Wednesday, July 29, 2015

Wayar Salula Da Internet Sun Zama Alakakwi


WAYAR SALULA DA INTERNET SUN ZAMA ALAKAKAI 

Yana daga cikin alkhairan da mu al'ummar wannan zamani muka samu shi ne na wayoyin salula da internet da suka saukake mana  al'amura. Kusan yanzu komai mutum zai iya yi da wayarsa, ya shiga duniyar gizo ya wataya. A da wani abun idan ya faru a garinaku da safe karfe goma ba zaka sani ba watakila sai lokacin BBC ko wata kafar watsa labarai ta waje,  amma yanzu cikin sauki mutane na samun dukkan irin labarin da suke so dake faruwa  ko ina a duniya.

Yanzu halin da ake ciki wayar salula ta kashe kasuwar abubuwa da yawa. Yawan masu amfani da computer ya ragu,  domin yanzu duk abinda computer zatai maka wayar salula ma zata iya, sai fa kadan. Yanzu babu bukatar ka jibge tarin kasakasan Radiyo dan jin wa'azi ko disco. Kasset 100 ko 200 da zaka ajiye ya cinye maka guri yanzu dan karamin abu da bai wuce maballin riga ba zai kwashe su duka.

Idan ka kalli wancan janibi sai kaga wayar salula ta kawo nakasu ga kasuwar Radiyo da Computer da kuma masu sana'ar sai da kaset na kida ko na wa'zai. Domin abinda sai ka saya da kudi a da yanzu kusan a bagas zaka same shi, wajen wanda baka sanshi ba be sanka ba, wuyarta kawai kana da Internet. 

Kwanaki dan uwa Malam Hamisu Nasidi Baban Auwaab​ yake bamu labari cewar, suna zaune bayan sun gaida kakarsu sai kowa ya koma gefe ya dauko waya yana latse latse, abinda kakar ta ce musu "ku matasan yanzu bakwa yin lazimi sai latse latsen waya" a hakikanin gaskiya lokacin da naga wannan magana ta tsaya min a Rai, domin yadda naga yadda muke amfani da wayoyinmu abin na neman zamar mana alakakai. 

Kusan yanzu abinda muke fara yi daga tashinmu daga bacci shi ne danna waya, haka kuma abu na karshe da galibi muke yi shi ne danna waya. Da yawa tuni suka dena yin Azkar na safe da yamma, kai yanzu hatta azkar na bayan idar da Sallah wasu sun dena, sabida gaggawa mutum ana idar da Sallah zai dauko waya yana duba Whatsapp ko Facebook​ da sauransu, kuma wannan lamari babu batun su wane, kusan duk munyi tarayya da Limamai da masu bin Sallah da kowa da kowa.

Wayar salula ta ragewa mutane yawan magana. A da sai kaga mutane sun hadu ana tattaunawa, amma yanzu daga an gaisa sai kaga kowa ya dauko wayarsa yana latsawa, hatta a makabarta wajen binne gawa sai kaga mutane na daddanna waya, haka wajen makoki ko gidan biki da sauransu. Wayoyin sun dauke mana hankali da lokaci fiye da yadda muke tsammani. 

Mutane hatta abinci basa iya ci a nitse sai suna danna waya, sabida kowa baya san wani abu ya wuce masa.Aboki sai ka je wajensa amma idan kai lissafi sai kaga yawan danna wayar ku yafi yawan maganarku. Rayuwarmu ta zama kowa ba shi da lokaci, da yawan mutane suna Ikirarin karancin lokaci amma a zahiri lokacin duk yana wayoyinsu. 

Gaskiya dai ga wasu waya ta zamar musu alakakai. Domin hatta sirri yanzu mutane ba su da shi sosai,  domin wani ko ina za shi sai ya rubuta ya sanar, kai wani ko bandaki yake sai kaga ya dauki hoto ya sa a facebook wasu kagansu adakin girki wani a can cikin daki zaka ga ya dau hoto,mata kuwa suyi ta abinci yana konewa sabida waya.

Ni kaina na sha dora girki abincin ya kone sanadiyar dannan waya, wannan ya faru yafi karfin lissafi. Gaba dayan lokutanmu suna Whatsapp da facebook da Twitter da sauransu. Kuma abin mamakin irin wadannan tashoshi na haduwarsa  mutane kullum sabbin ake kirkirowa wani zaure idan ka shiga sai kayi zaton babu kowa, amma sai kayi rajista ka shiga kaga jama’a dankar na ta watayawa. 

Lallai ya kamata mu farga kan yadda babu gaira babu dalili aka dauke mana lokaci. Dalibai basa iya tsayawa suyi karatu da kyau, Malamai basa iya karantarwa da kyau, Kaga Malami na danna waya dalibai ma na dannawa ana shiga shafukan zamunta. Kuma hatta a lokacin Jarabawa duk da gargadi da ake amma sai ka samu wasu suna duba Whatsapp ko Facebook, zakai mamaki mutum ya rubuta cewar yanzu haka ina dakin jarabawa ina neman addu'ar ku. 

Wani yace yanzu hatta hadari idan ya faru maimakon mutane sukai agaji, kawai sai su fara daukar hotuna. Kaga kawai mutane na yada hotuna na tashin hankali dan kawai suna san bada labarin wani hadari da ya afku,  musamman wannan lokacin da Allah ya jarrabemu da tashin Bom mutane daga zarar Bom ya fashi a inda suke, to sun samu aikin daukar Hoto ana yadawa, a wani hoto da na gani a  Gombe da wani Bom ya tashi ga mutum ya a kone da ransa amma naga mutane ba ta shi suke ba daukar too kawai suke.

Yana da kyau mu karawa kanmu lokacin kara kusanta ga Allah. Allah ka shiryemu. 

Yasir Ramadan Gwale​
29-07-2015

Saturday, July 18, 2015

SALLAR BANA : TSAKANIN MUSULMI DA ' YAN SHIAH


SALLAR BANA: TSAKANIN MUSULMI DA 'YAN SHIAH A NAJERIYA!!!

Abin farin ciki ne ainun a wad'annan lakuta ganin yadda kan al'ummar Musulmi a Najeriya ya had'u dangane da batun d'auka da kuma aje Azumi. Hakan babbar nasara ce, kuma alamu ne da suke nuna cin Nasara, domin, a baya mun shaida yadda aka dinga samun sab'ani wajen ganin watan Ramadan da kuma na Shawwal. Inda hukumomi zasu bayar da sanarwa amma wasu su k'ek'asa su ce basu yadda ba, sai sun gani da idonsa,  dan kawai haifar da sab'ani tsakanin Musulmi.

Cikin hukuntawarsa Subhanahu Wata'ala masu wancan ra'ayi sun fara dawowa daga rakiyarsa, inda wannan lokuta ake kara tsuke bakin sab'anin baki daya. Musulmi a kusan gaba d'ayan Najeriya sun d'auki Azumi tare sun kuma yi Sallah tare. Ko Shakka babu wannan zai baiwa Musulmin Najeriya karfi na tunkarar manyan abokan gaba wato SHIAH.

Da yake su mabiya addinin Shiah kullum burinsu shi ne a samu sab'ani tsakanin al'ummar Musulmi,  da burin Kada kai ya had'u. Hakan ta sanya suke kokarin ganin sun tabbatar da sab'anin sun d'auki Azumi daban sun kuma yi Sallarsu daban, sab'anin Musulmi da suka bi Umarnin mai alfarma Sarkin Musulmi Sultan Saad wajen dauka da kuma aje Azumi.  

A har kullum abinda ya kamata mutane su gane kuma su fahimta shi ne cewar, babu wad'an da suke kokarin kawo rarrabuwa ko wargaza zaman lafiya tsakanin al'ummar Musulmi kamar 'yan Shiah. Shugabansu kuma jagoransu Ibrahim El Zakzany shi ne kullum yake ihu da karad'in cewa "HADIN KAI"  amma gashi zahirin sa ya nuna tacacce mayaudari  ne, kullum yaudarar mabiyansa yake da sunan had'in kai, amma kuma ga shi a zahiri yana k'ok'arin tabbatar da samun b'araka da rarrabuwa. 

Daman kuma mun kwana da sanin kokarin cusa rarrabuwa tsakanin Musulmi shi ne abinda 'yan Shia suke ta fatan ganin dorewarsa a kowacce irin al'umma. In sha Allah kuma ba zasu Ci Nasara ba, kamar yadda aka samu wannan had'in kai na al'ummar Musulmin Najeriya, haka za'a  cigaba da samu. Allah ka kara tabbatar da had'in kai tsakanin Musulmi. Ya Allah duk wadan da suke kokarin ganin bayan Musulunci da Musulmi Allah kaga bayansu,  Allah ka bak'anta musu rai da ganin cigaban Musulunci.

Muna addu'ah da sunayan Allah tsarkaka madaukaka Ya Allah ka nesanta mu da zurriyar mu daga Shianci. Allah ka fahimtar da mu addinin Musulunci,  Allah ka bamu lafiya da zaman lafiya. Ya Allah Kada ka baiwa 'yan Shiah nasara a cikin dukkan lamuransu duniya da Lahira. Allah ka taimaki Musulunci da Musulmi.

YASIR RAMADAN GWALE​
18-07-2015

Thursday, July 16, 2015

Ganin Wata



GANIN WATA: Ma'aikatar harkokin addinin Musulunci a Sa'udiyya sun bayar da sanarwa a hukumance cewar a yau alhamis 29 ga Ramadan aka ga Jinjirin watan Shawwal, wanda hakan ke nuna kawo karshen kwanaki Ashirin da tara na watan Ramadan. Dan haka a gobe Juma'a zai zama daya ga watan Sallah In sha Allah.

Labari MARAR Dadi Daga Gombe


LABARI MARAR DADI DAGA GOMBE 

A daidai lokacin da al'umma ke fara shirin Sallah karama a gobe a duk fadin duniya, muka samu mummunan labarin harin Bom da aka kai tsakiyar kasuwa a Jihar Gombe! Wannan babban abin bakinciki ne da takaici ainun, abin akwai Kada zukata a yayin da al'umma ke d'oki da ganin anyi Sallah lafiya, wasu miyagun azzalumai mabiya Tafarkin shedan suke ta kokarin kawo karshen rayuwar mutanan da basu ji ba basu gani ba ta irin wannan mummunar hanya. Allah ya jikan wadan da suka rasu, muna mika ja je da ta'aziyar mu ga Gwamnatin Jihar Gombe da al'Umar jihar baki daya. Allah ka kawo mana karshen wannan tashin hankali da ya addabemu.  

Yasir Ramadan Gwale 
16-07-2015

Tuesday, July 14, 2015

Yakar Boko Haram


YAKAR BOKO HARAM
Babbar matsalar da ta addabi mutanan Nigeria ita ce wannan fitinar ta Boko Haram, har ma da kasashe ma'kwabtan Najeriya. Shi mai aikata laifi musamman irin na ta'addani irin na Boko Haram dabaru gareshi iri iri, a lokacin da jami'an tsaro ko Gwamnati ke k'ara shirin tunkarar wannan Ya'ki gadan gadan, suma a nasu bangaren 'yan Boko Haram ba wai kawai zaune suke suna jiran mutuwa ba.
Kamar yadda bayanai suka nuna cewar itama Boko Haram a yanzu kara shiri suke, domin had'akarsu da k'ungiyar ISIS babbar barazana ce ba ga Nigeria kad'ai ba har da ma'kwabtanmu. Alhamdulillah a yau abinda aka jima ana jira ya tabbata, na sauya jama'an tsaron da PMB ya gada daga Gwamnatin da ta shud'e. Wad'annan sabbin nad'e nad'e da akai an ce galibinsu sun fito daga yankin Arewa Maso Gabas, wanda fatanmu shi ne Allah ya basu ikon murkushe Boko Haram da karfin Allah.
Ba shakka, idan akwai abinda ya kamata mu dage da adduah akansa bai wuce samun zaman lafiya a Najeriya ba. Muna fatan Allah ya baiwa wad'annan jagorori Nasarar dirkake Boko Haram, Allah ka azurtamu da samun zaman lafiya mai d'orewa a kasarmu. Ya Allah Kada ka baiwa 'yan ta'adda nasara komai kaskantar ta. Allah ka baiwa sojojin Najeriya nasara akan wannan Yaki.
Yasir Ramadan Gwale
13-07-2015

Monday, July 13, 2015

Nuhu Ribadu Na iya Zama Sabon Shugaban PDP NA Kasa



MALAM NUHU RIBADU NA IYA ZAMA SHUGABAN PDP NA KASA
Jaridar Leadership Newspapers ta ruwaito cewar tsohon Shugaban hukumar EFCC kuma tsohon dan takarar Shugaban kasa a Rusasshiyar Jam'in yar ACN Malam Nuhu Ribadu na iya zama sabon Shugaban jam'iyyar PDP na kasa nan gaba a babban taron PDP na kasa da zai gudana.
Ba shakka wannan labari ne mai faranta rai, samun mutum irin Nuhu Ribadu a matsayin shugaba zai baiwa PDP damar yaki da cin hanci da rashawa a cikin jam'iyyar, wanda hakan zai bayar da damar samun nagartattun 'yan takara wadan da basu ci amanar kasa ba. Allah ya taimaki Nuhu Ribadu a wannan sabon mukami da zai samu, Allah kai masa jagoranci ka bashi ikon kawo sauye sauye masu alfanu ga rayuwar al'umma.
13-07-2015

Saturday, July 11, 2015

SA'UDIYYA : Sarki Salman Bin Abdulaziz Ya Jagoranci kaddamar da aikin fadada Masallacin Haramin Makkah Da Zai Kunshi Masallata Miliyan Biyu Ba Dubu Maitan


SARKI SALMAN YA K'ADDAMAR DA AIKIN FADADA HARAMIN MAKKAH DA ZAI KUNSHI  MASALLATA MILIYAN BIYU BA DUBU MAITAN 

Ranar Asabar 12 ga watan Yuli bayan da ya sha ruwa a Makkah, Sarki Salman Bin Abdulaziz ya jagoranci kaddamar da aikin fadada Masallacin Haramin Makkah da zai kunshi Masallata Miliyan biyu ba Maitan. Sarkin ya bayyana cewar wannan aikin shi ne zai bayar da damar gagarumin aikin fadada Masallacin da zai kunshi Masallatai Miliyan biyar nan da shekaru goma masu zuwa.

Da yake jawabi a wajen taron Babban Limamin Haram Sheikh Abdurahman as-Sudais (Imam of Masjid alHaraam, Makkah)​ ya bayyana cewa wannan shi ne katafaren aikin fada da Masallacin ka'aba da ba'a taba yin sa ba. Kuma shi ne, na uku a cikin manyan ayyukan fada da Masallacin tun bayan wanda  Sarki Fahad da Abdullah suka yi. Sheikh Sudais ya yabawa Sarki Salman akan wannan aiki tare da yi masa adduar fatan alheri akan kulawar da yake baiwa Masjid al-Haram​, sannan ya kara da cewa kamar yadda kasar Saudi Arabia​ ke kan tsarin Sunnah, ya sha alwashin ci gaba da tafiyar da Masallacin a bisa tsarin Sunnah.


A nasa jawabin Sarkin Kuwait Sheikh Sabah Ahmad Al-Sabah ya gode wa Sarki Salman da kuma Masarautar Sauin a bisa irin wannan kulawa da suke baiwa Haramain dake Makkah da Madina. Sarakunan Bahrain da Dubai​ duk sun aiko da sakon fatan alheri ga Sarki Salman akan wannan katafaren aiki.

YASIR RAMADAN GWALE​
12-07-2015

Wednesday, July 8, 2015

Muna Cikin Gagarumar Matsala


 MUNA CIKIN GAGARUMAR MATSALA 

Yana daga cikin dalilin aukawarmu cikin wannan mugun hali na tashin hankali da zaman dar-dar, da rashin kwanciyar hankali, shi ne wata gurbatacciyar fatawa da aka yada a tsakanin al'umma cewar karatun Boko da aikin Gwamnati da dangoginsa duk Haramun ne. Hakan ta sanya masu irin waccan fatawa a yanzu suka rikide suka koma KHAWARIJAWA suna ganin kowa bai fahimci addini ba sai su, kuma kowa akan bata yake sai sune kadai akan daidai.

Hakan na faruwa ne  irin yadda wasu kawai dan sun karanta addini basu fahimci komai a cikin abubuwan da suka shafi hukunce-hukuncensa ba (addini ba), kawai sai su fara yiwa al'muma fatawa babu gaira babu dalili. Domin haka siddan Yusuf ya zo cikin tsukakken tunaninsa da gajeren iliminsa, ya dauka cewar shima ya kai wani munzali da zai dinga tara al'mma yana yi musu fatawa. Aka wayi gari suna Halatta Haram suna kuma Haramta Halal. 

Irin hakan ce ta janyo, rana tsaka aka wayi gari suna baiwa mabiyansu fatawar cewar karatun Boko kafurci ne, har hakan ya kaimu ga wannan mawuywcin lokaci da ake cewa Boko Haram. Aka dinga yiwa bayin Allah fatawa cikin jahilci da daskararren tunani da rarraunan hange, aka dinga sanya wasu suka dinga yaga takardunsu, sabida ance musu bai halarta ba a Musulunce.

Wannan kamar wani 'yanci ne, da kusan duk wanda yake jin ya karanta ilimin addini, kawai zai dinga yin FATAWA akan dukkan abinda yaga dama ko duk tambayar da akai masa, ba tare da tunanin matsalar da wannan Fatawa tasa zata janyo ba. Malamai sun sha gaya mana, cewar magabata har gudu suke ana binsu ana rokonsu Allah akan su zo su yiwa al'umma Fatawa.

Amma yanzu muna cikin wani zamani da kowa yana jin cewar shi Malami ne, ya karanta addini yasan addini. Malaman da suka karantar da shi gani yake sunyi kafada da juna, dan haka muka wayi  gari kowa me fatawa ne, kuma kowa me Tafsiri ne musamman a wannan wata na Ramadan.  Da yawa suna nan suna baiwa al'umma fatawa cikin jahilci da rashin sani, wannan ta sanya sai kai ta ganin mutane na yin kwan-gaba kwan-baya, yau mutum yayi Fatawa gobe ya warware ta, ko kuma jibi yace ai fahimtarsa ne ba'ayi ba.

Shi Musulunci addini ne mai tsari ba addini ne da kowa zai kutsa kai cikin komai yana ganin kansa shi wani Mutafannini  ne a cikinsa ba. Lallai yana da kyau mutane su ji tsoron Allah, su dena sanya al'umma cikin halaka ta hanyar yi musu gurbatacciyar fatawa wadda babu abinda yake cikinta sai tsabagen yarinta da shirme da kuma san nuna isa.

Allah ya jikan Malam Jaafar Adam Kano da Malam Abubakar Hussaini Fagge, Allah ya gafarta musu. An sha yiwa Malam Jafar tambaya, amma sai ya bugawa Malam Abubakar Hussein Fagge waya yaji abinda zai ce, duk kuwa da Allah ya baiwa Malam Jaafar daukaka da shahara, sama da ta Malam Abubakar Hussain, amma sabida kiyaye amana ta Ilimi, Malamai suke yin kokarin maida komai zuwa ga asalin sa,  dan kare al'umma daga fadawa muguwar fatawa.

Haka nan,  Sheikh Albans Zaria Allah ya jikan sa, na taba ji yana fada cewar, abin yana bashi mamaki mutum yana Kano ko Katsina ya buga masa waya yana tambayarsa Fatawa, yakan gayawa masu irin wannan, cewar shin a garin ku babu Malaman Sunnah da zasu iya yin wannan fatawa sai ni ko kuwa jin baki ne. To haka ne, Malamai na Allah suke kiyaye amana ta Ilimi. 

Dan haka  yana da kyau mutane su kiyaye kansu daga fadawa hannun fatawar irin wadannan da suka dora al'umma kan karkatacciyar fatawar cewar karatun Boko da dangoginsa b'ata ne kuma kafurci ne. Lallai yana daga cikin ayyukan da ya kamata Manyan Malamai su maida hankali akai na dakile yaduwar irin wannan fatawoyi barkatai da wasu dalibai masu feleke da iya yi suke yi. Ya Allah ka nuna mana gaskiya, mu fahimci gaskiya ce ka bamu ikon binta; ka nuna mana karya mu fahimci karya ce ka bamu ikon kauce mata. 

Yasir Ramadan Gwale 
08-07-2015

Sunday, July 5, 2015

Gwamnatin Kano Ta Bar Farilla Ta Kama Yin Nafila


GWAMNATIN KANO TA BAR FARILLA TA KAMA YIN NAFILA 

Gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin sabon Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje ta bayar da Umarnin rufe dukkan makarantun Gwamnati na Firamare da Sakandare a fadin Jihar Kano ba tare da an kai karshen zango na uku na karatu ba. Duk da cewar a tsarin kalandar karatu ta wannan Shekarar 2015, zango na uku (third term) zai zo karshe ne a ranar 10 ga watan Yulin nan.

Babban abinda da ya zo da mamaki shi ne yadda makarantu masu zaman kansu a fadin Jihar Kano suke cigaba  da aiki yayin da na Gwamnati suke a garkame, wannan ne ya ja hankalin wata kungiyar mai kwarmato bayanai ta duniya ta Kwarmato wannan batu, Sanusi Bature Dawakintofa​ shi ne wanda ya sanya hannu a madadin kungiyar.

Sakamakon bincike ya nuna cewar sabuwar Gwamnatin Kano, wai ba zata iya ciyar da daliban sakanadare dake makarantun kwana ba a fadin Kano baki daya a cikin wannan wata na Ramadan mai dumbin falala, sannan suma daliban Firamare da ake ciyar da su sau daya, suma Gwamnati ba zata iya ciyar da su ba, dan haka ne ya sanya Gwamnatin  daukar matakin kulle makarantun sabida karanci kudi.

Wannan babban abin mamaki ne da kuma takaici duba da yadda Gwamnatin ta ware Miliyoyin kudi domin rabawa mutane akan titi koko da kosai a wannan watan na Azumi, wanda wannan Farilla ne ba wajibi ba ne a gareta, amma ta saki wadan da suke Farali ne a gareta ta kama yin aikin Nafila. Misalin hakan, kamar mutum ne Yaki yin Sallar Isha ya kama yin Sallar Asham da zaton watakila Asham din tafi Lada.

Ko Shakka babu wannan abu da Gwamnatin Kano tayi tozarta Ilimi ne. Ta yaya za'a rufe makarantun Gwamnati wadan da 'ya 'yan  Talakawa suke karatu a yayin da makarantu masu zaman kansu da masu karfi kan iya kai 'ya 'yansu su kasance a Bude.  Wannan ko Shakka babu, durkusar da ilimi ne, da dakushe karatun 'ya 'yan talakawa. Hakan kuma, na bayyanawa duniya irin yadda wannan sabuwar Gwamnatin ta Kano sam bata damu da karatun yaran Talakawa ba.

Dan haka lallai muna kiran sabuwar Gwamnatin Kano ta mayar da dalibai makaranta, ko kuma a dakatar da karatun makarantu masu zaman kansu, alabashshi a tafi tare. Idan ba haka ba kuwa, an yiwa karatun yara mummunar illah a Jihar Kano. Kuma irin wannan ne, ke sabbaba mummunar faduwar jarabawar 'yan sakanadare ta WEAR da NECO. 

YASIR RAMADAN GWALE​
05-07-2015

Saturday, July 4, 2015

Fahimtar Matsalar Boko Haram


BOKO HARAM: Da yawan mutane an gurbata tunaninsu an yi Nasarar amfani da farfaganda ta karya akan Boko Haram akansu, mutane sun dimauce sun gaza gane hakikanin lamura sai bagauniya suke sun kasa gane me ke faruwa. Wasu da dama tunaninsu yana basu cewar idan an jingina aikin ta'addanci zuwa ga 'yan ta'adda da suke yi sa,  sai tsukakken tunaninsu ya basu cewar ai duk kokari ne na tsarkaka Goodluck Jonathan​, amma duk zargi da farfagandar masu farfaganda ba zai sanya karya ta zama gaskiya ba. 

Ka kan fahimci jahilci mutane karara a lokacin da suke nesanta Musulmi daga aikata ta'addanci irin na Boko Haram, wasu a zatonsu babu yadda za ai Musulmi ya iya kashe Musulmi, da yake basu san tarihi ba, kuma basu san su waye Khawarij ba a cikin Musulunci, sannan sun manta su waye suka kashe Sayyaduna Usman Bin Affan. 

Ko dai mu yadda mu aminta cewar wadan da suke wannan ta'addanci Musulmi ne 'yan uwanmu da suka kauce hanya da gangan ko da ganganci,  ko kuma mu cigaba da zargin wasu daga can nesa muna ji muna gani al'umma daruruwa suna rasa rayukan su a lokaci guda, zargin da muke babu abin da zai haifar sai bakinciki da takaici.

Muna yiwa Gwamnati da sojojin mu addu'ar fatan alheri da fatan samun nasara akan wannan Yaki da suke da wadannan miyagun Azzaluman 'yan ta'adda marasa tsoron Allah.

Yasir Ramadan Gwale 
04-07-2015

Fahimtar Matsalar Boko Haram


BOKO HARAM: Da yawan mutane an gurbata tunaninsu an yi Nasarar amfani da farfaganda ta karya akan Boko Haram akansu, mutane sun dimauce sun gaza gane hakikanin lamura sai bagauniya suke sun kasa gane me ke faruwa. Wasu da dama tunaninsu yana basu cewar idan an jingina aikin ta'addanci zuwa ga 'yan ta'adda da suke yi sa,  sai tsukakken tunaninsu ya basu cewar ai duk kokari ne na tsarkaka Goodluck Jonathan​, amma duk zargi da farfagandar masu farfaganda ba zai sanya karya ta zama gaskiya ba. 

Ka kan fahimci jahilci mutane karara a lokacin da suke nesanta Musulmi daga aikata ta'addanci irin na Boko Haram, wasu a zatonsu babu yadda za ai Musulmi ya iya kashe Musulmi, da yake basu san tarihi ba, kuma basu san su waye Khawarij ba a cikin Musulunci, sannan sun manta su waye suka kashe Sayyaduna Usman Bin Affan. 

Ko dai mu yadda mu aminta cewar wadan da suke wannan ta'addanci Musulmi ne 'yan uwanmu da suka kauce hanya da gangan ko da ganganci,  ko kuma mu cigaba da zargin wasu daga can nesa muna ji muna gani al'umma daruruwa suna rasa rayukan su a lokaci guda, zargin da muke babu abin da zai haifar sai bakinciki da takaici.

Muna yiwa Gwamnati da sojojin mu addu'ar fatan alheri da fatan samun nasara akan wannan Yaki da suke da wadannan miyagun Azzaluman 'yan ta'adda marasa tsoron Allah.

Yasir Ramadan Gwale 
04-07-2015

Fahimtar Matsalar Boko Haram


BOKO HARAM: Da yawan mutane an gurbata tunaninsu an yi Nasarar amfani da farfaganda ta karya akan Boko Haram akansu, mutane sun dimauce sun gaza gane hakikanin lamura sai bagauniya suke sun kasa gane me ke faruwa. Wasu da dama tunaninsu yana basu cewar idan an jingina aikin ta'addanci zuwa ga 'yan ta'adda da suke yi sa,  sai tsukakken tunaninsu ya basu cewar ai duk kokari ne na tsarkaka Goodluck Jonathan​, amma duk zargi da farfagandar masu farfaganda ba zai sanya karya ta zama gaskiya ba. 

Ka kan fahimci jahilci mutane karara a lokacin da suke nesanta Musulmi daga aikata ta'addanci irin na Boko Haram, wasu a zatonsu babu yadda za ai Musulmi ya iya kashe Musulmi, da yake basu san tarihi ba, kuma basu san su waye Khawarij ba a cikin Musulunci, sannan sun manta su waye suka kashe Sayyaduna Usman Bin Affan. 

Ko dai mu yadda mu aminta cewar wadan da suke wannan ta'addanci Musulmi ne 'yan uwanmu da suka kauce hanya da gangan ko da ganganci,  ko kuma mu cigaba da zargin wasu daga can nesa muna ji muna gani al'umma daruruwa suna rasa rayukan su a lokaci guda, zargin da muke babu abin da zai haifar sai bakinciki da takaici.

Muna yiwa Gwamnati da sojojin mu addu'ar fatan alheri da fatan samun nasara akan wannan Yaki da suke da wadannan miyagun Azzaluman 'yan ta'adda marasa tsoron Allah.

Yasir Ramadan Gwale 
04-07-2015

Friday, July 3, 2015

Hadisin Abacha


HADISIN ABACHA 

An ruwaito wani hadisi daga tsohon Shugaban Kasa Marigayi Sani Abacha, wanda aka ce 'yarsa Gumsu ce ta ruwaito daga mahaifin nata, cewar "duk wani rikici da ya haura sa'o'i 24 Gwamnati batai maganinsa ba to akwai alamar tambaya akanta". Gaskiya ban san Inganci Isnadin wannan hadisi ba. Amma dai babu shakka a baya zamanin shudaddiyar Gwamnatin Goodluck Jonathan an bayar da fatawa sosai da hadisin kuma mutane da yawa sun yi ammana da wannan fatawa.

Shin tsakani da Allah har yanzu mutane suna da tunanin cewar babu wasu Boko Haram Gwamnati ce da ta shude ke iya-shegenta da sunan Boko Haram, ko kuwa da dama sun dawo daga rakiyar waccan fatawa ta Hadisin Gumsu? 

Yana da kyau mu fahimci gaskiya dangane da Boko Haram, sannan mu gayawa kanmu gaskiya. Shin mutanan da aka kashe jiya a Masallaci a Borno suna Sallah su waye suka kashe su? Shin har yanzu muna kore hannun Boko Haram akan irin wannan ta'annati da tunanin cewar Musulmi ba zai iya kashe Musulmi ba? Duk inda za'a je a dawo sai an komawa gaskiya idan ana san gaskiya.

YASIR RAMADAN GWALE
03-07-2015

Sanata Muhammad Ibn Rabiu Ibn Musa Alkwankwasy: CIKI DA Gaskiya . . .


SANATA MUHAMMAD IBN RABIU IBN MUSA AL-KWANKWASY: CIKI DA GASKIYA .  . .

Tun bayan da Rabi'u Kwankwaso ya zama Gwamnan Jihar Kano a 2011 bayanai sukai ta fitowa daga Gwamnatin  da Kwankwaso ke Jagoranta cewar tsohon Gwamna Malam Ibrahim Shekarau ya saci kudi masu dumbin yawa a zamanin mulkinsa na shekaru takwas, Gwamnatin Kwankwaso ta yi ta karad'i akan wannan batu, aka kasa nuna daidai inda Malam Shekarau yayi almundahana.

Mai magana da yawun tsohon Gwamna Malam Ibrahim Shekarau wato Malam Sule Yau Sule ya nemi da cewar Gwamnatin Kwankwaso ta gurfanar da Malam Ibrahim Shekarau a gaban hukumar EFCC ko a kai shi kotu dan ya gurfana, amma karshe sai muka ji Gwamna Kwankwaso na cewar sun bar Malam Shekarau  da Allah. Wanda wannan ba komai ya nuna ba sai tsabar bita da k'ulli  da Hassada da akaiwa Malam Ibrahim Shekarau.

Domin indai gaskiya ake so kuma gyara aka zo da niyyar yi bai kamata a bari Malam Shekarau ya sha da kud'in al'umma ba, indai da gaske ne Gwamnatin Rabiu Musa Kwankwaso tana da masaniyar cewar Malam Shekarau ya kwashi kud'in al'umma ba bisa ka'Ida ba kuma aka barshi ya sha da kud'in jama’a to ba shakka Kwankwaso ya cuci mutanan Kano.

Kullum abinda muke kira shi ne cewar Gwamnati ta jama’a ce, kuma domin jama'a ake yinta,  dan haka babu yadda mutum zai yi Gwamnati ya kwashi kudin jama’a sannan a bar shi ya sha, ace masa je ka ka gani, ai ya gani tun anan! lallai ko waye a kamo shi ya dawo da hakkin jama’a tunda ba gadon gidan su bane.

Gwamnatin Kwankwas tayi ta maganganu na batanci akan Malam Shekarau da nuna cewar yana yiwa ma'aikatan Gwamnati da suka ci dukiyar al'umma Allah ya isa, amma suka kasa kasa nuna wadan da Malam din ya yiwa Allah ya isa, karshe suka b'ige da yiwa Malamin Allah ya isa.

Yau cikin ikon Allah gashi Gwamna Kwankwaso kuma sabon Sanatan Kano ta tsakiya yabar Gwamna amma yana ta guje guje da lab'e lab'e Kada a kama shi a bincike shi, tir kashi! Indai cikin Kwankwaso da gaskiya, kamata yayi ya kai kansa EFCC dan a wanke shi daga zargin da ake masa na almundahana da kudin tsaffin ma'aikatan Gwamnati na fansho. 

Gwamnan Jigawa Malam Sule Lamido da yasan cewar cikinsa da gaskiya babu wata wuk'ar EFCC  da zata huda shi, shi da kansa ya kai akansa ofishin EFCC  din kuma aka bincike shi dan tabbatar yayi sama da fad'I ko bai yi ba, babu ko Shakka Malam Sule Lamido ya nuna jarumataka da kuma nunawa duniya cewar shi ba b'arawo bane.

Dan haka abinda muke Fata ga Sanatan Kano ta tsakiya kuma tsohon Gwamnan Kano Muhammad Ibn Rabiu Ibn Musa Kwankwaso ya yiwa Allah ya kai kansa EFCC domin a wanke shi daga dukkan zarge zargen da ake masa na wawure dukiyar al'umma. Wannan kuma babu abinda zai rage na daga ayyukan da Kwankwason yayi, domin su wadan da suka shigar da karar Kwankwaso a EFCC basu yi hakan dan nuna cewar bai yi aiki ba, illa suna ganin anyi zarmiya da dukiyarsu. 

Wannan abin da ya faru ya kara nuna mana hikimar Allah Subhanahu Wata'ala da bai sa Malam Salihu Sagir Takai ya samu Nasarar zama Gwamnan Kano ba a wannan lokacin, domin watakila da a karkashin Gwamnatin Malam Salihu  Sanata Kwankwaso ke wannan b'oye b'oye al'umma ba zata tab'a yarda cewar ba bita da k'ulli ake masa ba, sai gashi karkashin Gwamnatin Gwamna Gandujen Kwankwasiyya wannan abu ya bijiro.

Mu fatanmu shi ne hukumar EFCC ta yi bincike tun daga 1999 zangon farko na Gwamnatin Kwankwaso  da kuma zango biyu na Malam Ibrahim Shekarau  a cikinsu duk wanda ya dauki dukiyar al'umma ba bisa ka'Ida ba ya dawo da ita kuma ayi masa hukunci daidai da abinda ya aikata,  domin wannan shi ne gatan da za ai musu anan duniya, domin a Lahira akwai Shari'ah ta gaskiya da babu EFCC da ICPC babu Lauyoyi. 

Yasir Ramadan Gwale
02-07-2015