatun Alkur'ani, inda daga nan aka kaishi Makarantar Firamare ta Kwana dake garin Rano a shekarar 1963, shekarar da mahaifinsa ya zama Sarki, sannan ya kammala a shekarar 1969 inda daga nan ya wuce Kwalejin Rumfa, inda nan mai Martaba Sarkin Kano Alh. Ado Bayero ya yi lokacin tana Middle School, inda ya kammala a shekarar 1973 inda daga nan ya wuce zuwa Kwalejin Gwamnatin Tarayya dake Birnin Kudu inda ya samu shahadar kammala karatun Sakandire a shekarar 1975.

Bayan da Sunusi ya kammala karatun Sakandire ne ya nuna sha'awar koyon harshen Faransanci inda ya yi Diploma akan harshen Faranshi ya kuma kammala da sakamako mai daraja a kasar Faransa. Bayan ya dawo daga kasar Faransa ne ya shiga Kwalejin share fagen shiga jam'iah ta kano CAS, daga nan yayi babbar Diploma a sha'anin aikin Lauya a Institute of Administration dake Kwango a Zaria daga nan kuma ya samu shiga Jami'ar Ahmadu Bello Zaria inda ya yi digiri akan aikin Lauya ya kammala a shekarar 1983 ya kuma halarci makarantar horon lauyoyi ta kasa a 1984 yayi hidimar kasa a jihar Kaduna inda ya koyar a Kaduna Politechnic daga nan kuma ya yi ayyuka a matakai da dama har ya kai mukamin Director, kafin daga bisani a shekarar 1990 Mai Martaba Sarki ya nadashi Sarautar Dan Ruwatan Kano.

Daga nan Sunusi ya cigaba da aikinsa kuma yana rike da Sarautar gargajiya. Ya yi aiki a ma'aikatar Shari'ah ta Kano ya zama Legal Adbaiza a Kano Investment, daga nan likkafa ta cigaba ya kai har matsayin Famanan Sakatare a Ma'aikatar Yada Labarai ta jihar Kano tundaga 1996 har zuwa 2002. Ya kafa kamfanin aikin Lauya na Lamido & Co. Daga nan kuma ya samu sauye-sauyen Sarauta inda ya zama Tafidan Kano ya zama Sarkin Dawakin Tsakar Gida, daga bisani kuma ya zama Chiroman Kano Hakimin Gwale, sarautar da yake rike da ita har zuwa rasuwar Mai Martaba Sarki a ranar 06 ga watan shida 2014. 

08-06-2014

Friday, June 6, 2014

Mutum Shida Ne Manya A Kano: Mai Martaba Sarki Ne Babbansu

Marigayi Alh. Ado Abdullahi Bayero
MUTUM SHIDA NE MANYA A KANO: MAI MARTABA SARKI NE BABBANSU

Jihar Kano Allah ya hore mata mutane masu yawa kama daga Malamai da Attajirai da Sarakuna da 'yan Boko da sauransu. A baya-bayan nan Manyan Dattawa 6 ne a Kano wanda ake damawa da su a harkar Sha'anin tafiyar da mulkin al'umma jihar Kano da kasa baki daya, haka kuma, 'yan Siyasa a Matakai na Gwamnatin Tarayya da Jiha da kananan Hukumomi suna jin maganarsu kuma sun isa da kowa a kano akan duk abinda ya shafi al'umma.

Na farko Shi ne, Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Ado Bayero.

Na biyu shi ne, Alh. Aminu Alhassan Dantata.

Na uku shi ne, Khalifa Isiyaka Rabi'u.

Na hudu shi ne, Alh. Yusufu Maitama Sule (Danmasani Kano)

Na biyar shi ne, Alh. Magaji Danbatta.

Na shida shi ne, Alh. Tanko Yakasai.

Idan ana maganar jihar Kano to la shakka babu dattawa kamar wadannan mutanen, su ne wadan da suke da ruwa da tsaki akan dukkan wasu al'amura da suka shafi tafiyar da rayuwar al'umma a jihar Kano da kasa baki daya. wadannan mutane su ne wadan da gwamnati tafi jin maganarsu sama da ta kowa a sha'anin al'umma, Gwamnati na tafiya da su domin samun bakin zaren aiwatar da Shugabancin jama'a lami lafiya.

Babba kuma Jagora, jigo a cikin wadannan jerin Gwano shi ne Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Ado Abdullahi Bayero wanda ya kwanta dama a yau din nan. Babu shakka rasuwar Mai martaba Sarki ta haifar da wani wagegen gibi a jihar Kano. Samun dama irin wadda Mai martaba Sarki ya samu ta tsawon Shekaru da tsahon wa'adin Mulki kalilan ne daga cikin mutane suke samu.

Babu shakka dukkan wanda zai biyo bayan Mai Martaba Sarkin Kano, a matsayin sabon Sarki zai hadu da kalubale mai yawa wajen tafiyar da al'amuran jama'a kamar yadda Sarki ya yi. Sanin duk mutumin Kano ne, Mai Martaba Sarki mutum ne da ya yi nasa kuma yayi na jama'a, mutum mai kaunar jama'a, mai kiyaye ka'ida, mai bin doka, ba shida kwadayi, mai kula da lokaci, mai son yara da tausaya musu, mai cika alkawari. Lallai anyi rashi babba, Allah ya jikan Sarki ya gafarta masa ya sa Al-Jannah ce makomarsa, kurakuransa Allah ya yafe masa. Allah ya zaba mana madadinsa wanda zai dora daga inda ya tsaya da gaskiya da adalci da rikon Amana da tausayi da jin kai. Allah ya ka jikan sauran musulmi a duk inda suke.

YASIR RAMADAN GWALE
06-06-2014

Ta'aziyar Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Ado Bayero

Ranar Juma'ah ita ce rana mafi daraja a cikin ranakun Mako. A wannan rana ce Kamar yadda Walin Kano, Alh. Mahe Bashir Wali ya bayar da sanarwar rasuwar Mai martaba Sarkin Kano Alh. Ado Abdullahi Bayero Allah ya jikansa. In Shaa Allahu za'a yi jana'izarsa yau bayan Sallar Juma'ah a kofar fadarsa.

A madina da Zainab da dukkan dangi da 'yan uwa da abokai, muna mika sakon ta'aziyarmu ga Mai Girma Chiroman Kano Hakimin Gwale Alh. Lamido Ado Bayero da Sardaunan Kano Malam Ibrahim Shekarau da Dan Darman Kano Hakimin Kura Prince Bello Ado Bayero da Dan Majen Kano Sanusi Lamido Sanusi da Galadiman Maitsidau Alhaji Magaji Galadima da Gwamnatin Kano dukkan iyalan Mai Martaba Sarki da kuma al'ummar jihar Kano baki daya. Allah ya jikansa ya gafarta masa.

Yasir Ramadan Gwale
06-06-2014

Thursday, June 5, 2014

Yadda Aka Yi Nadin Wazirin Kano Da Gwamnati Ta Taka!!!

YADDA AKA YI NADIN WAZIRIN KANO DA RAWAR DA GWAMNATI TA TAKA!!!

Kamar yadda na yi bayani a rubutun da ya gabata a jiya, bayan rasuwar Wazirin Kano Sheikh Isah Waziri Allah ya jikansa, Mai Martaba Sarki ya tafi jinya Landan inda ya shafe kwanaki 78 baya Kano. Bayan dawowar Mai Martaba Sarki ne, Malam LDC ya je gaida Sarki da yi masa barka da zuwa da ya jiki, sun kuma tattauna da Sarki a kebe, bayan fitowar Malam LDC ne ya fara bada sanarwar nadashi a matsayin sabon Wazirin Kano. A bisa al'ada ta Mai Martaba Sarki (Allah ya kara masa lafiya), babu wani nadi da yake yi na wata Sarauta face ya shawarci Emirate Council dan tattaunawa da jin shawarwarinsu akan mutumin da ya dace a baiwa Sarauta kaza. Amma cikin kaddarawa tasa Subhanahu Wata'ala, a wannan marra sai Mai Martaba Sarki ya tabbatarwa da Malam LDC Sarautar Wazirin Kano ba tare da shawarar Emirate Council ba, wannan kuma ta sanya da dama daga cikin Manyan Hakimai da manyan fada da suka ji labarin nadin haka daga sama, abin ya zo musu da bazata.

Bayan da labari ya fara bazuwa ne daga Malam LDC cewa na nada shi Wazirin Kano, sai wasu daga cikin manyan 'yan Majalisar Sarki suka tambayi Uwar Soro gaskiyar wannan labari, nan ta ke ta garzaya ta tambayi Sarki akan rade-radin da suka ji a gari cewa mai Martaba ya nada Malam LDC sarautar Wazirin Kano, Mai Martaba kuma ya tabbatarwa da Uwar Soro cewa eh shi ya yi wannan nadin! A shekaru 51 da Mai Martaba Sarki ya shafe yana Sarautar jihar Kano kusan komai yana yinsa ne da Shawara, amma cikin jarrabawa ta ubangiji aka jarrabi Mai Martaba Sarki akan wannan nadi, dan haka ne da dama suka karbi wannan a matsayin ajizanci irin na dan Adam, duba da cewa Shekaru sun yiwa Mai Martaba Sarki yawa, gabbansa sunyi rauni, Allah ya kara masa lafiya.

Bayan wannan nadi da mai martaba Sarki ya yi, ya kuma sauya wasu Sarautu tare da nadin Sabon Hakimin Kura sannan aka sauya masa Sarauta daga Tafidan Kano Hakimin Kura zuwa Dan Darman Kano. Mai Martaba Sarki kuma ya yi umarni da a rubuta takarda a sanar da gwamnati wannan nadi da aka yi. To a gefe guda kuma jama'a suka fara yin gunaguni akan cancanta da dacewar Malam LDC akan wannan kujera ta Wazirin Kano, inda da dama suka yi korafi ta hannun manyan fada akan su roki Sarki ya sake Shawara akan wannan nadi da ya yi. A dab da faruwar wannan lamari kwana uku ko hudu kafin wannan nadi Mai Martaba Sarki zai yi, Mai Girma Gwamnan Kano ya je gidan Sarki inda ya gana da Sarki yake nemawa Dan Majen Kano Malam SLS Hakimcin Kura, Sarki ya baiwa Gwamnan hakuri akan tuni an riga anyiwa Bello Bayero sauyin Sarauta zuwa wannan sarauta kasar Kura.

Daga nan turka-turka ta kunno kai akan wannan nadi, inda gwamna ya samu irin wadancan korafe-korafe da aka yiwa Fada akan nadin Malam LDC, nan shima ya hau kujerar naki akan wannan nadi, labari yaje har kunnen Sarkin Musulmi a bisa abinda ke faruwa akan wannan nadi da Mai Martaba Sarkin Kano ya yi da kuma tirjiyar da gwamnatin Kano ta yi akan wannan nadi, cikin gaggawa Mai Alfarma Sarkin Musulmi ya aiko da Manzo na musamman daga Sakkwato domin yazo ya binciki me ke faruwa tsakanin Gwamnati da Masarautar Kano, an turo Magajin Garin Sakkwato domin ya ji me ke faruwa kuma ya yi kokarin sasantawa idan zai iya. Cikin ikon Allah aka lallabi Sarki akan ya duba koken da al'umma suka yi ya yi wani abu da zai sanya farinciki a zzukatan al'ummar kano akan wannan batu. Mai Martaba Sarki ya gamsu ya sauya ra'ayinsa akan wannan nadi.

A gefe guda kuma ita Gwamnati ta ki karbar nadin da aka yiwa Hakimin Kura da kuma Wazirin Kano da sarautu guda hudu da aka sauya. Daman akwai jikakkiya tsakanin Mai Girma Gwamna Dr. Dr. Rabi'u Musa Kwankwaso da wanda aka nada a matsayin Wazirin Kano, amma ko kusa wannan ba shi ne dalilin da ya sanya gwamna ya ki yarda da nadin ba, illa wasu al'amura da suka wakana wanda nan ba muhallinsu bane.

Bayan anyi wannan nadi Malam LDC na shirin fara tafiyar da Sarautar Waziri, al'amura suka yi dumi dangane da nadin, har ta kai Mataimakin Gwamna ya yi magana da yawun Gwamnti cewar basu aminta da wannan nadin ba. kamar yadda na fada a baya, bayan da aka roki sarki kuma ya aminta yabi abinda jama'arsa ke so ya bada umarnin a warware wannan nadi kwana uku bayan an nada Malam LDC, a nan ne murna ta koma ciki ga Malam LDC sannan a gefe guda kuma jama'a na murna da jinjina ga Mai Martaba Sarki a bisa yadda ya karbi koke-koken al'umma ya sanya farinciki a zukatansu. A dan haka ne aka umarci Wamban Kano babban Dan Majalisar Sarki ya yi taron manema labarai ya shaidawa duniya cewar an warware wannan rawani da aka nadawa Wazirin Kano Malam LDC.

A dan haka, wanda yafi cancanta da a yaba masa a wannan al'amari da ya faru shi ne Mai Martaba Sarki Alhaji Dr. Ado Bayero Allah ya kara masa lafiya, domin Sarauta ce da hakkinsa ne ya nada duk wanda yaga dama, amma ya sarayar da wannan hakki nasa dan sanya farinciki a zukatan al'ummar Kano, sannan bangare na biyu su ne Manyan 'yan Majalisar Sarki da kuma manyan hakimai da suka tsaya kai da fata wajen ganin kimar Masarautar Kano bata zube kasa ba akan wannan sarauta, sai kuma sashi na uku, wanda ita ce Gwamnatin Kano, wanda itama a nata bangaren ta yi kokari wajen ganin ta saurari koke-koken al'umma ta kuma yi abinda ya dace akai.

Alhamdulillah, yanzu kusan dukkan wata 'kura da ta taso tsakanin Fadar Mai Martaba Sarki da Gwamnatin Kano akan wannan nadi ta lafa kuma an fahimci juna an kuma yafewa juna akan abinda ya faru na 'yar turka-turkar da ta faru a tsakani. A hakikanin gaskiya wannan shi ne zahirin abinda ya wakana a yayin wannan nadi da aka yi illa iyaka na tsallake wasu abubuwa da ba lallai ne a fadesu a bainar jama'a ba. Muna fatan Malam LDC zai karbi wannan abu a matsayin kaddara da ta fada masa, muna kuma yi masa fatan alheri tare da kira a gareshi ya ji tsoron Allah ya kyautata tsakaninsa da Allah, sannan kuma ya kyautata tsakaninsa da al'umma. Akwai abin tsoro matuka ace al'umma su yiwa mutum mummunar Shaida. Allah ya tabbatar da mu akan gaskiya ya bamu ikon aiki da ita.

YASIR RAMADAN GWALE
06-06-2014

Me Ya Sa Mutanen Kano Basa Son Dan Chakare A Matsayin Wazirin Kano?[2]

ME YA SA MUTANEN KANO BASA SON DAN CHAKARE A MATSAYIN WAZIRIN KANO? [2]

A bayanin da na kawo jiya akan Malam Liman Dan Chakare, wasu suna cewar wai muna yiwa Malam Liman kazafi, babu shakka duk wanda yace abinda aka fada kazafi ne ko san rai, to babu shakka bai san waye Liman Dan Chakare ba. Akan wane dalili zamu yiwa Liman Dan Chakare kazafi bayan mun san laifin hakan yana da girma a Shari'ah. Wallahi duk wanda ya san waye Liman Dan Chakare to ya san cewa ba'a fadi komai akansa ba.

Ya isa abin misali a fahimci waye Liman Dan Chakare, ga duk wanda ya san badakalar da ta faru tsakaninsa da iyalin gidan Abacha zai tabbatar da dukkan maganganun da aka yi akansa. Malam Liman Dan Chakare ya yi amfani da sunan Mai Martaba Sarki Allah ya kara masa lafiya ba da sanin Sarki ba, ya dinga karbar kudi a hannun iyalin Abacha akan tsarewar da aka yiwa su Muhammad, karshe da dubu ta cika Maryam ce da kanta ta zo ta samu Sarki akan batun, Mai martba Sarki ya  tabbatar mata cewar shi bai taba sanya Liman Dan Chakare ya karbi wani abu da sunansa ba akan matsalar da ta faru. Wannan wata badakala ce da ta faru tun bayan tsare su Mohammed Abacha, wadan da suka san al'amarin sun sani, wadan da basu sani ba kuma iyalin Abacha na nan da rai za su bada bayani.

Bayan rasuwar Maarigayi Malam Isah Waziri, Mai Martaba Sarki ya tafi jinya Landan inda ya shafe kwanaki 78 baya gari, bayan dawowar Mai Martaba Sarki ne Liman Dan Chakare ya samu Sarki shi da shi suka gana, daga baya Liman Dan Chakare ya dinga bayar da sanarwar an nada shi WAZIRIN KANO, mukamin da daman ya jima yana neman a bashi. Ba tun yanzu Liman Dan Chakare ya so Wazirin Kano ba, tun bayan rasuwar Waziri Gidado Allah ya jikansa, ya so Mai Martaba Sarki ya bashi wannan Sarauta amma Mai Martaba bai yi hakan ba, duk da cewar Sarauta ce da mai martaba yake nada abokansa da aminansa, sai a yanzu da Shekaru suka yiwa Mai Martaba Sarki yawa gabbansa suka yi rauni, ajizanci ya riske shi abinda ya faru ya wakana.

A wannan nadin da aka yi masa, ta tabbatar cewar Fadar Masarautar Kano tana sauraron koke-koken al'umma, domin tun bayan sanarwar wannan nadi jama'a suka dinga kai korafinsu akan Malam Liman Dan Chakare da kuma bayanin irin halin da za'a iya shiga idan LDC ya cigaba da kasancewa Wazirin Kano. Wani abin da zai kara nunawa duniya waye LDC shi ne, daga bashi wannan Sarauta sai ya aikawa da iyalan Marigayi Malam Isah Waziri Allah ya jikansa da takarda yana umartarsu da su tashi daga gidan Wazirin Kano su koma wani wajen daban cikin awanni ashirin da hudu (24) yana san ganin Kangon gidan, iayalan Malam Isah Waziri sun shiga damuwa matuka da wannan wasika, kuma cikin nufin ubagiji Allah ya share musu hawaye aka ware masa nadin da aka yi.

Wadan da suka san Liman Dan Chakare sun san yadda yake kulafucin wannan Sarauta ta Wazirin Kano, an kuma sha jinsa yana maganar cewar ko sama da kasa zata hade sai ya zama Wazirin kano, cikin kaddarawa taSa Subhanahu Wata'ala, sama da kasa basu hade ba, Liman Dan Chakare ya zama Wazirin Kano na kwana hudu kacal! Wannan ko shakka babu dole tarihi ya rike, dole LDC ya shiga lissafin wadan da suka taba zama Waziran Kano. Har ila yau, da dama sunji LDC da bakinsa yana maganar wani Mafarki da ya ce yayi wanda duk mai hankali yasan wannan mafarki ba gaskiya bane, wanda wannan zai tabbatar da waye LDC. Wasu da dama suna koarin ai bamu fadi alkhairansa ba sai muke fadin kishiyarsu, mukam har ga Allah sai dai muce mun san cewa Malam LDC  Malami ne mai huduba mai Tamsiri, amma ayyukansa na zahiri su ne zasu tabbatar da gaskiyar ko waye shi, haka kuma, Shaidar da jama'a suka yi akansa kadai ta isa abin Misali akan waye shi.

Al'ummar kano da dukkan gwamnatocin da aka yi a kano masu tsananin biyayya ne ga mai martaba Sarki tare kuma da karbar dukkan wani abu da ya zo daga hannun mai martaba Sarki, amma akan Malam LDC al'umma suka nuna rashin gamsuwarsu da wannan nadin, kuma Mai Martaba Sarki ya ji ya karba ya kuma Aminta ya kuma bada umarnin da a ware nadin da aka yi, muna kara jaddada godiya da addu'o'in fatan alheri ga Mai martaba Sarki, Allah ya kara masa lafiya da nisan kwana. Shi kansa wannan nadi da abinda ya faru a lokacin nadin akwai al'amura da yawa a ciki masu ban mamaki wanda nan ba Muhallin fadinsu bane. Amma lallai al'umma su sani, babu wani abu da aka fada akan Malam Liman Dan Chakare wanda ba haka yake ba. kuma ina sake fada, duk wadan da suka Sanshi sun san ba'a fadi komai akansa ba. Malam LDC Dan uwanmu ne Musulmi, muna yi masa addu'ar Allah ya shiryeshi da mu baki daya shiriya ta gaskiya, Allah ya nuna mana gaskiya ya bamu ikon aiki da ita, ya nuna mana kraya ya bamu ikon kauce mata. Wadan da suka ji haushin abinda aka fada sai su gafarce mu, dama shi harshe na gaskiya kaifi gareshi.

YASIR RAMADAN GWALE
06-06-2014

Wednesday, June 4, 2014

Me Ya Sa Mutanen Kano Basa Son Dan Chakare A Matsayin Wazirin Kano?[1]

 
ME YA SA MUTANEN KANO BASA SON DAN CHAKARE A MATSAYIN WAZIRIN KANO? [1]

Da farko yana da kyau mu san waye Dan Chakare. Asalin Nassir Muhd Nassir da aka fi sani da Dan Chakare almaijiri ne na Malam Liman Dan Amo da yake a unguwar Daneji a cikin birnin kano, a lokacin da Dan Chakare yake matsayin almajiri bai cika maida hankali akan karatun addini ba, illa iyaka ya shahara da baiwa 'yan uwansa almajirai labarin Sarakunan zamanin da suka Shude irin tarihihi na Alfu-Laila-Wa-Laila ko Dare Dubu Da Daya, da Malam Liman Dan Amo ya lura cewa Nassiru baya karatu sai bayar da labarai barkatai, sai yake sanar masa cewa tunda ka iya bada labari ni zan kaika fadar Mai Martaba Sarkin Kano dan ka dinga sanya Sarki Nishadi da irin wadannan labarai naka, haka kuwa aka yi, Malam Liman Dan Amo ya je wajen Mai Martaba Sarki ya gabatar da Nasiru Muhd Nasiru a matsayin zai dinga kawo shi yana Nishadantar da Sarki, idan sarki ya bukaci yin nishadi sai ya sanar da Malam Liman Dan Amo, shi kuma ya zo da Nasiru fada dan ya baiwa Sarki Dariya da labaransa. Haka kuwa aka yi, duk lokacin da Sarki ya yi nishadi sai ya tura a sanar da Malam Liman Dan Amo ya zo da Nasiru dan ya baiwa sarki Dariya.

Ana haka, sai Dan Chakare ya samu shiga wajen Sarki, har ta kai yana zuwa ya baiwa Sarki labari shi kadai ba tare da ya sanar da Liman Dan Amo ba, ana haka sai Dan Chakare ganin ya samu shiga a wajen Sarki ya dinga yin rashin kunya ga manyan Hadiman Sarki, sannan kuma ya dinag Shiga Gidan Sarki babu Sallama. tafiya ta tafi har suka samu sabani da sarki ya daina zuwa wajen Sarki bayan da Sarki ya sa aka koreshi.

Daga nan ne ya koma wajen Khalifa Isyaka Rabi'u inda yake zama wajensa suna yin hira yana bashi labari, har ta kai shima, Malam Isiyaka Rabi'u ya yarda da dan Chakare ya dinga yin 'yan tafiye-tafiyensa na kasuwanci tare da Dan Chakare, a saboda amince masa da isiyaka Rabi'u ya yi, sai ya fara damfarar Isiyaka Rabi'u yana yi masa abubuwa na rashin gaskiya. Wannan ta sanya Khalifa Isiyaka Rabi'u ya kira taron Manema labarai ya nesanta kansa da Dan Chakare ya kuma yi kira ga dukkan abokan huldarsa da su kauracewa mu'amala da Dan Chakare.

Bayan da suka yi baram-baram da isiyaka Rabi'u sai Dan Chakare ya sake dawowa jikin Sarki bayan ya nemi afuwa da kuam 'yan dabarce-dabarcensa na Almajiranci, wannan karon ya cusa kansa fiye da yadda yake a baya a cikin fadar Sarki. Daga nan ne sarki ya fara sanya shi a cikin lamuransa. Har ya zama Alkali ya dinag aikata rashin gaskiya da musgunawa jama'a, wannan ta sanya a Unguwar Danaeji da Dan Chakare yake zaune Jama'a suka yi masa dukan tsiya suka koreshi daga unguwar, daga nan ne ya koma Unguwar Hausawa dake kusa da Kundila. Yana zaune yana zuwa wajen sarki yana gayawa Sarki karya da gaskiya kuma yana bin Sarki da 'Yan Tsatsube-tsatsubensa na ganin ya samu shiga a wajen Sarki har Mai Martaba Sarki ya sanya aka nadashi babban Limamin Masallacin Waje, wanda shi ne masallaci na biyu a Kano. Ko da Dan Chakare ya fara Limanci a Fagge ya dinga tsanantawa mutane ta hanyar yin doguwar huduba da karanta Doguwar Sura da nuna isa da gadara a cikin Huduba, domin yana yawan kiran Masu Saurarensa da Matsiyata ko Talakawa fakirai da sauran kalamai marasa dadi, haka nan kuma yakan sanya a kundume bishiyun masallaci a lokacin da ake tsananin zafin rana.

Bayan da yaga ya samu Shiga a wajen Sarki ya dinga yiwa dukkan mutanan fada Girman Kai da nuna isa, ta yadda baya ganin kimar kowa a fada idan ba Sarki ba. Nan Sarki ya sanya shi ya dinga yin Limancin Sallar Idi idan Limamin Masallacin cikin gari ya tafi Makkah Umara ko aikin Hajji, haka dai Dan Chakare ya dinga nuna isa da dagawa da takamar cewa shi wani ne. Ya cusa kansa a dukkan wasu al'amura da suka shafi addini a fadar Masaraurat Kano.

Kasancewar Dan Chakare ya yi karatu a Madina, Sheikh Dr. Ahmad Ibrahim Bamba (Darul Hadith) da suka yi karatu tare ya taba cewa Malam Nassir yana daya daga cikin Dalibai masu hazaqa a tsakanin daliban lokacin, mutum ne mai kaifin kwakwalwa, amma yace babu ko shakka akan cewa Malam Nassir ba karamin tadari bane a lokacin da yake Dalibi a Madina, domin yana dalibi ya taba aske gemunsa ya zuba a cikin ambulan ya kaiwa Sheikh Bin Baz saboda nuna tsageranci, ya ce wannan kadan ne daga cikin irin takadaranci irin na Malam Nassir a lokacin da yake Madina,

Wadan da suka san Dan Chakare sun shaide shi da cewa mutum ne mai girman kai da san nuna isa da san Mulki. Mutum ne mai Shaddadawa a cikin al'amuransa, a dukkan cikin Malam da suke kano babu wani malami da ya nunawa Sunnah kiyayya a fili irin Dan Chakare domin yana daga cikin Malaman da suka san meye Sunnah amma suke mata zagon kasa da shirya mata dukkan kutunguila da Makida wajen ganin an tadiye tafiyar Sunnah a Kano. Malam Jaafar Adam (Rahimahullah) ya fada a cikin wata lakca da aka yi a Masallacin Usman Bin Affan Gadankaya mai suna #GwagwarmayaTsakaninKaryaDaGaskiya, cewa Limamin Waje yana bin dukkan hanyoyi a fada wajen ganin an kuntatawa Sunnah da Ahlussunnah.

Abu mafi muni a tattare da Dan Chakare shi ne yadda yake nuna goyon bayansa ga SHI'AH dan muzgunawa Ahlussunnah. A baya lokacin da Masallacin Aliyu Bin Abi-Talib dake dab da Randabawul na dangi a Kano, 'yan Shi'ah sun yi kokarin mamaye Masallacin ta hanyar shirya taruka da wa'azozinsu a wajen, wannan ce ta sanya 'yan Boko masu fahimtar Addini dake Sallah a Masallacin suka sanar da Manya a Kano dan a sauyawa masallacin suna daga Masallacin Aliyu Bin Abi-Talib zuwa Masallacin Umar Bin Khattab, cikin nasarar ubangiji kuwa aka sauyawa masallacin suna, tun lokacin da Masallacin ya koma sunan Umar Bin Khatab 'yan Shi'ah basu sake zuwa masallacin dan yin taro ko lakca ba, a dan haka ne, Dan Chakare ya kiraye su zuwa Massalacin Waje da aka fi sani da Masallacin Fagge inda yake limanci ya basu cikakkiyar damar yin dukkan tarukansu da al'amuransu, ba dan komai ba sai dan nuna tsananin kiyayyarsa da gabarsa ga Sunnah.

Zan cigaba In Sha Allah zuwa gobe, ku dakace ni.

YASIR RAMADAN GWALE
04-06-2014

WAZIRIN KANO: Mai martaba Sarkin Kano Ya Nuna Dattako!

WAZIRIN KANO: MAI MARTABA SARKIN KANO YA NUNA DATTAKO!

Kwana hudu bayan da Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Dakta Ado Abdullahi Bayero ya nada sabon Wazirin kano bayan rasuwar Sheikh Isa Waziri, turka turka ta kaure tsakanin fadar mai martaba Sarki da fadar Gwamnatin Kano, inda ta bakin mataimakin Gwamna Abdullahi Ganduje, gwamnati ta bayar da sanarwar kin amincewa da nadin da mai martaba Sarki ya yiwa Sheikh Nassir Nassir Muhammad a matsayin sabon wazirin Kano, ta kuma umarci fadar maimartaba Sarki akan ta warware wannan nadi da ta yiwa Sheikh Nassir a cewar Gwamnati al'umma basu yi na'am da nadin na Waziri da aka yiwa Sheikh Nassir ba.

Wannan shi ne karo na farko da sa'insa irin wannan ta faru a bainar jama'a tsakanin Masarauta da Gwamnati. Sananne ne a tsarin Mulki cewar gwamnati tana gaba da masarauta a sha'anin iko da gudanar da al'amuran mulki na al'umma. Duk da cewa wannan nadi da maimartaba Sari ya yi, hakkinsa ne ya nada duk wanda yaga dama a matsayinsa Wazirinsa a cikin fadarsa. kamar yadda ya tabbata a tarihi, a lokacin Sarkin Kano Alu Dan Abdullahi Maje-Karofi aka fara nada wannan sarauta ta wazirin Kano, kuma ya nada wannan sarauta ne ga mafi kusanci da shi, kuma daman bisa ga al'ada a lokacin akan kira dukkan wani wanda yake da kusanci da Sarki kuma Shakuwarsu da Sarki ta bayyana da sunan Wazirin Sarki, ance a lokacin Sarki yafi shakuwa da Dansa kuma Galadiman kano Abdullahi a lokacin da haka Sarki ya nada sh Wazirin Kano kuma Galadiman Kano, tundaga wannan lokacin aka fara ayyana Wazirin kano.

 haka kuma, zamanin Sarki Alu ya nada wansa Ahmadu Mai Shahada a matsayin Wazirin Kano. haka nan, bayan shudewarsa Sarki Abbas ya nada Audu-Lele dan gidan tafidan kano Muhammadu maje-takai a matsayin Wazirin kano; bayan da turawan Mulki suka tunkude  ne tare da dukkan hakimansa da manyan fada suka nada wani bawan Sarki mai suna Dan-Rimi Ala-Bar Sarki a matsayin sabon Wazirin Kano; daga nan ne kuma Sarki ya cire wannan bawa ya nada wani malamin Addini mai suna Gidado a matsayin sabon Wazirin Kano; bayan rasuwar Malam Gidado ne kuma Sarkin Kano Abdullahi Bayero ya so ya nada wani Shehin Malami mai suna Sulemanu wanda shi ne Ma'ajin kano kuma aminin Sarki ne a matsayin sabon Waziri amma jama'ar gari suka nuna rashin gamsuwa da yunkurin nadin Malam Sulaimanu da Sarki yake son yi a matsayin sabon Wazirin Kano, a lokacin ne Mai Babban Daki Mariyatu Mai-Harara ta sanya Sarki janye wannan nadin da ya yi niyyar yi, a dan haka sai ya sauyawa Sulaimanu Sarauta inda ya nada shi Walin Kano kuma ya damka dukkan ayyukan waziri a hannunsa.

A dan haka ne, mai Martaba Sarki a lokacin ya fasa nada Wazirin Kano har kusan tsawon Shekaru 23 babu Wazirin Kano. Wannan a takaice yana nuna cewar sarautar WAZIRIN KANO Sarauta ce Wadda Sarki yake nada ta ga Aminansa wadan da suke ko dai limamai ko kuma Malamai masu ilimi. A saboda haka idan Mai-martaba Sarki ya nada Sheikh Nassir da aka fi sani da DAN CHAKARE a matsayin Wazirin Kano Sarki bai yi wani abu na kauce ka'ida ba, domin a al'adar nadin Sarautar Sarki na da ikon nada wanda yaga dama.

Duk da cewar Mai Martaba Sarki Allah ya kara masa Lafiya, yana da masaniyar cewar hakkinsa ne ya nada wanda yaga dama a matsayin Waziri amma ya yarda ya sarayar da wannan hakki nasa dan samun dorewar zaman lafiya tsakanin fadar Gwamnati da Masarauta, babu ko shakka Mai Martaba Sarki ya nuna Dattako a janye wannan nadi da ya yi.

ME YA SA MUTANE BASA SON DAN CHAKARE A MATSAYIN WAZIRIN KANO? Wannan shi ne abinda zamu duba a rubutu na gaba In Sha Allah. muna fatan Allah ya kwantar da wannan kura da ta taso tsakanin gwamnati da Masarautar kano. Allah ya taimaki Sarki ya karawa Sarki lafiya.

YASIR RAMADAN GWALE
04-06-2014

Tuesday, June 3, 2014

Matsalar Boko Haram!!!

BOKO HARAM: Da yawa daga cikin 'yan Arewa sun gamsu cewa matsalar Boko Haram ba zata zo karshe ba sai nan da 2015 idan dan Arewa "musulmi" ya zama shugaban kasa. Shi ya sa da dama suke ganin kyashin a tallafawa wannan gwamnati ta magance matsalar a rage salwantar rayuka da dukiyoyi, sun gwammace a yi ta kashe mutane daga nan har zuwa lokacin zabe, alabashshi idan namu ya samu sai a sake sabon lale. Maganganun mutane da yawa sun nuna haka. Bayan haka kuma, da karfi da yaji wasu suka ki yarda su fahimci gaskiyar wannan al'amari, ta yadda daga zarar mutum ya yi magana kan shawo matsalar sai a fara kallon waye shi dan wace jam'iyya ne, alhali kuma ga jama'a na ta rasa rayukansu dare da rana, kasuwanni na komawa kufai, yara na komawa marayu, mata na komawa zawarawa yanzu dai mu kalli yadda Jihar borno ta koma kamar Mogadishu!

Duk da maganar da Gwamnan jihar Borno Kashem Shettima ya yi na cewa wadannan 'yan Ta'addan na Boko Haram yaransu ne na Kanuri 'yan jihar Borno amma har yanzu wasu da suka yiwa lamarin nisa sun ki yarda su fahimci gaskiyar magana akan BH. Kwatsam kuma sai gashi dan majalsar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Bama, Ngala da Kalabalge Abdulrahman Terab ya sake tabbatar da cewar wadannan yaran da suke kai hare-haren nan babu ko tantama yaransu ne na jihar Borno! Wannan ita ce magana ta gaskiya, daga lokacin da muka tsaya cikin tsanaki muka fahimci gaskiyar al'amari dangane da BH to a lokacin muka sanya dambar magance matsalar, amma muddin aka cigaba da kauda kai a gareta ana alakanta laifin da wasu mutanen daban to zamu jima bamu fita daga cikin wannan matsaar ba, domin ba dan Arewa ba ko Sa Ahmadu Bello ne zai dawo ya zama Shugaban Kasa a 2015 haka nan matsalar zata cigaba da yaduwa, Allah ya kiyaye.

Allah ya sakawa Gen. Buhari da alheri, duk da kasancewarsa dan Adawa na wannan gwamnati amma ya yi bayani na gaskiya akan cewar dole a hada hannu da karfe a taimakawa Gwamnati wajen kawo karshen wannan matsalar ta BH a yankin Arewa maso gabas. Lallai gwamnati ita kadai ba zata iya kawo karshe wannan al'amari ba, har sai al'umma ta hadu gabaki daya wajen yakar lamarin, yau ko gwamnati ce ke da hannu a lamarin matukar al'umma sun tashi tsaye da gaske to sai sun kawo karshen abin.

Na fahimci wasu 'yan siyasa da dama musamman daga Arewa basa son wannan gwamnati ta shugaban kasa Dr. Goodluck Jonathan ta kawo karshen lamarin dan suna ganin Gwamnatin zata samu wani credit da su basa bukatar ta samu saboda siyasa, a dan haka wasu ke kafar ungulu dan dakile samun nasarar yakar 'yan ta'addar, Allah shi ne masani. Amma lallai mu sani cewar, kullum kwanan duniya al'ummarmu ne suke rasa rayukansu a sanadiyar wannan rikici da aka sanya siyasa dumu-dumu a cikinsa.

A nata bangaren kuma, gwamnati ya kamata ta ji tsoron Allah ta bi hanyoyi na gaskiya wajen kawo karshen wannan al'amari. Allah ya kawo mana karshen wannan tashin hankali.

YASIR RAMADAN GWALE
03-06-2014

Sunday, June 1, 2014

Tsakanin Larabawa da Turawa da bakaken fata!!!

Da ba dan Turawa ba da har yanzu Larabawa suna cikin duhun kai da nuna isa da Girman Kai da fariya da alfahari da nuna tsananin kyama ga wanda ba Balarabe ba musamman Bakar fata. A yanzu babu wadan da Larabawa suka dauka da mutunci kuma suka dauka su ne mutane suke girmamasu kamar Turawa, amma kuma shi Bature baya kyamar mutane dan saboda launin fatarsu a halin yanzu, sukan dauki mutane duk daya, wannan ta sanya Larabawa suka fara dawowa daga rakiyar karkataccen tunanin kyamar Bakaken mutane domin Turawan da suke zakwadi akansu su basa kyamar Bakar fata a zahiri idan Mu'amala ta hada kamar yadda Larabawa suke yi babu kunya babu tsoron Allah. Kadan ne daga cikin Larabawa wadan da suka yi Ilimi suka waye ta fannin Addini da Rayuwa suke girmama mutum ba tare da la'akari da launin fatarsa ba.

Zaka sha mamaki idan aka ce maka idan banda 'yan wadansu Shekaru kalilan Larabawan Palasdinu da Mafiya yawan Bakar fata Musulmi suke jin zafi da radadin halin da suke ciki na kunci da kaskanci arkashin danniya da muzgunawar Israela cewa sun tsani bakar fata, haka sauran larabawa da dama suke, Larabawan gaskiya da na karya! Domin da yawan larabawan da suke cewa su Larabawa ne a yanzu Barbarar yanyawa ne galibinsu kabilu ne, idan ka cire Sa'udiyya da Yemen da wani sashi na Iraqi da Bahrain da Palasdinu da Kuwaiti da Daular Larabawa da Qatar, amma mafiya yawancin sauran ba Larabawan gaskiya bane irinsu Masar da Jordan da Syria da Lubnan da Oman da Aljeriya da Morocco da Tunisiya da wagairuhum, kamar yadda galibin 'yan Israela suma ba Yahudawan gaskiya bane.

Da yawan Larabawa indai kai Bakar fata ne kawai su a wajensu Musulunta ka yi, dan haka suke mu'amalantar bakaken fata musulmi kamar sabbin Musulunta. Wani abin almara da ya taba faruwa da ni, wata Malamarmu Balarabiya kanta babu dankwali siket dinta iya kwabri, gani da gemu irin na Ustazai ga tabon Sallah a goshi na amma wai tana tambaya ta wai ko ni din Musulmi ne! kaji Larabawan zamani. Alhamdulillah, ya zuwa yanzu jinsin Bakar fata na kara wanzuwa sosai a tsakanin kabilun Larabawa domin hatta a gidan Sarautar Saudiyya akwai Bakar fata kuma tsatson Al-Sa'ud domin ta tabbata Sarki Faisal Allah ya jikansa ya auri Bakaken fata masu asali daga Afrika. Allah da yayi mutanan Turkiyya farare Tas ya yi mutanan Khaleej masu haske shi ne wanda ya yi Bakaken fata a Kenya da Sudan Ta Kudu da Burkina faso. Babu wanda ya fi wani a wajensa Subhanahu Wata'ala sai wanda yake da TsoronSa. Ya Allah ka azurtamu da tsoronka.

YASIR RAMADAN GWALE
01-06-2014