Saturday, December 31, 2011

Mallam Ahamadu Maigandu shi ne Gwarzona na shekarar 2011!

Assalamu Alaikum warah matullahi ta'ala wa barakatuhu.

Ya 'yan uwa ina gaisheku gai suwa irin ta addinin musulunci. kuma ina fatan alheri gareku baki daya. sanin kowannenmu ne cewa shekarar Musulunci tuni ta riga ta gabata, sannan kuma yau ne muke ban kwanan da wannan shekara ta miladiyya ta 2011. Kamar yadda muka sani gab da karewar wannan shekara wani muhimmin al'amari ya faru wanda dukkan 'yan uwa suka yi farin ciki da murna da faruwarsa, wato hadin kai da aka samu tsakanin bangarorin izala guda biyu Jos/kaduna.

Shakka babu wannan al'amari muhimmin abu ne. wannan hadin kai dai ya faru ne sakamakon rasuwar dan uwa kuma daya daga cikin jigo na kungiyar Izala reshen jihar kaduna. Jama'a da dama sun nuna alhinin wannan bawan Allah irin yadda aka ringa fadar kyawawan kalamai a gare shi ya nuna irin yadda ya zauna da jama'a lafiya. jama'a daga sassa da dama sunta tudada zuwa jiharsa ta Bauchi domin yin ta'aziya ga iyalansa da 'yan uwansa da abokan arziki. Da kuma nuna alhinin rashinsa.

Lokacin da Sheikh Sani Yahaya Jingir shugaban bangere na Jos ya nemi wannan hadin kai lokacin da ya kai ziyarar ta'aziyar Maigandu. shakka babu akwai jama'a da dama da suka kai ruwa rana domin samar da wannan hadin kai amma Allah bai sa hakarsu ta cimma ruwa ba, ina jin jina ga babban malaminmu sheikh Dr. Ahmad Gumi ganin irin shi ma yadda ya yi ta kokari a baya wajen ganin wannan hadin kai ya samu. Allah baisa wannan muhimmin al'amari zai samu ta bangarensa ba.

Shakka babu, wannan rasuwa ta wannan bawan Allah ba karamin alkhairi ta haifarwa dimbin musulmi ba. kowa dai yasan da cewa dole hankali ya tashi zuciya ta raurawa idanu su zubar da kwalla a ya yin da akayi rashi musamman na mutumin da yake hidima wa jama'a. Amma Allah cikin ikonsa ya sanya rasuwar wannan bawan Allah itace silar bude wani sabon babi na hadin kan al'ummar Musulmi a wannan kasa tamu. Tabbas iyalan Malam Maigandu da makusantansa sunji takaicin rabuwa da shi a lokacin da Allah ya rubuta rayuwarsa zata koma zuwa gareshii. kamar yadda Allah ya fada a cikin alkur'ani kowane mai RAI zai dandani mutuwa, mai gandu dai ya riga ya dandani tasa kamar yadda kowannemu zai dandana kamar yadda Allah ya yi alkawari. Amma kuma ta gefe guda kuma masu hankali sai suyi murna ganin cewa ta sanadiyarsa ne Allah ya samar da wannan babban muhimmin al'amari na hadin kan Musulmi Ahlussunnah a wannan kasa tamu.

Muna fatar wannan hadin kai da akasamu ya dore har iya tsawon rayuwarmu. kuma kamar yadda aka cimma matsaya kan Alkur'ani da sunnah shakka babu wannan shi ne zai hada kan al'ummar Musulmi baki daya, Allah ya cigaba da hada kanmu wajen yi masa da'a da biyayya da hani ga mummuna da kuma umarni da kyakkyawa.

Daga karshe ina addu'ar Allah ya jikan Mallam Ahamadu Maigandu ya gafarta masa yasa al'janna ce makomarsa. kuma 'yan uwansa da iyalansa Allah ya basu ladan hakuri ya cika a mizaninsu. kuma shima babban malaminmu kuma sabon shugaban wannan hadaddiyar kungiya Sheikh Sani Yahaya Jingir Allah ya saka masa da alheri kuma Allah ya yi masa jagoranci bisa wannan Nauyi da aka dora masa. Allah ya sadamu da alherinsa baki daya.

Mallam Maigandu wallahi kaine gwanina na wannan shekarar, Allah ya albarkaci zurriyarka ya kyautata bayanka.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@yahoo.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com


Saturday, December 17, 2011

Yadda Za A Magance Al’amuran Tsaro A Najeriya

Hakkin kowace gwamnati ne ta kare tsaron rayuka da lafiya da kuma dukiyar al’ummarta. Gwamnati itace ke da alhakin kulawa da dukkan al’amuran mutanan da suke karkashinta baki ne ko ‘yan kasa. kula da dukkan dangogin tsaro yana kan hukuma tuna daga tsaron kan iyaka, kula da shige da fice ta sama da ta ruwa. Tunda dukkan masu kayan sarki ko aikin damara suna karkashin hukumane kuma da dukiyar al’ummar kasa ake biyansu albashi. Kamar kuma yadda muka sani shugaban kasa shi ne shugaban kwanmandan askarawan kasarnan baki daya dukkan wani abu da yake da alaka da tsaro shugaban kasa shine mutum na farko akan wannan al’amari.

Sanin kowane dan Najeriya ne cewa sha’anin tsaro ya tabarbare a wannan lokaci da ake fuskantar matsin rayuwa. Al’amura na kara dagulewa a yayin da aikin yi ya yi karanci, jami’o’I da kwalejoji kuma suna ta kara kyankyasar sabbin masu kammala karatu, haka kuma jama’a na ta kara aure da haihuwa, al’umma na karuwa ita kuma gwamnati na ta kara fadada tunani wajen Karin samun hanyar kudin shiga. A daidai wannan lokaci ne kuma al’ummar kasa suka shiga cikin wani hali na zullumi da fargabar abubuwan da ka iya zuwa su zo wadan da suka shafi sha’anin tsaron rayuka da dukiyoyi.

Sanin kowa ne a ‘yan shekarun da basu wuce 15 ba ansamu hasarar rayuka da dukikoyi masu dimbin yawa ko dai ta hanyar fashi da makami ko rikicin kabilanci ko rikin addini ko sanadiyar tashin bam ko hadurra akan manya da kana nan hanyoyinmu koma ta wasu hanyoyin da ba wadannan ba wanda Allah ne ka dai yasan adadinsu a wannan kasa tamu mai al’umma kusan miliyan 167 da kuma kabilu daban da ban, bayaga tashe-tashen hankula da rigingimun kabilanci dana addini da suka sha faruwa kuma suke faruwa a daidai lokacin da kasar ta samu dimbin dukiyar da ba’a taba samuba tunda aka samu Najeriya a shekarar 1914, lokacin da aka hade kudu da Arewa a matsayin kasa daya al’umma daya.


Sannan ga kuma wata sabuwa da ke faruwa kamar yadda mukaji a makon da ya gabata cewa wasu kafofin yada labaran kasar nan suka ruwaito labarin yadda wasu tsagerun ‘yan kungiyar OPC masu rajin kare muradun yarbawa suka yi barazanar yaki da kungiyar boko haram a birnin Ikko. Hakanan a makon da ya gabatar ne muka ji yan tsagerun yankin Neja Delta suka yi tattaki da niyar yin zanga zanga a babban birnin tarayya Abuja, duk da jami’an tsaro sun yi nasarar dates su a garin Lokoja, hedikwatar jihar Kogi. Suma yan kungiyar MOSSOB, masu fafutukar ganin kasar Biafra sun kara nanata kudurin su na ganin ko dai dan kabilar Ibo a bashi dama a shekara ta 2015 domin ya hau kujerar shugabancin kasar nan ko kuwa a basu dama su kafa kasar su domin su cika burin jagoran su, Ojukwu da ya kwanta dama a yan kwanakin baya.

Duk dan Najeriya yasan da cewa kullum ana kara samun yawan aukuwar al’amura da suke nuna cewa tsaro yayi karanci a kasar nan. Kama daga abin da ya shafi fashi da makami da fyade da tashin bamabamai da karuwar hadurra akan manya da kana nan hanyoyi, dama rikicin kabilanci da na addini da ya ki ci yaki cinyewa. Duk wannan ‘yan Najeriya na sane dasu, kuma ana ta dogon turanci akan yadda ya kamata wadan da al’amarin yashafa su fuskance shi. Idan ana so ayi maganin tabarbarewar tsaro a Najeriya to kuwa kamata ya yi gwamnati ta dauki mataki kamar haka.

Abu na farko, dole ne duk inda aka samu labarin fashi da makami ko fyade ko daba ko kalare ko tashin Bam ko fadan kabilanci ko na addini, garkuwa da mutane, fasa bututun mai, da ta’addacin tsagerun Neja Delta, OPC, MASSOB, Boko Haram. Tilas ne gwamnati ta kame wandan nan mutane kamar haka, na farko Mai unguwa da kansila da dagaci da shugaban karamar hukuma da DPO na ‘yansanda da darakta ‘yansada na farin kaya na wannan karamar hukuma ko kuma yankin da abin ya faru. Akan cewa tilar su bada bayanin ya akayi abin da ya faru wanda yake da alaka da tsaro ya auku, saboda duk al’amarin tsaron wannan yanki yana karkashin kulawarsu ne, saboda sune wakilan hukuma ta wannan bangare a kuma wannan yanki. Domin a matakin farko wadan nan sune wa ‘yanda suke da hakkin kula da shiga da fitar mutane na yankin da suke ciki, wajibi ne gwamnati ta tuhumesu akan cewa kodai sunyi sakaci wani mugun mutun ko wasu miyagun mutane azzalumai sunzo da nufin cutar da al’umma, ko kuma dama da hadin bakinsu aka aikata dukkan ta’asar da ta afku. Tunda sune suke shugabantar al’umma a wannan yanki duk abin da ya faru su ake tunkara.

Abu na biyu, wajibi ne gwamnati ta gudanar da binciken na gaggawa kuma bisa gaskiya da adalci akan dukkan rahotannin da suka shafi tsaro. Dole ne kuma a hukunta dukkan wanda aka kama da laifi komai girman mukaminsa akuma bayyanawa jama’a suji. Sannan hukuma ta gargadi jami’anta akan sakaci da aiki da kuma hukuncin duk wanda aka samu yayi sakaci da aikinsa har aka samu Baraka ta gefensa.

Abu na gaba kuma, dole ne gwamnati ta samarwa jami’anta ina nufin na tsaro cikakkun harkokin jindadi da walwalarsu da ta iyalansu. Tundaga kyakkyawan albashi da kuma kayan aiki wadan da sukayi dai dai da zamani, wanda wannan shi ne zaiyi maganin cin hanci da rashawa akan harkar tsaro.

Idan har gwamnati ta gwada daukar wadannan matakai al’amura basu kyautata ba to tabbas kamar yadda masu Magana suke cewa da akwai lauje cikin nadi, akwai wadan da sukewa gwamnati zagon kasa ta fuskar tsaro, akwai baragurbi kuma dole gwamnati ta binkitosu tare da hukunta su ko su wane kuma komai girman mukaminsu.

Domin munyi imani dukkan wasu makamai ko na harbi ko masu fashewa da suke yawo acikin kasa gwamnati tana da masaniyar daga inda suka fito. Domin makami ba kamar abinci bane da ake shukawa a gona haka kuma ba kamar kaya bane da kowane dan kasuwa zai iya sana’antawa a masana’antarsa, tabbas duk inda kaga makami yana da alaka da hukuma ko ta kusa ko ta nesa domin yarjejeniyar mallakar makamai da kasashen duniya suka cimma ta Kyoto Da kuma ta Geneva ta tabbatar da haka. Ashe kaga kenan babu yadda za’ace hukuma batada masaniyar yadda makamai suke yawo acikin kasa ko a hannun jami’anta ko a hannun daidaikun mutane.

Idan kuwa aka bi dukkan wadan nan matakai al’amura basu kyautata ba to tabbas gwamnatin da kanta itace kanwa uwar gami, kawai ana yaudarar al’ummar kasa ne akan sukurkucewar tsaro amma da saninta akayi wasarari da harkokin tsaro don baiwa wasu dama suci karensu babu babbaka alabasshi daga baya a cimma wata boyayyar manufa. Dadin dadawa munsan cewa al’amuran da suka shafi tsaro a kowace kasa suna da bukatar sirri to wajibin hukuma ne ta san irin dabarun da za’abi wajen kyautata al’amura da suka shafi sha’anin tsaro kuma suke da bukatar sirri wanda munsan gwamnati tana nata kokarin. Munsan akwai dokar da gwamnati ta sanyawa hannu kwanakin baya ta ‘yancin neman bayanai wato Freedom of information Bill, munsan da cewa duk inda mutum ya kaiga neman labarai bazai binciki ya ake gwamnati take da makamai ba kuma nawa aka siya nawa aka batar.

Mun san da cewa duk wani makami da yake a Najeriya idan ba na gwamnati bane wanda ita keda al’hakin mallakarsa da kuma kulawa da shi, kuma babu ta yadda za’a yi ya fita batare da masaniyar wadan da abin ya shafa ba. To kuwan babu ta yadda zamu yarda cewa makamin nan ba shigo da shi akayi kodai takan iyaka ko kuma ta gabar teku ko ta amfani da jirgin sama wanda duk wadan nan gurare al’hakin gwamnati ne ta kula da su, idan kuwa tayi sakaci da wannan bangare to tabbas wannan ko wace irin gwamnati ce bata cancanci acigaba da bata goyon baya ba tunda bata iya tsarewa al’umma kasaba ta fuskar tsaro. Haka kuma babu wani mutum da zai iya kera makami ba tare da gwamnati tana da masaniya ba domin dukkan wani abu da ya shafi tsaro babu wanda yake da karfin iko akansa sama da hukuma.

Kamar yadda mukajicewa hukumomi na kokarin sanya na’urar binciken a kofar shiga majalisa mai gani har hanji wadda ake kira Fulbody scanner don kare ‘yan majalisa. To suma al’ummar kasa suna bukatar wannan na’ura don kare rayuwarsu da dukiyarsu, domin ‘yan majalisa ba su kadai bane ‘yan Najeriya ba muma talakawa muna da hakkin gwamnati ta kula damu ta dukkan bangarori ba sai ta fuskar tsaro ba kawai. Kuma bisa yadda mukaji shugaban kasa ya gabatar acikin kasafin kubin shekarar nan mai kamawa anware kudi kusan Naira Biliyan N921.91 a sha’anin tsaro muna fatar al’amura su kyautata wanda a cikin wannan halin ne abun takaici zaka iske ba wanda suka fi cutuwa da rashin tsaro da mummunan talauci da rashin aikuin yi da rashin hadin kai da shugabanci irin alummar Arewacin Najeriya.

Lallai muna kira ga gwamnati ta yi iyakar iyawarta wajen kawo karshen tashin bamabami da kuma rikicin kabilanci dana addini da yaki ci yaki cinyewa a birnin Jos da sauran sassan jihar filato da garkuwa da mutane da fyade da satar jarirai a asibitoci da satar mutane akan hanya da rikicin manoma da makiyaya da wadan nan makudan kudaden da aka fitar wajen sha’anin tsaro.

Idan ba haka ba kuwa abinda Bahaushe yake cewa abinda yaci doma bazai bar awe ba. Wanda wannan yake nuna irin juyin juya halin da yake faruwa yanzu haka a yankin tsibirin larabawa da Arewacin Afrika babu abin da zai hanashi wanzuwa a Najeriya, kamar yadda mukaji kwamitin da shugaban kasa ya kafa akan rikicin bayan zabe karkashin jagorancin dattijo Sheikh Ahmad lemu sunyi gargadi akan wannan batu. Lallai hukumomi su sani duk wadan can abin da suke faruwa a yankin kasashen larabawa rashin Adalci ya janyoshi, don haka adalci shi ne zai zaunar da kasarnan lafiya, kuma shi ne zai cigaba da zaunar da kasar nan a matsayin kasa daya al’umma daya. Muna tabbatarwa da gwamnati kamar yadda suka sani yanzu duniya tana tafiya ne bai daya. Allah ya taimaki kasarmu Najeriya ya bamu lafiya da zama lafiya.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@hotmail.com

http://yasirramadangwale.blpgspot.com

Saturday, December 10, 2011

Makarantun kwana: Annobar Madigo da Luwadi daga ina?

Ya ‘yan uwa barkanmu da sake saduwa, da kuma fatan za a gafarceni akan wannan maudu’I maras dadinji. Ya dan uwa mai karatu lokaci ne ya yi na mu fito mu fadi gaskiyar yadda al’amura suke, ina fatar za a yimin kyakkyawar fahimta, kuma za’a gafarceni bias furta wadan nan kalamai masu matukar nauyi . Zance na gaskiya makarntun kwanan kamar yadda muka sansu a lokacin baya yanzu abin ba haka yake ba.

Makarantar kwana, itace makaranta wadda tafi hada zumunci so sai tsakanin dalibai. Kuma idan banyi karya ba zumuncin ‘yan makarantar kwana bai cika baci ba ko lalacewa komai tsawon lokaci bayan kamala makaranta. Kusan idan ka dauki rayuwarmu gabaki daya zumuntace tun ta makarntar sakandare, mafi yawan dalibai basa wasa da wannan zamatakewa da sukayi a makarantun sakandare, musammanma idan akace makarantar kwana ce. Wannan ce ma ta sanya kake jin kungiyoyin tsaffin dalibai na aji kaza a makaranta kaza. Wanda da wuya kaji na daliban makarantu jami’a ko gaba da sakandare ba.

Kusan daliban makarantar kwana sukan ce duk wanda baiyi makarantar kwana ba to da sauransa a harkar karatun Boko. Domin rayuwar makarantar kwana wata irin rayuwa ce da take da tasirin gaske ainun, hakika duk irin yadda za a baka labarin makarantar kwana ba kamar kaje bane. Domin yara galibi wadan da suke gab da lokacin balaga kan samu kansu cikin wata irin rayuwa wadda babu uwa babu uba, sai dai kawai abokai da yayyi da kanne na makaranta. Annan ne akan kulla abota ta hakika kuma mai dorewa domin kuna tare ku kwana ku tashi ku ci-abinci koda yashe tare. Wannan irin rayuwa ba karamin dadi gareta ba.

Da can idan muna hira da yayyinmu mata ko maza idan suna bamu labarin makarantar kwana sai muji wata irin duniya ce mai dadi kamar kayi tsutsu kaje ka risketa, haka kuma idan ana baka labarin “seniority” sai kaji an zare maka sha’awar makarantar kwana, domin ana bada wanki da debo ruwa da wanke-wanke da tsallen kwado da kama kunne da sauransu wannan kan sa yara su tsoraci makarntar kwana.

Hakika lokacin da nayi makarantar kwana na tabbatar da dukka abubuwan da ake ta fadamin a baya lokaci mai tsawo. Na tuna wata rana da shugaban makaranta wato principal ya tara dalibai “juniors” da “seniors” wato manya da kanana inda yace “abin da nake so daku manyan dalibai hukumar makaranta bata hana ku baiwa kannenku wanki ba, amma abinda muke so daku idan kun bada wanki ku bada sabulu” munsha wahalar wanki da debo ruwa a wannan lokacin domin bama iya samun ruwa daga cikin makarantar Unity Karaye sai munje wani kauye da ake kira kusalla ko kuma munzo cikin garin karaye Torankawa ko kuma kofar zango sannan mu samu ruwa; galibi wannan yafi faruwa a zangon karatu na biyu da na uku lokacin da dukkan rijiyoyin makaranta sun kafe ga kuma rani yayi nisa damina bata soma ba.

A irin wannan rayuwa ta makarantar kwana babu lokacin da dalibi ya fi kauna kamar lokacin darussa da kuma lokacin barci domin sune lokutan da babu wanda zai kiraka ballantana ya aike ka. Zaka samu yara wadan da suke ‘yan ajin farko jss 1 zuwa jss 3 basa iya zama cikin dakunan kwananansu domin gudun duka ko kuma aike, dan ajin ss 1 shine wanda ya fara jiyo kanshin ‘yanci sau da yawa zaka samu sukan zauna acikin dakunansu. Laifi kankani dalibi zaiyi ayi masa hukunci kama daga tsallen kwado zuwa kama kunne ko hawan bango da sauransu, munsha tsallen kwado kamar sojoji.

Gaskiya idan zan iya fada makarantar kwana na daya daga cikin makarantun da suke gyara yara a wancan lokaci, domin ananne za’a koya maka gaida “senior” duk safiya haka kuma dole idan ya taho kaima ka taho ka dakata har sai yashige dalibai juniors sukanyi ladabi irin wanda basa yiwa iyayansu ko yayyensu, idan akayi sa’a wani daga haka shi ke nan ya mike da wannan tarbiyya.

Zance na gaskiya makarantun kwana na yanzu abin ba haka yake ba. Idan zan iya tunawa babbar matsalar da akafi fuskantar a lokutan baya bata wuce dalibai masu shan taba sigari ba da kuma dai sauran abubuwa na kuruci dangin hauka da ba a rasa ba a tsakanin dalibai.

A irin yadda nake samun labari yanzu shine duk abin da na sani da akeyi a baya na seniority yanzu ya zama tarihi domin yanzu gwamnatoci kan yi kokarin katange makarantun maza ba kamar da ba kawai da za a yanki daji ba, yanzu bayan katange makarantu akan samarmusu da famfunan tuka-tuka wanda wannan shi ya rage musu babbar matsalar ruwa. Sai kuma wata babbar annaoba da ta kutso kai gadan gadan cikin makarantun kwana kuma take ci kamar wutar daji itace dabi’arnan ta Luwadi ko kuma Madigo a makarantun mata.

A wani rahoton da na karanta yana cewa kusan kaso 12 na daliban Najeriya dake makarantun kwana suna aikata wannan danyan aiki na madigo da luwadi wanda kalmomin basu da dadin fada a baki ina fatar za’a gafarceni. Haka kuma wannan rahoton yace kusan kaso 15 na daliban jami’a suma sukan aikata wannan mummunan aiki na zakkewa juna da nufin biyan bukatar sha’awa. Banida cikakkiyar masaniyar wannan rahoton gaskyane ko kuwa akasin haka.

Kwanakin baya wata yarinya da bansanta ba ta rubutomin wasika daga wata makarantar kwana dake cikin birnin kano tana gayamin don Allah na fadakar akan wannan matsala da take faruwa a makarantun mata, ta fadamin a cikin wasikar cewa Wallahi lokacin da aka kaita hankalinta ya yi matukar tashi domin tace Wallahi rububinta aka ringa yi kamar ‘yartsana, tace ana yaudarar yara da kayan kyale-kyale da kuma nuna masu soyayya, tace idanma kika ki akan yi miki ta karfin tsaya ta hanyar rikeki da toshe miki baki, wannan yarinya ta sahidamin cewa tayi karyar rashin lafiya kawai don ta koma gida ta sanar da mahaifinta abin da ke faruwa, tace amma da tazo gida ta sanar da mahaifinta gaskiyar lamari sai ya karyata ta tare da cewa batason makarantarne shi yasa ta fake da wannan abu.

Tabbas wannan abu ba karya bane. Domin da zakayi hira da daliban makarantun kwana ka tambayesu gaskiyar wannan al’amari zasu sanar da kai cewa lallai wannan abin yana kara samun tagomashi a tsakanin dalibai. Domin binciken da na gudanar ya tabbatarmin da haka. Dalilan da kansa haka yaduwa cikin sauri sune kamar haka.

Abu na farko, kuruciya da kuma karfin balaga domin galibi akan kai yara makarantar kwana adaidai lokacin da suke kan ganiyar balaga ko kuma suke gab da balaga. Kamar yadda masana suka ce mafi yawanci mazakuta takan cika girmanta ne a shekaru 18 zuwa 22 wannan takan sanya galibi sha’awar yara takan motsacikin sauri. Haka kuma abu na gaba shine yanzu zamani yazo inda yawancin yara kan tafi da wayoyin hannu a boye masu dauke da fina-finan batsa masu yawan gaske, me kake jin zai faru alokacin da yara suke kan ganiyarsu ta balaga kuma ga fina-finan batsa a tsakaninsu?

Abu na gaba shine harkar wasan kwallan kafa, itama wata muhimmiyar hanyace da kanjefa mafiyawanci yara fadawa cikin wannan mummunar ta’ada domin ta haka ake yaudarar wasu da daman gaske, sannan itama kwallon kasashen turai ta Champions league da laliga da sirie A da sauransu sun taka muhimmiyar rawa wajen jefa da yawa daga cikin yaranmu cikin wannan yanayi. Domin akan kulla mummunan kawance tsakanin wannan yaro da wancan yaro. Wato abin yakai yanzu hattana irin mukaman da akan nada yara wato prefect sai annemi yaro ya bada kansa sannan akai sunansa domin tantancewa kuma wannan ana hada baki da wasu daga cikin miyagun malamai marasa kishi da tsoron Allah.

Haka suma makarantun ‘yammata suna da nasu hanyoyi na yaudarar kamar sayan kayan kwalliya irin na zamani da suturu masu dankaren tsada da sarka da yari da sauran abubuwan da ka iya jan hankalin yara mata cikin sauri.

Wannan babban kalubale ne ga iyaye. Lallai wajibin kowane uba ne ya tabbata ya kula da tarbiyyar ‘ya ‘yansa, musamman suturarsu da inda suke zuwa da kuma abokanan mu’amalarsu. Kusan yanzu yana daga cikin abinda iyaye basu cika dubawa ba shi ne abokanan mu’amalar ‘ya ‘yansu, domin zaka ga basu cika basu muhimmanci ba, wanda galibin mu Hausawa mukan dora laifin lalacewar ‘ya ‘yanmu akan abokai kowa ka tambayeshi zaice abokai suka lalata masa yaro haka idan da zaka tambayi uban lalatacce zai gayamaka cewa lalatattun yara suka bata masa yaro, amma duk da haka iyaye basa daukar wani mataki akan wannan batu.

Sannan, yana daga cikin hakkin hukuma ta tsarewa al’umma tarbiyya da kuma mutunci, hukuma itace zatayi tsari dangane da wannan abu da yake cigaba da yaduwa cikin sauri, haka kuma ma’aikatar ilimi da malaman makarantu yana da kyau su sanya ido sosai akan dalibai domin amana ce aka basu kuma su kanda sani sai Allah ya tambayi kowa dan gane da amanar da aka bashi tundaga iyaye har zuwa malami, kuma dole ne su duba hanyoyin da za’abi wajen ganin anshawo kan wannan matsalar tare kuma da hukunta duk wanda aka kama da aikata wannan laifi a bainar jama’a, wanda wannan inaganin itace kadai hanyar da zata iya kawo raguwar wannan aika-aika, zai zama darasi ko izna ga duk wanda yake aikatawa yaga yadda aka hukunta mai yi a bainar jama’a koda kuwa bulalace. Domin babu wanda zai so yaji cewa dansa ko ‘yarsa suna aikata wannan danyan aiki. Allah ya shiryi al’ummarmu.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@hotmail.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

Sunday, December 4, 2011

Me ya sa matasan Arewa ke gudun kana nan sana’o’i?


Rashin aikin yi a tsakanin matasa na daga cikin matsalar da take addabar kasashen duniya a yanzu. da yawan kasashen suna ta neman hanyoyi da za a kawo karshe ko kuma rage adadin marasa aikin yi, rashin aikin yi babbar barazana ce ga zama lafiyar kowace kasa, haka kuma barazanace ga tsaron lafiya da dukiya. Kusan kididdiga ta nuna mafiya yawan wadan da ke cikin wannan mummunan yanayi na rashin aikin yi matasane wadan shekarunsu suka kama daga 18 zuwa 30 a mafiya yawan kasashen duniya.

Najeriya kasace da Allah ya huwace mata al’barkatun jama’a wadan da galibinsu matasane maza da mata. Kusan kididdiga ta baya-bayan nan ta nuna cewa akwai kusan mutane miliyan 167 a Najeriya wanda wannan adadi ke karuwa cikin sauri a cewar masana, acikin wannan lissafi kusan sama da kashi 65% matasane ‘yan bana bakwai masu jinni ajika. Kuma mafiya yawan al’ummar Najeriya suna yankin Arewa ne.

Babbar matsalar Najeriya yanzu bata wuce rashin aikin yi tsakanin matasa ba kamar sauran takwararorinta kasashen duniya. Dalilan da suka samar da rashin aikin yi tsakanin matasa a Najeriya abayyane suke. Rashin ingantacciyar wutar lantarki kusan itace babbar matsalar da ta haifar da rashin masana’antu wanda hakan ya haifar da rashin aikin yi, domin da wutar lantarki ne galibin kamfanoni ke aiki wanda suke taka muhimmiyar rawa wajen rage adadin marasa aikin yi akusan galibin kasashen duniya. Yau a Najeriyya babu masana’antu a yankin Arewa da zasu iya rage adadin matasanmu kama daga wadan da suka kamala jami’a da kuma wadan da suka fito daga kwalejoji dama wadan da basu sami damar zuwa makaranta ba.

Kididdiga ta nuna cewa gwamnatin PDP karkashin shugabancin tsohon shugaban kasa Olushegun Obasanjo ta kashe kudi sama da dalar amurka Biliyan 16 kimamin Naira tiriliyan 1.3 akan wutar lantarki acikin shekaru 8, amma babu ita babu dalilinta kuma kudin shiru kamar an shuka dusa. Abin tambaya anan shi ne shin ina wutar ta ke? Kuma idan ba’ayi aikin ba kamar yadda muka gani ina kudin suke? Akwanakin baya ‘yan majalisa sunyi dambarwa akan wannan batu amma yanzu shiru kake ji,abun da yake nuna anci bulus kenan.

Idan muka dauki misali da kasar Brazil ta kashe kudi kimanin dalar Amurka biliyan 5 wajen samar da wutar lantarki mai karfin megawatt 120,000 acikin shekara 3 kacal, haka itama kasar Afurka ta kudu sun kashe kudi kimanin dalar amurka biliyan 1 wajen samar da megawatt 5,000 acikin shekara daya kacal. Idan ka dawo nan gida Najeriya zaka ga cewa kudin da aka fitar ya ninka na Afurka ta kudu ninkim baninkim amma megawatt nawa aka samar mana? Lokacin da marigayi tsohon shugaban kasa Mallam Umaru YarAdua yazo ya kudiri aniyar ganin bayan matsalar wutar lantarki a Najeriya wanda ya durfafi aikin fafur wajen ganin ya cimma kudurinsa na samar da megawatt 10,000, Allah bai cika masa burinsa ba ya kwanta dama. Wannan shugaban da ya gajeshi cewa yay i zai dora daga inda ‘yar Adua ya tsaya inda ya nada kansa munistan makamashi da wutar lantarki amma babu wasu alamu da suke nuna da gaske ake akan wannan batu.

Idan kuma muka komo yankin Arewa a yanzu haka wutar lantarki da muke samu daga babban kamfanin rarraba wutar lantarki na kasa bai wuce megawatt 3,000 ba gaba daya yankin Arewa mai jihohi 19, wanda wannan kaso kusan shi ake baiwa jihar Legas ita kadai. Abin tambaya me gwamnatocinmu da ‘yan majalisun mu suke? Ina sarakuna da ‘yan boko ina tsofaffin sojojinmu ina sababbinsu ke ina kungiyar dattawan Arewa? Ina duk masu fada aji da muke dasu me sukayi akan cewa yankin Arewa ya samu wutar lantarki tabbatacciya.

Idan kuma muka koma batun aikin yi tunda yake Manya manyan masana’antun da muke dasu a kano da kaduna sun kwanta dama sakamakon sakacin magabatanmu akan wutar lantaarki me ya rage mana? Abin da muka gada iyaye da kakanni wato sana’o’in hannau, amma duk munyi watsi da su. Ina noma da kiwo duk mun watsar dasu sai tsurarun talakawa marasa galihu suke wannan yanzu.

Yankin Arewa mu muka fi kowane yanki albarkar jama’a a Najeriya amma mune muke da adadi mafi yawa na marasa aikin yi; wani abu da na gani ya bani mamaki shi ne inda naga Inyamuri na sana’ar pawa wato ya sayi saniya ya kai abbatuwa a yanka a rabawa Hausawa naman sukuma su sayar idan yamma tayi su hada masa kudinsa, kaga wannan shine cikakken koma baya awajen mutanan Arewa me ya hada inyamuri da sana’ar pawa? Kuma kaje kasuwar Hatsi ta Dawanau dake kano kasha mamaki inda zaka ga inyamurai na cin karensu da babbaka, inyamuri zai sayi wake da masara da gyero ya kai sito ya ajiye idan yayi tsada ya fito dashi ya sayar.

Mafi yawan matasa yanzu a Arewa basa son yin sana’ar hannu. Kowa ya nade hannun riga yana jiran ya samu na banza babu sididi babu sadada. Muna da dimbin matasa da suka kamala jami’a basu da aikin yi, amma kuma su baza suyi sana’a ba indai ta hannu ce kowa ya dogara da cewa sai aiki mai maiko ko kuma aikin da zakayi kudi nan da nan, don haka kullum sana’o’inmu kara komawa baya suke yi. Mafi yawan sana’o’inmu basu da bukatar kama hayar shago ko kanti basu da bukatar kudi da yawa amma zaka samu tashoshi na matasa agefen tituna acikin biranenmu na Arewa suna zaman banza.

Zance na gaskiya iyaye sun taimaka wajen kara yawan masu zaman banza a Arewa. Domin kuwa zaka ga yaro baya samun wani kwarin gwiwar cewa yay i sana’a tun yana karami, haka kuma anshagwaba yara talaka da mai kudi kowa ya shagwaba dansa kaga saurayi dan shekara 18 zuwa 20 harma 25 ana bashi kudin kashewa mu duk agurinmu yaro ne; wanda inda aka cigaba duk dan shekara 15 ya tashi daga sahun yaro ya koma saurayi. Misali a kasar Jamus duk dan shekara 18 dole ya fita daga gidan iyayansa ya nemi na kansa don fuskantar rayuwarsa. Idan banyi karya ba zaka iske matashi dan shekara 30 a Arewa yana zaune agida baya aikin fari bayan a baki kuma ana ciyar dashi da tufatar dashi kai harma da bashi kudin kashewa amma babu wani kwarin gwiwa da ake bashi nacewa yaje ya koyi sana’a.

Ka shiga ka suwanninmu kaga yanda matasanmu suka zama ‘yan kamasho. Mutum zai wanke riga ya fita kasuwa banda haram babu abin da ya tafi nema da sunan wai ya tafi kasuwa amma bashida rumfa ko kanti bashida jari kona kwabo, kawai yana ci ajikin talakawa ‘yan uwansa da daurin gindin wasu daga cikin ‘yan kasuwa. Bayan idan za’ayi Magana ta gaskiya shi kansa kasuwancin da muke takama da shi anyi rugu-rugu da shi ‘yan kasuwa nawa ka sani wadan da suka karye kodai sakamakon bashi ko fashi ko damfara ko zurmiya ko sanbanza da zulama? Suna da yawan gaske basa samun wani tallafi na kirki daga al’umma ko daga gwamnatoci. Yanzu kusan duk kasuwanninmu Sinawa da indiyawa sun mayesu idanma kaga muna kasuwanci to ba namu bane su mukemawa. Me ya janyo mana fadawa wannan hali?

Haka kuma gwamnatocinmu basuyi mana wani tsari na koyar tare da fadawa yara muhimmancin sana’a ba a makarantu tundaga sakandare har zuwa jami’a. ya kamata ace acikin jadawalin karatunmu akwai koyar da sana’o’I yaro tun yana makaranta akoya masa wani abu da zai iya yi ana gaba, haka suma jami’o’I ya kamata ace akwai wani tsari na karfafawa dalibai gwiwa idan sun kammala jami’a su dogara da kansu ba lallai sai mutum ya yi aikin gwamnati kona kamfanonin sadarwa ko wani muhimmin aiki zai zama wani ba.

Na karanta a wani shafi na Makarantar kimiyya da fasa wanda Abubakar salihu baban sadiq yake kula dashi. Inda ya kawo wata kasida da marigayi steve jobs wanda shi ne shugaban kamfanin Apple inc Kafin rasuwarsa dai ana kirga shi daga cikin mutanen da suka yi tasiri mafi girma a duniya wajen habbaka harkar sadarwa da kere-kere, musamman kan wayar salula, da kwamfuta, da na’urorin sadarwa nau’uka daban-daban, da allon shigar da bayanai na kwamfuta (Keyboard), da lasifika da dai sauransu. A yadda shi wannan mutum ya bada tarihinsa ya ce shi bai samu damar yi ko kammala jami’a ba, ya maida kai waje sana’ar hannu ne a karshe ga yadda Allah ya mai dashi. Na kawo wannan ne a matsayin misali kawai.

Ya kamata yanzu duk da wasu gwamnatoci suna kokarin koyawa matasa sana’o’i tare da basu jari, ya kamata wannan shiri ya shiga cikin jadawalin koyar da karatu tundaga matakin sakandare har jami’a kamar yadda yake a shekarun baya.

Yanzu idan ka dauki harkar kiwon kaji da kiwon kifi kawai wata babbar sana’ace da zata rike mutane da yawa, misali ka kalli yawan jama’ar kano da kaduna da sokoto zaka iya kididdigar kwai nawa ake ci a wadan nan garuruwa ko kuwa kifi nawa ake ci? Amma wani abin ban Haushi da takaici shi ne kaso sama da 50% na kwan da muke ci bama iya samar da shi a Arewa sai anshigo mana da shi daga kudu duk da albarkar da Allah ya bamu ta ruwa da kasa mai yabanya.

Mu kanmu yanzu a Arewa sai kaga cewa kamar wani mulkin mallaka ake yi mana domin irin gonakan da tsohon shugaban kasa Obasanjo ya sa aka sayarwa da manoma ‘yan kenya da zambabwe a jihohin Taraba da Kwara ake amfani da matasanmu su noma kuma akwashe a fita dasu daga baya a sarrafa wani abu a kawo mana a farashi mai dan karen tsada bayan mu muka sha wahalar. Allah ya kyauta.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@hotmail.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

Sunday, November 27, 2011

Rikicin Kabilanci da na Addini a Najeriya: Ina Mafita

Najeriya kasace da ta fi kowacce kasa yawan jama'a a nahiyar Afrika kuma kasace mai kabilu daban daban ga kuma yaruka masu yawan gaske kusan kididdiga ta nuna akwai yaruka sama da 250 a Najeriya, kamu Allah ya albarkaci Najeriya da Dumbin arzikin da kusan baitaba baiwa wata kasa aduniya ba kamar yadda masana suke fada, Haka kuma najeriya tana da addinin musulunci da kirista da kuma masu addinin gargajiya.

Duk dan Najeriya ba zabinsa bane ya kasance dan asalin wannan kasar, haka Allah yaso ya hada kura da akuya agarke daya haka Allah ya liccemu kuma ya hadamu a wannan guri da ake kira Najeriya bada zabin mu ba, kuma yayimu kabilu daban daban, wani Bahaushe wani Inyamuri wani kuma bayerabe haka kuma wani dogo wani gajere wani baki wani fari wani mummuna wani kuwa idan ka ganshi kamar shi yayi kansa, Allah mai yadda yaso, hakadai Allah ya yimu bisa zabinsa kusan da za'a tambayi dan Najeriya me ye zabinsa watakila da ba nan zaice ba. mukam muna yiwa Allah godiya da muka kasance 'yan Najeriya kuma masu kishin kasarsu kamar yadda kowanne mahaluki aduniya yake kishin kasarsa, misali duk dan kasar Mesedoniya baiyarda da cewa wata kasa tafi kasar sa ba, domin kuwa tun a makaranta duk yaro ana gaya masa daga Allah sai mesedoniya don haka ne suke alfahari da kasarsu da kuma yarensu.

Yawaitar rikicin Addini dana kabilanci a najeriya, mu duba rikicin kafancan a jihar kaduna wanda akayi ashekarar 1987, mutum nawa ne suka rasa rayukansu da dukiyoyinsu basuji basu gani ba, aka maida wasu marayu wasu mata kuwa suka koma zawarawa.

Sannan mutum nawane wadan da aka hallaka sunaji suna gani saboda kabilanci a Idiyaraba a shekarar 2002, Haka kuma mutum nawa aka kona aka lalata musu dukiyoyinsu aka raba iyaye da 'ya 'yansu a shagamu ashekarar 2001 badon komai ba sai kawai don kabilanci shin su sukayi kansu ne? Mu kalli yadda matasa dauke da makamai suka dirarwa kauyen agbohol a jihar bunuwai ashekarar 2004 wai suna ikirarin su mutanen ba 'yan asalin kauyen bane kawai sabida bambamcin kabila.

An kashe mutane da yawa kana kuma aka jikkata wasu da dama arikicin zangon kataf a shekarar 1992 inda aka yiwa musulmi da kirsta

kisan gilla da kisan wulakanci basuji basu gani ba kawai don biyan bukatar wasu. Sannan mu kalli abin da yafaru a yankin kudu maso

kudu tsakanin kabilun Ijow da itsekiri aka kashe yara da mata da basuji basu gani ba, badon komai ba sai don bambancin kabila

ya kamata mugane kowannenmu bazabinsa bane ya kasance dan kabilar da yake.

Haka kuma mu duba irin yadda rikicin jos wato jihar pilato yaki ci yaki cinyewa tsakanin musulmi da kirista inda yake neman zama

wani dan karamin yakin dumiyar Najeriya, kusan wannan rikici yafaru kashi kashi kusan yafi cikin yatsu amma har yanzu wutar wannan

rikici bata lafa ba, Kusan tundaga shekarar 2001 jihar pilato tayi bankwana da zaman lafiya, har kawo yau wannan rikici bai lafa ba.

A shekarar 2004 rikicin addini ya fara aukuwa a kauyen yalwa dake cikin karamar hukumar Shandam wanda sanadiyar wannan rikici ne

ya watsu zuwa wasu garu ruwa makwabta irinsu karamar hukumar lantan ta arewa da ta kudu da ma wani yanki na Wase wanda

sanadiyar haka ne wannan rikici ya watsu har zuwa sauran jihohi makwabta irinsu kaduna da kano inda aka halaka dukiya mai dumbin yawa

kuma aka kashe rayuka masu yawan gaske kuma aka jikkata wasu, kusan shi rikici masominsa aka sani amma ba'a san karshensa ba,

kusan wannan rikicin da ya samo asali daga kauen yalwan shandam shi ne ya sake barkewa ashekarar 2006 inda a sanadiyar wannan rikicine

dubban jama'a suka rasa rayukansu da dukiyoyinsu.

Kusan rikicin da yafi kowanne kazanta shi ne wanda ya faru a shekarar 2008 wanda ya samo asali daga zaben karamar hukumar Jos ta arewa,

inda daga rikicin zabe ya koma na addini kuma kusan wannan rikici da ya auku shiryayye ne domin ko shakka babu musulmi suke da rinjaye

a wannan karamar hukuma ta jos ta arewa kuma inda zakasan abin da makirci ya mai karatu hukuma sai ta sanya ranar zaben ta kasance ranar

Alhamis inda za'a wayi gari juma'a ranar da musulmi ke fitowa sallar juma'a inda aka hallaka musulmin da basuji ba basu ganiba inda asanadiyar

wannan rikicine 'yan sanda suka binne gawarwaki 426 a rami daya bayaga biliyoyin dukiyar da aka rasa da kuam dubban motocin da aka kona

bayan wannan wani rikicin ya sake barkewa a Dutse-Uku duk a karamar hukumar jos ta arewa, a sakamakon wani mutum da yazo maida

gidan da aka kruguza masa kiristoci suka farmasa a wani kaulin kuma sakamakon wasan kwallo da wasu musulmi sukayi a harabar wata coci,

wallahu a'alam, baya ga wannan rikici na watan nuwamba a wannan shekarar ta 2008 wani rikicin ya sake barkewa wanda kuma ya kazanta inda 'yan sanda sukace sun kirga gawarwaki 362 a yashe akan titi, haka kuma anyi ta ganin wasu gawarwakin musamman a garin Digo na Hauwa inda akaringa ganin gawa acikin rijiya da shadda da gurare marasa kyan gani. Haka kuma babu wanda zai iya kiyasta adadadin mutanen da suka rasa ransu a karamar hukumar Riyom da kuma Dogo na Hauwa.

Baya ga wannan kuma ga kisan mummuke da akeyi da kuma dauki day-day aciki da waje garin jos inda zaka ga wani akwata wani rijiya wani

ma yashe kan titi. Abin tambaya anan shine me yasa a yankin jos ta arewa ne wannan rikici yafi faruwa. Anan ina ga ya kamata gwamnati tayi

duba na tsanaki dan gane da abin da yafi dacewa da jihar pilato idan rabata shi ne mafi alkhairi to babu jira abinda ya kamat ayi kenan.

Kuma me yasa najeriya tayi kaurin suna wajen rikicin addini da na kabilanci shin mukadai ne kabilu da yawa mukadaine muke da bambancin Addini.

Malamai sun sha yin wa'azi a masallatai, haka kuma acoci anshayin irin wannan wa'azi cewaDuk Addinin Musulunci dana kirista babu wanda yake umarni da kisan ran da bataji bata gani ba. Kuma musanifa Dukiyoyin mu ne muke halakawa wanda mukayi wahala wajen tarawa, tayaya muna halaka dukiyoyinmu da kanmu kuma zamu kirawo masu saka jari kasarmu shin su mahaukata ne basa sin dukiya ne.

Mafita shi ne muji tsoron Allah mu koma ga Allah duka musulmi da kirista, kuma yaka mata gwamnati ta hada kai da kungiyoyi irinsu spreme council

for Sharia in Nigeria da Jama'atu nasrul islam da crristian Association of Nigeria da kuma masu rike da sarautu da malaman addini wajen kawo

karshen wannan rikici. Allah ya zaunar da kasarmu lafiya ya bamu karuwar arziki da wadata Amin.

Yasir Ramadan Gwale

Shugaban kungiyar muryar Talakawan

Najeriya reshen jihar kano.

07028690570

Shin ko Gaddafi Ya Tafi Da Mafarkinsa Na Raba Najeriya?

Kanar mu’ammar Ghaddafi kusan shine shugaba mafi da dewa a duniya a wannan zamani. Gaddafi kusan ya shafe shekuru sama da arba’in yana mulki ko kuma shugabancin kasar Libya kusan a wannan karnin babu wani shugaba da ya shafe irin wadan nan shekaru yana shugabanci.

Dukkan mutumin da ya san abu mafi tsawon lokaci zai fahimce shi sosai. Kamar yadda Gaddafi ya shafe lokaci lokaci mai tsawo yana shugabanci za ayi masa zaton cewa yasan shi ciki da bai, wato za ayi masa zaton cewa yasan dukkan wani abu da shugaba ya kamata ya yi wajen kyautatawa al’ummarsa haka kuma yasan dukkan wani abu da zai tsanantawa al’umma.

Hakika idan ana batun shugabanci na adalci Gaddafi ya kamanta. Kanal Gaddafi da ya shafe tsawon lokaci yana shugabancin kasarsa ta Libiya kuma ya kyautatawa al’ummarsa daidai gwargwado. Misali Gaddafi yana daya daga cikin shugabanni kalilan da suka damu da jindadi da walwalar al’ummarsu. Muhimmin aikin da gaddafi ya yiwa Libiyawa shi ne irin yadda ya samar musu da ruwan dadi sakamakon kasar libiya tana kewaye da tekun Mediterranean sea daga Arewacin kasar da kuma Arewa maso yammacin kasar kuma gashi kasace maicike da sahara daga yamma da kuma kudu da gabas wannan ruwa na teku dake arewa da kuma Arewa maso gabas ruwa ne mai gishiri da kuma zartsi, haka gaddafi ya keto daruwan dadi daga gabar tekun Tyrrhenian sea wanda ke daura da tsibirin Malta wanda ke gab da kasashen Turai ta yamma.

Bayaga wannan kokari da gaddafi yayi na samarwa da mutanansa da ruwa mai dadi ko kuma wanda aka rage gishirinsa da kaso mai yawa. Sannan gaddafi ya samarwa da mutanansa da ilimi kyauta tundaga matakin farko na firamare har ya zuwa jami’a. ba wai Libiyawa ba kawai harma da mutanan Afurka da kasashen larabawa matalauta kamar Siriya da Yaman Da palasdinu. Haka kuma Gaddafi ya samarwa da mutanasa harkar lafiya kyauta da kuma kayan masarufi kamar kyauta.

Sannan kuma Gaddafi yana taimakawa da marasa galihu da albashi indai ‘yan libiya ne kuma ko ina suke a duniya, haka kuma yace duk wani abu da dan libiya libiya zai saya kamar mota da kayan kere-kere na zamani zai biya rabin kudin ne gwamnati zata biya masa rabi. Haka kuma maganar gidan zama bakada bukatar ka gina ko kasayi gidan idan kana libiya gwamnatin gaddafi zata baka gida har tsawon rayuwarka kuma ta baiwa ‘ya ‘yanka.

Bayan haka, Gaddafi ya taimakawa kasashen Afurka matalauta da kudade masu dimbin yawa, wani abin burgewa dangane da Gaddafi shi ne cewa ba ataba samunsa ko zarginsa da wawure dukiyar kasarsa ba, ko shakka babu Gaddafi ba barawo bane, kusan shi ne shugaba daga cikin larabawa da ya fara kirkiro wata hukuma mai suna “ min aina laka haza” ma’ana ta in aka samu wannan kamar kace wani dan karamin hisabi kuma wannan anayiwa duk dan libiya idan karshen shekara ta zo kuma ana farawa daga shugaban kasa ne zuwa kasa.

Sai dai kash gaddafi daga karshen rayuwarsa ya ringa wasu abubuwa da suka saba da yadda aka sanshi. Inda ya ringa taimakon kungiyoyin tarzoma da tada hankali a kasashen larabawa da Afurka wannan ta soma janyo lalacewar dangantaka tsakaninsa da kasashen Turai da Amerika. Gaddafi yay i ta kokarin hade kan kasashen Larabawa a matsayin wata kasa guda a karkashin shugabancinsa sai dai hakarsa bata cimma ruwa ba inada mafi yawan kasashen larabawa suka ki amincewa da shi akan wannan batu. Wannan tasa ya watsar da wannan batu nasa ya koma batun kafa kasar Afurka kwaya daya karkashin shugabancinsa wannan ma dai bata samu ba ga Gaddafi,

Mafiya yawan mutane sunyiwa Gaddafi gurguwar fahimta. Da yawan mutane musamman musulmi daga yankin Afurka ta yamma suna kallon Gaddafi a matsayin wani shugaba mai kishin addini wanda zance na gaskiya ba mai kishin addini bane kalamansa da ayyukansa suka nuna haka, sai dai Gaddafi yana da matukar kishin larabawa da kasashen larabawa, domin Gaddafi yay i kaurin suna wajen nuna soyayya ga kasar Palasdinu, kuma kullum batunsa shi ne sai munkwato kasarmu ta al’ummar larabawa daga hannun yahudawa abokan gaba bawai kasarmu ta mu Musulmi yake cewa ba.

Gaddafi mutum ne da ya jingine hukuncin Allah. Kasan cewar libiyawa suna son tafiyar da kasarsu bisa tsarin islama amma Gaddafi yace sam bazai tafiyarda gwamnati bisa tsarin musulunci ba saidai zai tafiyar da gwamnatinsa bisa tsarin wani kundi da ya kira da suna “Green Book” tsarine da akaso anuna addini amma duk wani tsari na Allah babu shi cikin wannan tsari ya zama shiba alqur’ani ba kuma shi ba constitution ba. Wallahul musta’an duk da wannan zuma da gaddafi yake baiwa mutanensa sunfi son tsarin Allah da Manzonsa.

Daga baya mai aukuwa ta auku ga shugaba kanar mu’ammar Gaddafi. Inda mafi yawan mutanan da aka Haifa karkashin mulkinsa suka bijire masa da taimakon kasashen Turai da Amerika da NATO sakamakon wani juyin juya hali da ya bulla a kasashen larabawa a wannan lokaci.

Gaddafi ya yi kira da a raba kasar Najeriya zuwa kasashe guda biyu. Wato kasar Musulmi da ta Kirista Musulmi masu kasa daga yankin Arewacin Najeriya mai hedikwata a Abuja da kuma kasar kirista daga kudunancin Najeriya mai hedikwata a Lagas, kamar yadda ya faru tsakanin kasar sudan mai hedi kwata a khartoum da kuma sudan ta kudu mai hedikwata a Juva. Wannan ta fusata shuwagabannin Najeriya inda shugaban Majalisar dattawa ya kirashi da cewa “Mahaukaci ne”. wanda wannan maganar ta marigayi Gaddafi abar kallo ce da kuma duba na tsanaki.

Ko shakka babu alamu sun nuna cewa da wahala kasar Najeriya ta cigaba da zama tsintsiya madaurinki guda. Domin yadda muke a yanzu ko shakka babu ana kwarar wani bangare wanda wannan shi ne babban abin da ya haifar da kasar sudan ta kudu wato rashin adalci, kuma idan ba ayi hankali ba maganar Gaddafi zata tabbata,domin shugaban kasa da yafi kamata ya nuna adalci ga al’ummarsa shi ne mutum na farko da ke nuna bangaranci da fifiko ga wani bangare da kuma wasu mutane.

Tabbas maganar Gaddafi dan gane da raba Najeriya bawai kawai da ka ya yita ba. Domin ya shafe kusan tsawon sama da shekara arba’in yana kallon Najeriya watakila lokacin da yake shugaban kasa a libiya shugaban Najeriya na yanzu yana makarantar sakandare ko firamare to kaga babu yadda za ayi tunani da hange nasu yazo daya. Allah masani, lokaci ne kawai zai tabbatar mana cewa shin maganar Gaddafi dangane da Najeriya zata rabu ko kuwa zata ci gabada zama kasa daya al’umma biyu.


Sufurin Jirgin kasa a Najeriya: jiya ba Yau ba!

Sufurin Jirgin kasa a Najeriya: jiya ba Yau ba!

Jirgin kasa kusan shi ne abin sufuri da yafi kowace hanya ta sufuri sauki da kuma tabbas. Jirgin kasa shi ne abinda da zaka hau ba tare da fargaba ba ko zullumi, baka tunanin hadari ko ‘yan fashi ko ‘yan kwanta-kwanta. Sannan zaka hau jirgin kasa cikin kudi kalilan. Jirgin kasa ana yi masa kirari da dama, kamar yadda shugaban Amurka ya taba kamanta gwamnatin Amurka da cewa kamar jirgin kasa ta ke ba shida ikon sauya akalar jirgin sai dai kawai ya kara gudunsa ko ya rage gudunsa.

Jirgin kasa ya fara zurga zuraga ne a Najeriya ranar 4 ga watan maris din shekarar 1901, inda yake safara daga Legas zuwa Ibadan cikin sauki da kwan ciyar hankali a wancan lokaci ga kuma arha, jirginsa ka du mutum ka dau kayansa kamar yadda masu Magana suke cewa. Daga nan likkafa taci gaba inda a shekarar 1911 aka sauya jirgin kasa a Najeriya daga mai aiki da gawayi zuwa mai aiki da man dizal sannan kuma aka kara zangon da jirgin zai ci har zuwa Arewacin Najeriya inda yake cin zangon kilomita kusan 45,000 acikin kasar nan.

Duk wannan suna karkashin hukumar sufurin jiragen kasa ta wancan lokacin inda take da jiragen kasa kimanin guda 50 wadanda ke safara gabad da yamma kudu da Arewa. Jirgin kasa kan tashi tundaka ikko ta jihar Legas har zuwa Nguru a jihar Borno ta wancan lokacin inda daga nan yakan ratsa har tsohuwar rusasshiyar jihar Gongola ta wancan lokacin, gashi da manya-manyan tashoshi a kudu da arewacin kasar nan.

Kusan babbar moriyar da akaci ta jirgin kasa a wancan lokacin itace safarar kaya da yake daga kudu zuwa Arewa inda yake Daukar gyada da fatu da kiraga da hatsi da kayan gwari wato tattasai da albasa da attarugu ya kai kudancin kasarnan, sannan ya dauko kayan Marmari kamar ayaba da lemo da kwarar manja da da tufafi ya kawo kasar Arewa, jama’a na amfani dashi cikin kwanciyar hankali. Kusan duk lokacin da jirgi ke zuwa daga kudu zuwa Arewa idan ya yada zango a zariya jama’a kan samu Alheri sosai ta fannoni da daman gaske, haka har ya karaso kano inda nan ma zakatar wata kasuwa ce ta musamman a duk lokacin da akace maka jirgin kasa yazo jama’a na ta hada-hada abin gwanin ban sha’awa. Haka nan jirgin zai tashi har ya isa jogana inda nan ma yakan yada zango duk dai jama’a na ta kaiwa da kawowa ana ta neman arziki.

Kwanci tashi hukumar jiragen kasa dake da ma’aikata kimanin 3505 a duk fadin kasar nan da kuma makarantar koyar da aiki da tukin jirgin kasa dake legas duk suka fara sukurkucewa. Itadai wannan makaranta har yau har kwanan gobe tana nan kuma ana karatu ana yaye dalibai, amma hukumar kula da sufurin jiragen kasa ta Najeriya wadda akafi sani da Railway yanzu ta shiga wani hali na ha’u’lai inda kamfanin ya tarwatse baka ganin komai sai karafa da tarin shara da tsoffin gine-gine tun na turawan mulkin mallaka a duk jihar da layin dogo na jirgin ya bi.

A wancan lokacin da ake amfani da jirgin kasa zaka iske duk titunan kasarnan suna da kyau babu gargada tundaga badagari har zuwa baga duk inda kaga titi da kyansa da lafiyarsa, da wahalar gaske kaga mota tayo laftun kaya tana bin kwalta duk wani kaya mai nauyi da za ayi doguwar tafiya da shi yana tashar jirgin kasa; wata kila wannan shi ne dalilin da yasanya tituna suke da ingancin gaske a wancan lokacin.

Amma abin yanzu ba haka yake ba. Kusan kasar nan tafi kowace kasa bada mamaki a duniya domin bawai komawa baya kawai Najeriya ta ke yi ba kawai aguje a sukwane take komawa baya kuma a murgude. Yanzu maganar da muke dukkan wadan can jirage da suke safara daga kudu zuwa Arewa sun daina wato sun zama tarihi dukkan wata safara yanzu ana yenta ne adogayan motoci masu daukar kaya fife da kima.

Kusan ashekaru 1960 zuwa 1970 dukkan manyan gurare a Najeriya zaka iske da wutar lantarki inda alokacin nan Masallacin juma’a na kofar gidan mai martaba sarkin kano lantarki ake kunnawa a ya yinda masallacin dakin Allah mai alfarma da ke makka acibalbal ake kunnawa ballantana ma kayi tunanin jirgin kasa acan. Amma yanzu bazaka kamanta Najeriya da Saudiyya ba wajen wutar lantarki haka idan ka dauki sufurin jirage kasa sunyi mana fintinaku. Domin yanzu haka akwai irin jirgin nan mai tashi kamar kiftawar ido mai gudun tsiya yana yawo ko ina a kasar.

Alokacin marigayi tsohon shugaban Umaru kasa Musa ‘Yaradua ambayarda kwangilar gyaran hanyar dogo daga legas zuwa kano ga wani kamfaninkasar cana amma har yanzu wannan zance shima shiru ka keji. Ko yaushe sufurin jiragen kasa zai dawo ka’in da na’in a Najeriya? Oho; hana rantsuwa akwai kana nan jirage da suke safara misali a legas da kaduna da kano wanda suna yi ne iyakar jihohinsu. Allah ya kaimu lokacin da harkar jirgin kasa zata koma kamar da a Najeriya.


Waiwaye Adon Tafiya: Rayuwar Bahaushe Ada Da Yanzu

Waiwaye Adon Tafiya: Rayuwar Bahaushe Ada Da Yanzu

Ya dan uwa mai karatu ina mai yimaka godiya da ka samu zarafin karanta wannan mukala tawa, Allah ya sa mu dace amin. Ko kasan rauwar malam Bahaushe a lokutan baya da suka gabata rayuwace mai ban sha’a kwarai da gaske domin tundaga Burgu har zuwa yahuri duk inda kaga malam bahaushe halinsu daya wajen tausayi da amana da biyayya da kamun kai ga kuma taimakon junansu.

A taikaice ya mai karatu Bahaushe kusan dukkan kabilun kasarnan babu wanda ya kaishi gaskiya da amana, wannan tasa kowacce kabila ta ke son hulda da malam bahaushe ba don komai ba sai don tsare gaskiya da girmama abokin zamansa. A lokutan baya wannan tasa ko kasuwanci za’a kulla tsakanin kabilu akan nemi malam Bahaushe ya zama shaida domin ana da yakinin bazaiyi ha’inci da rashin amana ba.

Zaka yarda dani idan ka kalli yadda baki daga kasashen waje idan suka zo nageriya sukan so su zo kasar hausa, misali shuwagabannin kasashe da yawa sun kawo ziyara nageriya amma duk wanda yazo nageriya bai zo kasar hausa ba to ka gayamasa tabbas yana da sauran kallo. Shugaban kasar zambabuwe Robert Mugabe yazo kasar hausa har cikin fadar sarkin kano haka tsohon shugaban kasar Tanzaniya wato julios Nyarere da kuma Shugaba yuwairi musabveni na Uganda, dama kar kayi maganar kasashen Ghana da nijar da sudan da kamaru da benin kusan wadan nan kasar hausa ta zama gida a gurinsu.

Idan kuma muka duba kasashen asiya da kasar turai da amurka dukkan wani shugaba da zai kawo ziyarar aiki nageriya yakanso yazo kasar hausa ba don komai ba sai irin yadda suke samun labarin mutanen cikinta. Idan ka dauki kasar ingila kusan zamuce kasar hausa gidace agaresu.

Wani abain ban sha’awa da rayuwar malam bahaushe har gaiyatarsa akeyi zuwa sauran kasashen duniya, badon komai ba saboda rayuwarsa abin sha’awane saboda me yana da kula da al’adunsa aduk inda ya tsinci kansa domin kuwa zaka ga malam bahaushe da sanye da babbar riga da hula da carbi a hannunsa a tsakiyar birnin landan wannan yakan baiwa turawa da yawa sha’awa ta yadda zakaga suna yawan daukar hota dashi. Ya ishi malam bahaushe alfahari shi ne an gaiyyaci hausawa kusan 42 zuwa ingila a shekarar 1897 domin su taya sarauniyar ingila Victoria muranar cikarta shekara 60 abisa gadon sarauta, ko shakka babu wannan wani abune da tarihi bazai mance da shiba arayuwar malam bahaushe.

Idan ka kalli rayuwa da zamantakewar malam bahaushe ta yadda yake kula da makwabtansa tayadda zaka samu malam bahaushe yana cin abinci musamman na dare da makwabtansa, hakana malam bahaushe yakan hada yaran makwabta ya yi masu kaciya ko asanyasu makaranta tare wannan ko shakka babu zamantakewa ce mai kyau. Tayadda wasu musamman turawa mutum zai shekara baice da makwbcin bihin ba, amma idan ka dauki rayuwarmu idan makwabcin ka ya kwana uku bai ganka ba sai ya tambaya anya wane lafiya kuwa kwana biyu bana ganinka. Wannan tasa ko acikin gaisuwar malam bahaushe zakaji ykan kula da makwabcinsa ta hanyar tambayarsa ya iyalinka kuna lafiya, da sauransu wannan tasa naga wani abin mamaki lokacin da muka gaisa da wani balarabe sai na ce ya iyalinka sai yace kaico ina ruwanka da iyalina, ni kuwa na bashi hakuri nace Allah sarki malam bahaushe rayuwarka abinkoyi.

Haka kuma idan ka dubi abokan zamanmu wato yarabawa da inyamurai zaka ga a idiyaraba bayerabe ya dauki malam bahaushe aiki a matsayin mai kula da sashin kudi wanda ko amafarki bazai taba daukar inyamuri ya bashi amanr kudi ba haka abin yake idan kaje abbah idan zaka iske inyamuri ya dauki bahaushe aiki yana kuma kula masa da dukiyarsa bai dauki inyamuri dan uwansa ba, wannan karara ya nuna irin yadda malam Bahaushe yake da amana a wancan lokacin kuma duk inda akaga malam bahaushe da shigarsa ta hausawa zakaga yadda ake girmamasu.

Na taba jin wani dan jaridar Radiyo nageriya Kaduna wato halilu getso yace ya sauka a filin jirgin sama na Heathrow da ke landan yace yaje sanye da kayan hausawa da hula da carbi a hannunsa kuma tafiyace bashi kadai ba yana cikin wata tawaga ce amma yace shikadaine ba’a bincika kayansa ba, yace awannan lokacin jami’an tsaron wannan filin jirgi sun girmamashi yace badon komai ba sai yadda suka samu labarin Bahaushe mutumne mai gaskya da rikon amana, yace aka tambayeshi mene cikin jakarka yace ‘yar kukace da yajin daddawa na kawo wa ‘yan uwana tsaraba sai kuma ‘yan tsummokarana. Yace haka nan ya wuce amma sauran abokan tafiyarsa dake kabilu daban daban ne sun sha tambayoyi da bincike.

Wannan tasa malam bahaushe ya cirri tuta domin dukkan kabilun kasarnan babu mutumin da ake girmamawa bilhakki kamar malam bahaushe kuma ciki da wajen nigeriya duk inda akaga malam bahaushe ana yimasa kallon wani mutum mai amana da gaskiya da adalci awancan lokacin.

Kamar yadda nace waiwaye adon yafiya sai kawaiwaya baya kaga yadda kake sannan sai kayi tunanin gaba me yakamata kayi. Ko shakka babu yanzu rayuwarmu bah aka take ba yanzu za’a hada baki da mista bahaushe ayi yaudara da ha’inci da makici kala-kala, sannan malam bahaushe ya zama mutum mai buri da yawa ga son taro dukiya mai dimbim yawa ta kece raini da auren mata barkatai ga son gina gidaje ko ina amma kuma ko kadan bamu son shan wahala ko ta sisi. Shin taya zamuyi mu dawo da martabar da akasan malam Bahaushe awancan lokacin mai karatu kalubale gareka.

Zuwa ga Marigayi Mallam Umaru Musa Yar’Adua

Ya mai girma tsohon shugaban kasar Najeriya ina yi maka sallama irinta addinin musulunci Assalamu Alaikum. Amincin Allah ya tabbata a gareka ina mai addu’a a gare ka da kuma fatan samun rahamar Allah da kuma addu’ar Allah ya gafarta maka zunubanka. Amatsayin ka na dan Adam kuma wanda ya rayu da mu a wannan duniyar kafin cikar wa’adinka ko shakka babu kai maikuskure ne kamar kowane bil’adama, kuma a halin da ka ke ciki ya shugaba baka bukatar wani abu daga garemu face addu’a da kuma fatan samun rahama daga madaukakin sarki wanda mulkinsa baya karewa haka kuma rahamarsa bata takaita ga wasu kawai ba shi ne da kansa yace ku rokeni zan amsa muku subuhanahu wata ala! tsarki ya tabbatar masa wanda ya dauke ka a dai dai lokacin da Najeriya da ‘yan Najeriya ke bukatarka.

Ya shugaba Mallam Umaru Yar’adua ko shakka babu a matsayina na dan Najeriya kuma mai kishin ta! kuma kasar da ka taba zama shugabanta lokacin da ka ke raye ko shakka babu ka tafi da burace-burace masu yawa, wanda masu magana suna cewa kana ta ka Allah ma yana tasa sai dai ta Allah ita ce tabbatacciya. Tabbas mun san katafi da burin ganin cewar rayuwar dan Najeriya ta kyautatu al’amura sun koma yadda suke; musamman wadan nan kudurori naka guda bakwai da ka sanya a gaba wadan da mukai ta daukin ganin ka cika wadan nan alkawura da ka dauka, kaico mai aukuwa ta kasance a gareka batare da Allah ya cika maka burinka ba. Ina mai yimaka albishir da cewa insha Allahu wadan nan kudurori naka zasu cika ko ba dade ko bajima kuma Allah yaga zuciyarka kuma ina sa ran zaicika maka ladanka.

Ya shugaba tun lokacin da ka kwanta rashin lafiya al’ummar wannan kasa sun tausaya maka kwarai da gaske birni da kauye kowa addu’a yake ta fatan alheri agareka da kuma nema maka sauki agurin Allah agaskiya ban taba ganin mutumin da ‘yan Najeriya suka tausaya masa ba kamar kai ya shugaba, tun kana kasar saudiyya muna ta yi maka addu’a har aka dawo da kai cikin wani hali mai cike da rudani ya shugaba lokacin da na samu labarin saukar ka afilin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da misalin karfe shida na safe a wata kafar watsa labari ni kadai ina kwance sai da na mike na yiwa Allah godiya! gaskiya nayi farin ciki sosai a wannan safiya, kwatsam daga baya sai labarin ya sauya cewa baka murmure ba. Amma lokacin da muka samu labarin wasu malaman addini da shuaban majalisar koli ta tabbatar da shari’a a najeriya Dacta Ibrahim Datti Ahmed sun kai maka ziyara munji sanyi a ranmu cewa kana nan kana samun sauki wannan ko shakka babu ya sa ran duk wani mai kaunarka yayi dadi.

Ranar 5 ga watan mayu da misalin karfe 6 da minti 3 na kunna radiyan Muryar Amurka abin da na faraji shi ne muryarka abinda ya fara zuwa raina shi ne cewa Shugaba ya samu sauki kawai sai najin an saka wakar mutuwa mai bantsoro daga nan hankalina ya tashi domin nasan ta Allah ta kasance agareka, tun a wannan lokaci hankalin ‘yan Najeriya ya tashi domin kuwa ka tafi alokacin da muke begen ganin irin halin da ka ke ciki ya kyautatu, domin kuwa jita-jita ta yadu sosai game da kai, kan kace kwabo jihar ka ta haihuwa Katsina ta fara daukar harami domin ‘yan uwa da abokan arziki da dangi da sauran ‘yan Najeriya suna ta tururuwa domin halartar jana’izarka Allahu Akbar yadda ka tafi haka dukkaninmu zamu taho kuma kasani wallahi kai da ka rigamu bakayi gaggawa ba kuma mu da muke raye ba mu yi jinkiri ba, kamar yadda Mamman shata ya fada a wata waka da ya yiwa chiroman Gwambe.

Ya shugaba bayan tafiyarka abubuwa da dama sun auku a kasarmu Najeriya abu na farko da aka farayi shi ne nada mataimakinka wanda kafin rantsar dashi cikakken shugaba ya rike mukamin mukaddashi, daga nan kuma abubuwa duk suka sauya domin kuwa ‘yan Arewa da yawa sukai ta rugawa Abuja suna kamun kafar neman kujerar mataimakin shugaban kasa, a karshe dai Allah ya tabbatar da ita akan Gwamnan jihar kaduna Namadi Sambo, bayan nan shugaban da ya gajeka yace zai dora daga inda katsaya, domin yadauki alkawarin cigaba da muhimman kudurorin nan naka guda bakwai. Sai dai yanzu babu su babu dalilinsu Bayan haka abin da kayi ta kokarin ganin yasamu shi ne wutar lantarki wadda sabon shugaba yace dakansa zai gyara.

Bayan haka kayi alkawarin aiwatar da karbabbe kuma sahihin zabe wanda nasan da kana raye ka aiwatar da wannan zabe akace baka ciba tabbas nasan da zaka bada mamaki ta hanyar mika mulki ga wanda ya yi nasara, shugaba yaje Washinton a kasar Amurka da Nice a kasar Faransa kuma duk ya yi alkawarin shirya karbabben zabe, inda ya dauko mutumin da kaso 90 na mutanan Najeriya suka kyautata masa zaton zai yi abin kirki a wannan hukuma ta zabe wato INEC mutumin kuwa shi ne farfesa Attahiru Jega wanda kafin dauko shi shi ne mataimakin shugaban jami’ar Bayero da ke Kano. Kuma sabon shugaban ya yi alkawarin cewa bazai bar duk wani mutum da yake dauke da katin wata jam’iyya ba yakasance a cikin wannan hukuma ta zabe. Sai dai anyi zabe kuma wanda yaci yaci wanda ya fadi ya fadi shin ya cika alkawari ko bai cika ba wannan ‘yan Najeriya su ne sheda

Ya mai girma marigayi tsohon shugaban kasa. Yanzu dai duk abin da aka shirya ya kasance. Don shugaban kasa na yanzu wanda tsohon mataimakin ka ne ya tsaya takara kuma wannan hukuma ta zabe karkashin jagorancin Jega ta tabbatar da cewa shi mutanan Najeriya kusan Miliyan 23 suka zaba. Sai dai babban abokin hamayyarsa tsohon shugaban kasa Gen. Muhammad Buhari da jam’iyyarsa ta CPC sun garzaya kotu da nufin kalubalantar wannan zabe; kamar yadda shi Gen. Buhari ya yi a baya na kalubalantar zabenka a karkashin tsohuwar jam’iyyarsa ta ANPP wadda tsohon Gwmanan Jihar Kano Mallam Ibarhim Shekarau ya yiwa takara.

Ya mai girma marigayi, kamar yadda ta faru a lokacin ka kotun sauraran kararrakin Zabe ta tabbatar da shugaba mai ci wato Goodluck Jonathan a matsayin wanda ya lashe wannan zabe. Kamar yadda ta faru a agareka. Ya maigirma tsohon Shugaban kasa na so nayi babbar mantuwa ta rashin shida maka abin da ya biyo bayan sakamakon zaben shugaban kasa.

Kusan bada sakamakon zabe ke da wuya sai rikici ya barke a kusan daukacin jihohin Arewa inda matasa suka fusata suka yita kone-kone musamman Gidajen sarakuna wadan da ake zarginsu da karbar toshiyar baki da kuma gidajen fitattun ‘yan siyasa kamar Alh. Bashir Tofa da Rt. Hon. Ghali Na’abba a kano haka abin yake a kaduna kai hattana tsohuwar ministarka ta ilimi Haj. Aishatu Dukku wadda ake kallo a matsayin wadan da suka raba gari da shugaba mai ci itama bata tsira ba daga wannan kone-kone, antafka asarar dukiya mai dimbin yawa. Bayan da Dantakarar jam’iyyar CPC Gen. Buhari ya barranta daga masu wannan kone-kone inda yace hattana shima an kona masa motoci abin ya lafa.

Daga nan kuma aka shiga batun hada-hadar rantsar da sabon shugaban kasa. Wanda wani abu mara dadin ji ya faru a yayin wannan hidima, ya maigirma tsohon shugaban kasa juma’ar da ta ta zo kafin ranar lahadin da a itane za a rantsar da shugaban kasa an tsaurara matakan tsaro a kusan ko wane gefe na babban birni tarayya Abuja, inda Musulmi da zasu tafi Babban masallacin kasa sallar juma’a aka tsananta musu ta hanyar sa su daga hannu sama da yin doguwar tafiya a kasa kafin sukai ga masallacin, ya mai girma shugaba lokacin da aka rantsar da kai bamu fuskanci wannan matsin lamba ba. Wannan ta sa limamin da ke fassara huduba da turanci Uztaz Abubakar Siddeeq ya nuna rashin jin dadin abin da akayiwa musulmi inda yace harda jakadun kasashen duniya sun fuskanci wannan wulakanci, wannan ta kai ga dakatar dashi akan wannan aiki da ba biyansa albashi ake yi ba.

Ya mai girma marigayi Umaru YarAdua, bayan rantsar da shugaban kasa ya sauya dukkan al’amura ba yadda aka tsammata ba. Sannan ya kafa kwamiti karkashin dattijo wato Sheikh Ahmad Lemu kan ya binciki musabbabin wannan rikici da ya biyo bayan zaben shugaban kasa, kwamitinsa ya yi bincike na gaskiya da adalci kamar yadda muka zata kuma ya mika rahotonsa! Rahoton ya kunshi muhimman abubuwa wadan da idan har ambisu za a samu kyautatuwar al’amura, wanda kuma suka tsoratar akan cewa matukar aka bi son zuciya aka kaucewa wannan rahoto kasar nan na iya fadawa wani mawuyacin hali da kasashen larabawa suke ciki a yanzu.

Bayan nan kuma, wasu muhimman al’amura da suka shafi tsaro sunyi ta aukuwa, kamar rikicin Jos wanda musulmi suka ji haushinka a lokacin da kake raye inda kaje ta’aziyar rasuwar Gbom Gom Jos da Victor Pam, amma ko ka tsaya ka jajan ta musu. Wannan rikici dai har yanzu da nake rubata maka wannan kasida yana nan kuma yana cigaba, shugaban kasa da gwamnan jihar plateau sun kasa shawo kan wannan al’amari, kisan rai kusan yanzu har ya zama ba labari ba a birinin Jos da sauran sassan jihar plateau.

Haka kuma ya shugaba, Rikicin nan na Boko Haram da ka bada umarnin gamawa da su kafin tafiyarka ta karshe zuwa neman magani saudiyya wanda shi ne ya kai ga halaka shugaban kungiyar mai suna Mallam Muhammad Yusuf, wannan rikici shima ya dauki sabon salo inda akayi ta tayar da bama bamai a garin Maiduguri abin ya wuce dukkan lissafinmu, har sai da ta kai ga rasa ran Dantakarar gwamna na jam’iyyar ANPP Alh. Madu fannami Gubio da wasu fitattun mutane da masu unguwanni abirnin na Maiduguri, babban wanda ya faru kuma ya girgiza mu shi ne wanda bom ya tarwatse a damaturu ta Jihar Yobe wanda rahoton ‘yan sanda ya nuna kusan mutane 100 ne suka halaka tare da daruruwa da suka ji raunuka.

Sannan kafin wannan na damaturu ya faru. Bom ya tarwatse a hedikwatar ‘yan sanda ta kasa da ke Abuja, ‘yan awanni bayan shugaban ‘yan sanda na yanzu wato Hafizu Ringim ya yi ikirarin cewar kwanakin ‘yan Boko Haram kididdigaggu ne. Sannan an sake samun wani Bom da ya fashe a ginin majalisar dinkin duniya da ke Birnin tarayya Abuja, duka wadan nan hare-hare kungiyar Boko haram ta dauki alhakin kaisu.

Sannan, gwamati ta nada kwamiti karkashin Giltimari na ya duba yadda za’a shawo kan al’amarin ‘ya ‘yan kungiyar ta Boko Haram sai dai wannan ma bai biya bukata ba domin kuwa ‘yan kungiyar sun zargi shi Giltimari da marawa tsohon gwamna Ali Shariff baya, yanzu dai shima giltimari ya mika rahoton sa zuwa fadar shugaban kasa.

Da yawan mutane suna ganin gwamnatin tarayya ta bayar da a huwa ga wadan nan matasa; kamar yadda ka cika kudurinka na farko wato samar da cikakken tsaro a yankin neja dalta ta hanyar yiwa wadan nan tsageru ahuwa da mayarda su makaranta da koya masu sana’o’i da basu jari, wanda wannan shugaban ya cigaba da wannan tsari ta hanyar kashe masu kudi makudai tare kuma da turasu kasashen Turai da Amurka da Malaysia da Afurka ta kudu wai duk da sunan yi musu ahuwa, wanda wannan shi ne abin da ke neman motsa ko kuma iza wutar kabilanci a zukatan ‘yan Najeriya inda da yawanmu ‘yan Arewa muke ganin bai kamata a fifita wadan nan tsageru da wannan ta gomashi ba abar miliyoyin matasa a yankin Arewa suna watan gaririya akan tituna, da yawa suna ganin irin wannan shi yake haifar da kungiyoyi irinsu Boko Haram da darul Islam da makamantansu a yankin Arewa.

Ya mai girma marigayi tsohon shugaban kasa, hukumar nan da ka tursasawa shugabanta na da sauka tare da mayar da shi makaranta a Kuru tare da kokarin kamashi da laifin da bai jiba bai gani ba wato Mallam Nuhu Ribadu wanda shi ma ya yi takarar shugaban kasa a karkashin jam’iyyar ACN a zaben da ya gabata, ka nada Uwargida Farida Waziri a matsayin wadda zata jagoranci wannan hukuma wanda ya gajeka shima ya barta don taci gaba da aiki a wannan hukuma ta EFCC, amma sai dai mafi yawan ‘yan Najeriya sun zarge ta da gazawa wajen aikinta bata iya kai banten ta ba kamar yadda magabacin ta Mallam Ribadu ya kai ta hanyar kame tare da kwato dukiyar da azzaluman shugabanni suka diba alokacin da suke rike da madafan iko. Yanzu dai itama madam Waziri ta kama gabanta a wanna hukuma kamar yadda shugaban kasa ya umarci kakakinsa Dr. Rueben Abbati ya bada sanarwar sauke ta daga shugabancin wannan hukuma da umarta Mallam Ibrahim Lamorde a matsayin wanda zai rike hukumar nan da wani lokaci .

Abubuwa da yawa sun faru, ya mai girma marigayi tsohon shugaban kasa tun bayan barinka wannan duniyar Musamman ma a inda kafi sani wato Najeriya, bazai yiwu gareni na baiyana maka dalla dallar abin da ya faru ba duk da nasan wannan sakona ba zai sameka ba, amma ina fata ya zama izna. Kamar yadda hausawa suke cewa “kukan kurciya jawabine amma......”

Daga karshe ya mai girma marigayi tsohon shugaban kasa, ina yi maka addu’a ta fatan alheri da samun rahama agurin mahaliccinka da kuma fatan can inda ka ke tafi nan. Allah ya tabbatar mana da alheri a kasarmu Najeriya ya azurtamu da shugabanni masu tsoron Allah.