Sunday, December 21, 2014

Siyasar 2015 An Kai Arewa An Baro


SIYASAR 2015 AN KAI AREWA AN BARO

Shi fa yaki irin na siyasa dan zamba ne, dole ayi shirin tunkararsa indai da gaske yakin za'a yi. Dole kayi nazarin kanka a karon farko, kasan waye kai me zaka iya, meye karfinka, meye rauninka, meye manufarka, me kake san cimmawa; sannan kuma, sai ka nazarci abokin fito na fito, meye karfinsa, meye yake nema da zai iya cin lagonka da shi, wanda daman kai tuni ka gama sanin wadan can hanyoyi ka gama nazartarsu, dan haka ko da abokin fito na fito ya taso maka kana da dukkan dabaru da kai tanadi na kare kanka daga duk wani yunkuri irin nasa. Dole kuwa kai haka, domin kaine ka taro yakin ba shi ne yazo ya sameka ba, dan haka ne aka Ruwaito Manzo SAW idan zai fita Yaki yakan nufi Gabas alhali kuma inda zai tunkara a yamma yake, wannan dabara ce ta yakin da ake neman cin nasara da gaske.

Manyan 'yan Siyasa daga Arewa tun lokacin da aka fara fuskantar 2015 sukai ta batun dole sai mulkin Najeriya ya koma Arewa. Alhali babu wani shiri da akayi dan hakan, wace Manufa Arewa take da ita gamammiya idan Mulkin ya dawo Arewa? duk da dai kawai yaudara ce kawai ake yi da sunan Arewa, kuma galibi Talakawa sune ke bata lokacinsu da sunan Arewa, dan nasan babu wani dan siyasa da zai ce yana yin siyasar Neman Mulki kuma yace da sunan Arewa yake yi. Shi yasa galibin masu kiran Arewa, kodai 'yan Siyasar da ba neman Mulki suke ba, kawai basa san a manta da su ne shi yasa suke kiran Arewa, ko kuma wasu mutane ne da ba zasu iya sanyawa ako hana komai ba. Daman kuma Talaka maganarsa bata cika tasiri ba a wajen masu mulki.

Shin masu fatan mulki ya dawo Arewa wane tanadi suka yiwa hakan? Idan Mulki ko Shugabancin Najeriya ya dawo Arewa me suke san cimmawa, ko kuwa kawai muna san Mulki a suna ace wane dan Arewa shi ne Shugaban kasa alhali kuma babu wani abu da zai iya kullawa! Na farko dai tun ran gini tun ran zane, wadan da suka ginamu akan kabilanci sunyi kuskure. Shi yasa aka wayi gari babu wani da yake batun Najeriya a siyasance, dan kudu fatansa dan kudu ko da kuwa babu wani abu da za'a tsinanawa mazabarsa, haka shima dan Arewa, ai bincike ya nuna cewa da dama daga cikin mutanan kudu maso kudu suna cikin mawuyacin halin rashin aikin yi da rashin karatu, duk kuwa da cewa sitiyarin da ke jan Najeriya dan garinsu ke tukashi.

A ganina da wahala Mulkin Najeriya ya iya dawowa Arewa a hannun jam'iyyar hamayya, idan maganata gaskiya ce, to Gwamnonin nan guda biyar ko bakwai da suka tada kayar baya a PDP kuma daga karshe suka fice suka koma APC sune suka kai Arewa suka baro! Wannan dai ra'ayi da tunani na ne, kuma gwargwadan abinda na gani na fahimta. Sai nake ganin kamar muna da saurin mantuwa, mun rudu da yawanmu alhali kuwa a Najeriya ba'a zaben gaskiya a matakin Shugaban kasa! Batun Arewa da Yarabawa kuwa aganina wani abu ne adukunkune mai rikitarwa, dan kuwa mai yasa ba'a dauko Kayode Fayemi da ya fadi zaben Gwamnan Ekiti an bashi mataimakin Buhari ba? Duba da cewa sananne ne kuma anga kamun ludayinsa, amma aka dauko tsohon kwamashina alhali ga Gwamna da yake da dukkan kwarewa ta Mulki! Wannan fa wata katuwar ayar tambaya ce, amma duk aka ja baki akai gum... Zan cigaba In sha Allah.

Yasir Ramadan Gwale
21-12-2014

Sunday, December 14, 2014

Kwangwaratuleshans Janar Muhammadu Buhari


KWANGWARATULESHANS JANAR BUHARI

Assalamu Alaikum Warahmatullah. Sunana YASIR RAMADAN GWALE, ina mai yin amfani da wannan dama wajen taya Janar Muhammadu Buhari murnar lashe zaben fidda gwani a karon farko da aka kasa a faifai Janar yayi takara kuma ya lashe zabe. Ba shakka na san Zainab na cike da murnar samun wannan Nasara, ina kara tayata murnar samun wannan Nasara da GMB yayi.

Ina fatan Janar Buhari a matsayinsa na jagora zai rungumi kowa da kowa dan tafiya tare. Nasarar Buhari nasara ce ga Dimokaradiyya, a koda yaushe dimokaradiyya na alfahari da irin wannan damar da ake baiwa al'ummah dan bayyana ra'ayinsu na tsayawa zabe. Haka nan kuma ina taya Gwamnan Kano Rabiu Musa Kwankwaso murnar zamowa na biyu a wannan zabe, ba shakka Kwankwaso yayi kokari ya nuna iya siyasarsa, da yawa na ganin Atiku Abubakar ne zai zo matsayi na biyu, amma kwankwaso ya shammaci mutane. Ina kuma taya Atiku Abubakar din alhinin samun wannan matsayi na uku, na tabbatar ba haka ya so ba amma hukuncin Allah shi ne abin karba, kuma ya burgeni matuka da ya nuna jarumtaka ya karbi faduwa! Wannan ita ce kaiwa makura a dimokaradiyya duk da ba laifi bane neman hakki idan har wani yana ganin anyi masa ba daidai ba.

A daya gefen kuma ina taya tsohon mawallafin jaridar Leadership Newspapers Pharm. Sam Nda-Isiah murnar samun kuri'u guda goma ba shakka, na aminta da irin kishin kasa da kaunar Najeriya da Sam yake da shi, ina masa fatan Allah ya bashi wata dama da zai hidimtawa al'ummar Najeriya.

Haka kuma, Janar Buhari zai kuma fuskantar Shugaban Kasa Dr. Goodluck Jonathan dan yi wannan karon battar a karo na biyu. Tun a zaben da ya gabata na 2011 da yawan 'yan Najeriya masu bibiyar harkokin siyasa sun san lagwan kowa tsakanin Buhari da Jonathan. Fatana shi ne Allah ya saukaka mana al'amuranmu ya zabar mana shugabanni na gari adalai a dukkan matakai na shugabanci. Kuma in sha Allah zan taimaka da Naira 10,000 ga kwamatin yakin neman zaben Janar Buhari na BSO.

Ina taya murna ga 'yan uwanmu abokanmu 'yan Buhariyya musamman wadan da suka tayamu murnar samun Nasarar Malam Nuhu Ribadu da Malam Salihu Salihu Sagir Takai dama wadan da basu tayamu murna ba, da kuma masu yi mana mummunan fata, har da masu yi mana tadiya da mugun baki irinsu Mansur Manu Soro duk muna musu murnakuma muna yi musu adduar fatan alheri. Allah ya taimaki kasarmu Najeriya ya bamu nasara, ya amintar da mu ya bamu lafiya da zaman lafiya.

Cc: Ibrahim Sanyi-Sanyi, Muhammad Aliyu Dutsin-Ma, Kwamared Baban Shareek Gumel, Affan Buba Abuya, Sagir Musbahu Daura Dole, Hussein Abdussalam, Attahiru Muhammad Marnona, Abubakar Aminu Ibrahim, Bashir Ahmad, Sunusi ShehuSunusi Musa, Auwalu Lawan Aranposu, Hamza Ibrahim Baba, Abdulrashid Ahmad, Baba Bala Katsina, Ibrahim D Itsenyabi, Khaleel Nasir Kiru, Lawal Muazu Bauchi, Yamai Muhammad, Hk Yaradua, Husain Husain Kyar'adua, Uba Danzainab.

Bcc:....

Yasir Ramadan Gwale
14-12-2014

KHRTAOUM: Ban Kwana Da Ismail Lamido


KHARTOUM: BAN KWANA DA ISMAIL LAMIDO

Da fatan an sauka gida lafiya Malam Ismail Lamido. Allah ya saka da alheri da wannan takakkiya kuma ya bar zumunci. Muna godiya mara adadi ga Jagoranmu Sardaunan Kano Malam Kano Shekarau CON. Allah kuma ya bamu Nasara a wannan zabe. Allah ya baiwa Malam Saluhu Sagit Takai Gwamnan kano kuma ya yi masa jagoranci zuwa ga adalci da daidaito. Allah ya taimaki jihar Kano da Najeriya.

Yasir Ramadan Gwale
13-12-2014

Thursday, December 11, 2014

Taya Murna Ga Malam Shamsu Abbaty

L-R Shamsu Abbaty da abokinsa

TAYA MURNA GA MALAM SHAMSU ABBATY

Congratulations Malam Shamsu Abbaty. Allah ya sanya alheri ya yiwa rayuwarka albarka. Ba shakka yau muna cike da farinciki da farincikinka ka, zamu kasance cikin sahum masu murna da fatan alheri a wannan rana. Allah ya yi maka jagora ya ya sanya maka albarka.

A madadin Ni Yasir Gwale da Auntynka Zainab Gwale muna tayaka murnar wannan saukar karatu da ake yi a yau a Kamfala Uganda.

Yasir Ramadan Gwale
10-12-2014

Tuesday, December 9, 2014

Alhamdulillah Takai Yaci Zabe


ALHAMDULILLAH TAKAI YACI ZABE

Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin Sarki da ya nuna mana wannan Nasara ta Malam Salihu Sagir Takai da ya zama dan takararmu na Gwamna a Kano. Muna kara mika godiya ga Daliget da suka zabi cancanta. Allah ya bamu nasara a babban zabe mu kada madu bacci. Allah mun gode maka.

JIGAWA: Muna taya murna ga Malam Aminu Ringim bisa nasarar da ya samu. Allah ya nuna mana babban zabe lafiya.

KADUNA: Muna taya Dallatun Zazzau Malam Ramalan Yero murnar samun nasara da yayi. Allah ya baka Nasara a babban zabe Dallatu.

Yasir Ramadan Gwale
09-12-2014

Alhamdulillah Malam Nuhu Ribadu Yaci Zabe


ALHAMDULILLAH MALAM NUHU RIBADU YACI ZABE

Alhamdulillah muna godiya ga Allah madaukakin sarki da ya nuna mana wannan Nasara. Haka kuma muna kara mika godiya ga Daliget na Adamawa hakika kun zabi wanda ya dace. Muna murna da wannan zabe da kuja yiwa Malam Nuhu Ribadu. Alhamdulillah Allah mun gode maka. Allah ka nuna mana babban zabe lafiya kuma muna kara rokonka Ya Allah ka baiwa Malam Nuhu Ribadu nasarar lashe babban zabe mai tafe. Masha Allah.

Muna kuma fatan kara samun Nasara ga Malam Salihu Sagir Takai a nan gaba kadan.

Yasir Ramadan Gwale
09-12-2014

Sunday, December 7, 2014

Jinjina Ga Jami'an Tsaron Najeriya


JINJINA GA JAMI'AN TSARON NAJERIYA

Ba shakka wannan Nasara da jami'an tsaron Najeriya suka samu na kame wannan jirgi cike da kayan yaki da ake kyautata zaton makiya zaman lafiyar Najeriya ne suke taimakawa 'yan ta'adda da miyagun makamai wajen jefa rayuwar al'umma cikin mawuyacin hali, wannan Nasara da jami'an tsaron suka samu na kame wannan jirgi abin a yaba ne tare da karfafa musu guiwa wajen jajircewa akan aikinsu. Muna yabawa da wannan aiki na kokarin tabbatar da zaman lafiya, da kuma kwa-kwulo wadannan miyagu azzalumai 'yan ta'adda wadan da suka dauki zubar da jinin al'umma a matsayin wani aiki na yau da gobe.

Addu'armu bata tsaya kadai akan Allah ya tona asirin irin wadannan miyagu ba, Muna kara yin adduah akan Allah ya yi mana maganin duk wani abu da yafi karfinmu, Allah ka yi mana maganin duk wasu miyagu azzalumai 'yan ta'adda da suka addabemu. Allah ka rusa shirinsu ka wargaza sha'aninsu. Allah ka darkakesu, ka dawo mana da dawwamammen zaman lafiya.

Allah ka taimaki jami'an tsaronmu da suke aiki babu dare babu rana wajen ganin an samu zaman lafiya a garuruwanmu. Haka nan kuma, muna kira ga Gwamnati da ta basu dukkan kulawa wajen ganin sunci lagon 'yan ta'adda. Allah ka taimaki kasarmu Najeriya ka bamu lafiya da zama lafiya.

YASIR RAMADAN GWALE
07-12-2014

Tuesday, December 2, 2014

HATTARA GWAMNATIN KANO: Jihar Kano Bata Karkashin Dokar Ta'baci


HATTARA GWAMNATIN KANO: Jihar Kano Bata Karkashin Dokar Ta'baci

Ranar juma'ar makon da ya gabata 28 ga watan Nuwamba, rana ce da al'umma da yawa a cikin Birnin Kano ba zasu taba mantawa da ita ba. Wannan ita ce ranar da aka kai hari mafi muni a tarihin hare-haren da 'yan ta'adda makiya Allah makiya san zaman lafiya suke kawowa Kano. An kashe dattawa da matasa da yara a lokacin da suke Ibada dan yin munajati tare da ubangijinsu. Ba shakka wannan al'amari muninsa yakai muni. Ina kara yin adduah ga wadan da suka rasa rayukansu a wannan rana, Allah ya jikansu ya gafarta musu ya sa al-jannah ce makomarsu. Masu raunuka kuma Allah ya basu lafiya, ya sa ciwon ya zama kaffara a garesu.

Lokacin da wannan al'amari ya auku, Mai girma Gwamnan jihar Kano wanda shi ne Shugaban Tsaro na jihar Kano (Chief Security) baya Kano yana can kuryar kudancin Najeriya, shima Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Muhammadu Sunusi II shima baya kasar baki daya, haka zalika Kwamashinan 'yan Sanda  na jihar Kano shima baya Kano! Cikin kaddarawar Allah wannan mummunan kaba'ira ya faru.

Faruwar wannan mummanan harin ta'addanci da awa hudu misalin karfe 06:04 Uba Danzainab ya sanar mana a facebook bikin da ake a ofishin mataimakin Gwamna na cike form din takararsa ta zama Gwamna Kano! A irin wannan lokaci da al'umma ta shiga cikin damuwa da rudani, akai wawar asarar rayukan al'umma, masu mulkin da ya kamata ace sunfi kowa nuna  damuwa da rayukan al'ummarsu sama da komai, amma a kyale al'umma a shiga al'amuran siyasa? Yanzu wannan daidai ne?

Haka nan shima Gwamnan Kano Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, duk da cewar baya Kano lokacin da abin ya faru, sai washegari Asabar da safe sannan muka ji cewar Gwamna yaje Masallacin kofar Gidan Sarki da Asibitin Murtala dan jajantawa wadan da abin ya shafa tare da ganin irin girman barnar a Masallacin Gidan Sarki, amma bamu ji cewa ya halarci jana'izar wadan da aka binne a makabartar Dan Dolo a safiyar asabar din ba.

A wannan ranar ne kuma tsohon mataimakin Shugaban Kasa Alhaji Atiku Abubakar ya bada sanarwar soke bikin da wasu abokansa suka shirya masa na murnar samun karin shekara da yayi (BirthDay), ya bada sanarwar cewar ya soke bikin ne domin jimami tare da taya al'ummar Kano alhinin abinda ya faru. Ba shakka ko domin siyasa Atiku yayi hakan ya kyauta, domin ya nuna cewa jinin al'ummah yana da kima da daraja a wajensa.

Haka kuma, wani abin mamaki da ya kuma faruwa a lahadin da ta biyo bayan asabar din, sai muka samu sanarwa a facebook daga Baba Dantiye cewar Gwamna Kano yaje bikin auren wasu Yarabawa a jihar Legas! Yaushe za a ce Gwamna wanda shi ne yafi kamata yafi kowa nuna damuwa akan rayukan al'ummar jihar Kano, amma ace har ya fice ya tafi yawan bukukuwa? Shin hakan na nufin tsohon mataimakin shugaban kasa yafi Gwamnan Kano mutunta rayukan al'ummar Kano?

Shin yanzu idan mun zargi Gwamnatin tarayya akan rashin nuna damuwa da rayukan al'umma, su kuma Shugabanninmu na jihohi mu ce musu me? Tsakanin Gwamnatin tarayya da Gwamnatin Kano wa yafi kamata ya fi nuna damuwa da raukan al'ummar jihar Kano?

Lallai ya kamata mu sani cewar Jihar Kano fa bata karkashin dokar ta baci, dan haka Gwamnan Kano shi ne shugaban tsaro Chief Security na jihar Kano, shi ne wanda yake da ruwa da tsaki akan duk abinda ya shafi tsaro a cikin kano musamman cikin birni. A irin wannan halin da aka samu kai aciki, Gwamna baya gari, Sarki baya gari, Kwamashinan 'yan sanda baya gari, shi kuma Magaimakin Gwamna yana can yana bikin ciken form din tsayawa takara. To dan Allah waye ya damu da rayuwar al'ummar da ake shugabanta?

Ina mai amfani da wannan damar wajen yin kira ga Gwamnatin Kano da Mai Girma Gwamnan Kano Engr Dr. Rabiu Musa Kwankwaso da Mataimakin Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje, akan su fito su nemi afuwar al'ummar Kano akan wannan rashin ko in kula da aka yi a daidai lokacin da Kano ta fada cikin bala'i. Rashin yin hakan shi ne zai tabbatar mana da cewar masu mulkin ba gaskiya suke ba akan kula da rayuwar al'umma, sunfi damuwa da sha'anin mulkinsu da siyasarsu sama da rayuwar al'ummar da suke shugabanta.

Ina sake amfani da wannan damar wajen kara yiwa al'umma ta'aziyar wannan ibtila'i da ya samemu Allah ya jikan wadan da suka rasu a sanadiyar wannan hari. Marasa lafiyan cikinsu Allah ya basu lafiya ya sa hakan ya zama kaffara a garesu. Masu kai wadannan hare-hare Allah ka sansu kana ganin Allah kai musu abinda yafi dacewa da su. Allah ka amintar da mu a garuruwanmu.

Yasir Ramadan Gwale
02-12-2012

Monday, December 1, 2014

MAganar Gaskiya Dangane Da Kahse-Kashen 'Yan Boko Haram


MAGANAR GASKIYA

Rabin gaskiya ba gaskiya bane. Ba zaiyuwu ba ace akwai magana rabi gaskiya rabi karya. Kodai ta zama gaskiya zalla ko karya zalla. Dole mu tunawa kanmu tarihi dan fuskantar gaskiyar al'amari.

Wadan da suka kashe sahabin Manzon Allah kuma surikinsa, Usman Ibn Affan Alaihis-Salam, Musulmi ne masu fatan samun shiga al-jannah, sun kashe shi yana karanta al-Qurani zancen Allah. Haka zalika, wadan da suka kashe Malam Jaafar Adam Rahimahullah ranar juma'ah yana limancin Sallar Asuba, Sallar da munafukai basa halatta inji Manzon Allah. Nayi imani wadan da suka kashe Malam Jaafar musulmi ne ba arna ba.

Dan haka babu wani dalili da wani zai fito yace mana WAI MUSULMI BA ZASU IYA KASHE MUSULMI A MASALLACI BA wannan ba gaskiya bane. Ya faru a baya kuma yana cigaba da faruwa a yanzu. 

Wadan da suke wannan kisan da ake kira Boko Haram dole mu yarda cewa su Musulmi ne, amma kasancewarsu Musulmi ba shi ke nuna halaccin abinda suka aikatawa ba, kuma aikinsu ba shi ke nuna haka duk Musulmi suke ba. Akwai Musulmin kirki na gari masu tsoron Allah; kuma akwai Musulmin banza gurbatattu marasa tsoran Allah.

Ba yadda zaka kore Musulmi daga Musulunci duk munin aikinsa indai ba shi ya kore kansa daga Musulunci ba. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yayi alqunutu yana kama sunan wasu Allah ya haneshi, ya gaya masa Subhanahu Wata'ala cewa shiriya a hannunsa take buwayi gagara misali.

Bambancin addini ko bambancin siyasa ba shi zai halatta mana kiyayya da gaba ba. Na gamsu cewa Shugaban kasa baya yin abinda ya kamata ace yayi a harkokin tsaro. Amma kai tsaye a ce shi ne ke kashe mutane wannan ba gaskiya bane.

Dole mu gayawa kanmu gaskiya. Shin tsakani da Allah akwai wani Musulmi ko dan Boko Haram ko ba shi ba da zai yarda ya daura Bom a jikinsa Bom ya tashi da shi dan bukatar Goodluck Jonathan ta biya? Shin arna irin na Najeriya zasu saka Bom a jikinsu su mutu dan bukatar Jonathan ta biya? Akwai wani mai hankali daga cikin Musulmi ko kirista da za ayi yarjejeniya da shi dan shi din ya mutu?

Ya kamata mu fadi gaskiya kuma mu yi adalci a maganganunmu. Idan har zamu dinga baiwa Boko Haram uzuri muna cewa basu bane wasu ne daban. To wallahi wannan abin ba zai taba yin sauki ba sai dai ya karu. Mun shagaltar da kawukanmu da zargin juna su kuma zasu mamaye garuruwanmu. Wanda ya sani ya sani wanda bai sani ba ya sani.

Indai ana san kawo karshen wannan kashe kashe dole abi hanyoyi na gaskiya dan magance matsalar. Amma ba zai yuwu ba a dinga siyasa da rayuwar al'umma. Ko mun yarda ko bamu yarda ba Khawarijawa sun sanyamu yakin da bamu shirya ba. Sarakuna ya kamata suyi abinda ya dace cikin hikima.

Adduah kadai ba zata magance mana wannan halin da muke ciki ba. A cikinmu babu Annabi Musa ko Abu Huraira. Manzon Allah SAW ba adduah kadai yayi ya kwanta Mala'iku sukai masa Badar ba.
Kayi tir ko kai Allah wadai wannan ba zai taba sauya gaskiya ba. Tana nan a matsayinta na gaskiya, haka nan ba zai taba sanya karya ta zama gaskiya ba.

Lallai jagororinmu subi hanyoyin da suka kamata wajen kare salwantar rayukan al'ummah da suke mutuwa ba gaira ba dalili. Allah ka nuna mana gaskiya mu fahimci gaskiya ce ka bamu ikon binta ka nuna mana karya mu fahimci karya ce ka bamu ikon kauce mata.

Yasir Ramadan Gwale
30-11-2014