Friday, February 17, 2017

 
ALLAHU AKBAR: ALLAH YA JIKAN MALAM JA'AFAR ADAM!!!
 
Malaminmu Sheikh Jaafar Ibn Mahmud Ibn Adam (RH), shi ne mutum na farko daya fara fitowa k’arara yayi fito na fito da masu Da’awar cewa Boko Haramun ne, ashe bamu sani ba Malam ya fanshemu akan wannan jihadi da yayi na yakar wannan tunani. Watakila badan wancan yaki da Sheikh Jaafar yayi ba, da yanzu Ahlussunnah suna shan wahala wajen fayyace gaskiyar Magana cewa Ahlussunnah mun barranta daga wad’ancan 6atattu masu da’awar ce...wa karatun Boko da aikin Gwamnati Haramun ne.
 
Sai gashi duk wanda zai soki mabiya sunnah ko yayi mana gugar zana, ko ma kai tsaye ya alakanta mu da wad’ancan mutane, an yanke masa hanzari tuntuni. Domin duk girma da tarin Ilimin Falsafar mai falsafa, to Malaminmu Sheikh Jaafar Ibn Adam shi ne ya fara fitowa fili 6alo 6alo ya yaki cewa karatun Boko Haramun ne.
 
Saura da me? Mutum ne ya kasa kada kai da hujja, ya kasa zuwa da wujja wadda zata share abinda ka zo masa dashi na ilimi, dan haka ba shida wani abin yi, sai dai yace maka, ai tsanani ko kaifin kishin addini shi yake 6u66ugar da ‘yan ta’adda, har suna ikirarin ai masu irin wannan fikira sun samo ta ne daga Litattafan Ibn Taymiyya.
 
Mu kuma muka ce musu, zakewa a cikin ilimin Falsafa shi ne yake sabbaba barin Allah gaba daya. A garin nan Kano ba wani gari ba, akwai mutanan da muka sani sun daina Sallah sun daina Azumi sabida zakewarsu cikin mummunan tunani irin na Falsafa. Ko ba haka bane? Kuma abinda basu sani ba, munce ne duk inda Wahayi ya sauka babu batun yin aiki da hankali ko tunani.
 
Yasir Ramadan Gwale
17-02-2017