Saturday, May 19, 2012

Saudi-Bahrain: Karyar Iran ta kare!

Saudi-Bahrain: Karyar Iran ta kare!

A ranar sha hudu ga watan mayun wannan shekara ne (14th May, 2012) kungiyar kasashen Gulf Cooperation Council (GCC) wadan da suka hada da kasar Saudiyya da Bahrain da Hadaddiyar Daular Larabawa da Kuwait da Oman da kuma kasar Qatar, suka bada shelar da ta ke nuna hadewar kasar Saudiyya da Bahrain, a matsayin kasa guda mai bin tafarkin mulkin Sarauta karkashin Larabawa sunni. Hakika wannan hadewa muhimmin al'amari ne ga samun zaman lafiyar kasashen yankin Gulf. Hadewar dai tazo ne a yayin da aka samu akalla shekara guda 'yan shi'ah masu samun goyon baya daga Iran da Hizbolla ke ta kokarin yin juyin juya halin da zai kai ga kifar da gwamnatin Sheikh Hamad Bin Issa Alkhalifa a kasar ta Bahrain. Da farko dai sun fara ne da neman kawo sauyi a bisa yadda ake tafiyar da mulkin kasar, inda masarautar kasar ta bayyana gudanar da wasu sauye sauye da zasu baiyawa majalisar kasar dama mai yawa a cikin kundin tsarin mulkin kasar.

Ita dai kasar Bahrain, kusan za a iya cewa wani tsibiri ne da ya ware kadan daga cikin kasashen larabawa, kasar tana gab da kasar Saudiyya. ita dai wannan kasa ta Bahraina ta samu ne a shekarar 1783, lokacin da musulmi Ahlussunnah karkashin Gidan sarautar Alkhalifa suka fatattaki 'yan shi'ar Farisa. inda suka kafa daula mai bin tafarkin Sunni. Tun wancan lokacin ne kasar Farisa wadda ake kira Iran a yanzu take ta hakilon ganin cewar kasar Bahrain ta komo karkashin Daular Shi'ah, kasan cewar Bahrain ita ce kadai daga cikin kasashen larabawa da ta ke da mabiya addinin Shi'ah masu yawa. Kamar yadda muka sani kasar Iran kusan itace kasar da tafi kowacce kasa kusanci da kasashen larabawa bayan kuma ita ba kasar Larabawa bace, don haka kullin tunaninsu shi ne ya zasuyi su kwato kasar bahrain daga hannun gidan Sarautar Alkhalifa. Da kuma kokarin kawo tarzoma a daukacin kasashen larabawa, wanda suke gani wata dama ce a garesu ta su shiga su yada addinin Shi'a ga larabawa musulmi.

Tun bayan bore tare da zanga-zangar kasashen larabawa da ta samo asali daga Tunisiya, inda talakawa sukaci nasarar hambarar da gwamnatin zalunci ta Zainul Abedeen Ben Ali, abin ya rika yaduwa tare da goyon bayan munafukar kasar Iran da kuma 'yan Shi'ar Lebanon. haka abin ya ci gaba da yaduwa har ya isa kasar Masar wadda ita ce mafi kusanci da kasashen Turai da Amerika, inda suma talakawa sukaci nasarar hambarar da Shugaba Hony Mubarack duk kuwa da barazanar da ya ringayi musu, haka dai wannan guguwa ta yi ta kadawa a tsakanin kasashen larabawa, kuma itace tayi sanadiyar tafiyar Shugaba Ali Abdallah Saleh na Yemen da kuma kisan da akayiwa Shugaba Mu'ammar Ghaddafi na libya.

Haka dai wannan zanga-zanga ta cigaba da ruruwa har ta isa kasar Siriya, inda anan ne tafi yin muni ainun sama da kowacce kasa da akayi wannan zanga-zanga. Hakika gwamnatin Shugaba Bashar Assad ta yi amfani da wannan dama inda tayi ta kisan musulmi mabiya sunnah wadan da su ne suke da rinjaye a wannan kasa ta Siriya, anruwaito sosjoin gwamnatin Assad suna kai muna nan hare-hare akan garuruwan musulmi mabiya sunnah wadan da suka hada da Homs da Dar'a da Hama da Idlib da Aleppo da sauransu bayan kuma an yanke musu wutar lantarki da ruwan famfo, harkokin kasuwanci sun durkushe gabikidaya a wadan nan yankuna, duk kuwa wannan na faruwa ne da goyon bayan da Assad yake samu a fakaice daga kasar Iran da kuma kungiyar Hezbollah dake kasar Lebanon, kasancewarsa Dan Shi'a Alawiyyi, a gefe guda kuma shi Assad din yana kara samun goyon baya daga kasashen Turai da Amerika da Chana da kuma Rasha, duk wannan saboda suna tsoron kada su bari Assad ya sullube a sami wani shugaba daga cikin musulmi Sunni wanda zai kasance mai kishin addinin musulunci, wanda hakan zai kai ga tayar da maganar tuddan Golan da kasar Israela ta mamaye wanda shi shi Bashar Assad da Mahaifinsa Hafeez Assad suka kauda kai wa Israela. Sai kayi mamakin duk irin kurarin da kasashen turai sukeyi akan hakkin dan Adam, Bashar Assad yana kashe mutanansa amma suna rarrashinsa.

Duk da cewa kasashen larabawa sun goyi bayan wakilin majalisar dinkin duniya Mista Kofi Anan akan ya je kasar Siriya ya tattauna yadda za'a sasanta rikicin siyasar kasar. Amma wannan babu abinda akeyi illah yawan shakatawa da taron shan shayi, domin duk irin manufofin da Kofi Anan ya je da su Assad ya sa kafa ya yi fatali da su amma kuma ana tausarsa da cewa ya yi hakuri, a zauna akan tebur a sulhunta. shakka babu abin nan ne da ake kira Interest ya yi yawa akan kasar Siriya shi ya sanya kasashen Turai da Amerika suke ta jan-kafa akan Assad duk wannan yana kara bayyana karara irin yadda sakatariyar harkokin wajen Amerika Hilary Hoadharm Clinton da kuma jakadiyar Amerika a majalisar dinkin duniya Suzan Rice suke ta yin amai suna lashewa akan wannan batu na kasar siriya, da kuma 'yancin dan Adam.

Idan har da gaske suke akan yadda suke lallabar Assad, me yasa basuyiwa marigayi Saddam Hussein Allah yajikansa irin wannan ba? ko kuwa kawai domin shi musulmi ne sunni, shakka babu wannan a bayyane take cewa Amerika da NATO sun afkawa Saddam Hussein saboda kasancewarsa Musulmi sunni, domin dukkan irin bayanan da mista Hatz Blick ya bayar sun nuna cewar Saddam ba shida wasu makamai masu hadari ko guba. A gefe guda kuma ana ta kokarin nunawa duniya cewa akwai baraka tsakanin Amerika da Iran, sanin kowane cewar da hadin bakin kasar Iran dari bisa dari aka yaki Saddam, kuma 'yan shi'a su Muktada Al-sadar da suke samun goyon baya daga Iran suka ci karensu babu babbaka duk da ana nuna cewa akwai tsamin alaka tsakaninsu da Amerika, koma dai meye Hausawa sunce shi munafurci dodo ne mai shi yake ci, don haka komai tsawon lokaci zai bayyana.

Idan kuma muka dawo batun kasar Bahrain, dole ne mu yabawa sarkin Qatar Sheikh Hamad Bin Jassim Althani da kuma shi kansa sarkin Bahrain Shiekh Hamad Bin Issa Alkhalifa da kuma Sarki Abdallah Bin Abdulazeez Ali-Saud na Saudiyya, hakika wannan namijin kokari ne sukayi na kokarin dinke barakar wannan yanki. kuma muna fatar watan wata rana a samu yanayin da zai kai ga kafa kasar larabawa kwaya daya (United State of Arabia), wadda muna sa ran ita zata kai ga kafa shugabancin musulmi guda daya a duniya, kuma muna nan muna fatan ganin kasar Iran ta komo karkashin Musulmi sunni, a kusa ko a nesa. domin sanin kowa ne cewa babu wata kasa a yanzu da take mafi hadari a duniya sama da kasar Iran, domin duk wani munafurci da fadi tashi da su akeyi, ya Allah ka wargaza aniyarsu ka rusa lamarinsu, ka hansu sakat.

kaicon tsufa, hakika Tsufa wata cuta ce da batada magani, kuma babu yadda dan Adam zai yi da rayuwa sai tsufa ya riskeshi, tsufa ya zowa Sarki Abdallah Bin AbdulAzeez Al-Sa'oud na Saudiyya a lokacin da duniyar Larabawa da ta musulmi suke da bukatar shawarwari da tunaninsa, da hange irin nasa, muna addu'a ga Khadumul Haramainissharifain, Allah ya kara masa lafiya da kwanciyar hankali, Allah ya sanya albarka acikin rauwarsa, hakika ya yi hidima ga dakin Allah mai alfarma da masallacin manzon Allah dake madina, Allah ya cika a mizaninsa, Allah ya jakwanansa. Muna kuma Addu'ar Allah ya yafe masa laifukansa wanda ya aikata bisa kuskure da wanda ya aikata bisa sani ko ajizanci. Allah ya taimaki Masarautar Sadiyya da Addinin Musulunci baki daya. ya Allah ka nuna mana ranar da za'a kawo karshen shi'ah a wannan duniyar.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com  

Saturday, May 12, 2012

Matasa a Jiya da Yau!


Matasa a Jiya da Yau!
Nagartaccen matashi shi ne ginshikin samar da kyakkyawar al'umma. Hakika dukkan al'ummar da take da dimbin matasa to tayiwa Allah godiya, domin wannan al'barka ta matasa itace take nuna cewa lallai za'a jima ana damawa da wannan al'umma a fagen rayuwa ta  nan gaba. Hakika matasa babu abin da suke da bukata kamar jagoranci da kokarin sanyasu bisa turba ta gaskiya, wadda zasu gina kansu domin gaba, kuma su sami zarafin gina al'ummar da suke rayuwa a cikinta.

Manazarta da masharhanta da dama sun wasa kwakwalwa wajen baje kolin tunani da bincike da ra'ayin shin wai waye matashi? Kamar yadda larabawa suke da wani Karin Magana inda suke cewa"ita jarumtaka ga matashi aka santa, idan ya kasance matashi babu jarumtaka, to sunansa wani abin" wannan Karin Magana ya nuna matukar iya zance na larabawa, shakka babu kyakkyawan matashi shi ne abin misali da kwatance, kuma jarumtaka tsakanin matasa wannan abin bukata ne kwarai da gaske.

 Hakika dukkan wani mutum da yayi sa'ar samun kansa a wannan sarari mai fadi da ake kira duniya, kuma yayi katarin dacen shige wannan yanayi ko lokaci na matashintaka kuma ya yi sa'a ya wuce lafiya to babu abinda ya kamaceshi illa ya yiwa Allah godiya, da kuma nazarin yadda za'a gina goben masu zuwa nan gaba.

Bari mu kalli matashi a shekarun baya: hakika a zamanin dacan matasa su ne suka bayar da gagarumar gudunmawa wajen dorewar wannan al'umma, hakika matasan da suka gabaci wannan al'umma tamu sun bayar da gagarumar gudunmawa wajen ganin mun sami ingataccen yanayin wanzuwa; misali ka dauki ganuwar birnin kano da zariya da kasar karaye da wasu garuruwa a Arewa da suke da ganuwa, ka tambayi kanka shin su wa suka gina wannan ganuwa? Mala'iku ne, al-janune, mutanan boye ne, turawan mulkin mallaka ne? shakka babu amsar wannan tambaya itace a'a matasan wannan al'umma da suka gabacemu su sukayi wannan katafaren aiki mai dumbin tarihi a lokuta masu tsawo da suka shude; ka zagaya birnin kano tundaga kofar Danagundi har kazagayo kofar Na'isa kaga yadda akayi gini babu ha'inci babu amaja, ka kuma lura da yadda ginin yake ka kuma tambayi kanka shin kasar da akayi wannan gini daga sama aka ringa zubo da ita ko kuwa ya abin yake, hakika wannan kasa kwakwularta aka ringayi daga kasa anayin bululluka da tubali har akayi wannan gini, duk wannan fa matasane sukayi, wannan misali kadan ne daga cikin irin misalign ayyukan da matasa wadan da suka gabaci wannan al'umma sukayi, kuma idan ana biyansu lada to bai taka kara ya karya ba; nasan watakila wani yace to ai bayi ne sukayi wannan gina ba 'ya 'ya ba, koma dai su wane sukayi lallai matasa ne, domin nayi imanin dattawa ko mata bazasu iya irin wannan namijin kokari ba.

Haka zalika mu sake komawa baya a tarihi, mu kalli irin yadda akeyin dalar gyada a kano da hadejiya kaga irin tarin buhunan gyada dubbai kure gani wanda duk matasa ne suka noma mafi yawanci, kuma a duke da fartanya ba kamar yanzu da ake da tarakta ba, inda mutum yana zaune akan mota yana bata umarni ba tare day a duka ba. Kuma suma wadan nan matasa da sukayi wannan noma, sunyi ba tare da samun wani lada na kuzo mu gani ba.
Hakika matasa a lokutan baya ba malalata bane idan mutum ya kalli wadan nan misalai guda biyu da muka bayar, matashi ne zakaji ance ya nome gonarsa da ta mahaifinsa da kuma ta surikinsa duk a damina daya ba tare da anbashi ladan ko sisi ba da sunan ladan hidima. Shakka babu tarihin wannan kasa bazai taba mancewa da irin gagarumar gudunmawar da matasa suka baiwa wannan kasaba a lokutan da suka gabata.

Sannan mu kalli matasa a wannan lokaci: shakka babu bazanyi kuskure ba idan nace matasan wannan al'umma a yanzu malalata ne na kin karawa, kowa ya nade hannun riga jira yake yaci ko ya samu ba tare da yasha wahalar ko kwabo ba, ka duba irin yadda Allah ya hore mana dimbin matasa ninkin ba nikin wadan da suka gabata, amma amfanuwar da akeyi dasu ko kusa bata kai amfanuwar da akayi da matasan da suka gabata ba; tambaya shin me ya jawo haka? Shin tarbiyya ce wadan nan matasa na yanzu basu samu ba daga magabatansu ba ko kuwa ya abin yake? Ka shiga cikin lungunanmu da sako da kwararo-kwararo kaga dimbin matasa 'yan bana bakwai majiya karfi suna zaune babu aikin fari balle na baki kawai suna zaune suna hira marar amfani a duniyance ko a lahirance, daga rana ta tarar da inuwa a sake daukar benci a maidashi inuwa, a cigaba da hira maras kan-gado.

Allah ya hore mana kasa mai fadi ba mai kwazazzabo da yawa ba, kuma bamai tuddai da yawa ba, kasar noma iya ganinka tundaga Kauran Namoda har katagum ka zarce har zuwa Nguru kasace mai fadi da za'a iya noma abinda zai iya cida kasarnan da makwabtanta, uwa uba kuma ga albarkar kasa da Allah ya bamu, mangwaro zaka sha ka yarda kwallon insha Allah idan ruwan damina ya dakeshi sai kaga yayi tsiro idan akayi sa'a babu abinda ya tabashi akwana a tashi sai kaga ya zama bishiya, duk wannan kadan ne daga cikin irin al'barkar da Allah ya yiwa wannan kasa.

Babu shakka kamar yadda na fada a farko, matasa sune kashin bayan kowace al'umma! Amma idan ya kasance matasan ba cima zaune bane kamar yadda muke a yanzu; abin mamaki kaga katon gardi yakai shekara 30 ko 35 amma wai har yanzu a gidansu ana bashi kudin batarwa, ba'a yi masa wani tanada da zai dogara da kansa ba, ballantana ya yi tunanin gina rayuwar manyan gobe.

Tun Ran Gini Tun Ran Zane: Allah ya albarkaci Bahaushe da iya Magana. A ganina dalilan da suke janyo matasa su zama masu mutuwar zuciya sune kamar haka:

Iyaye: Hakika, iya ye a wannan zamanin sun taka muhimmiyar rawa wajen ragwantar da 'ya 'yansu, domin zaka samu, musamman tsakanin iyaye maza da 'ya 'yansu babu wata alaka mai karfi, uba baya zama da 'ya 'yansa yana nuna musu yadda rayuwa take, ballantana ya basu irin tarihin gwagwarmayar da yasha a rayuwa ba, kalilan ne daga cikin iyaye suke zama da 'ya 'yansu suke nusar da su irin yadda rayuwa take. Tabbas da iyaye sun tsaya sun kula da tarbiyyar 'ya 'yansu maza da mata wajen nusantar dasu akan yadda zasu gina rayuwarsu a nan gaba da abin ba     haka yake ba.

Tsananin son 'ya 'ya: Hakika a wannan lokacin Allah ya jarrabi iyaye da yawa da tsananin son 'ya 'ya zakaga kowane uba baya son yaronsa ya sha wahala ko da kuwa wahalar alkhairi ce anan gaba, misali zakaga yaro tun yana karami irin yadda ake tarairayarsa da irin yadda duk sadda ya nemi abin batarwa a dauka a bashi ba tare da nuna masa cewa wannan abinda ake bashi sai ansha wahala ake samu ba, kai wasu iyayenma har kudi sukeyi canji wadan da zasu rika baiwa 'ya 'yansu duk safiya kafin su fita, idan kuwa akayi sa'a wani uban yana da dan abin hawa sai kaji wai kullum sai ya dana yaransa kafin ya fita, duk wannan yana daya daga abinda ya janyowa matasan wannan al'umma lalaci.

Halin ko inkula daga makwabta: A bayyane yake cewa yanzu makotaka ta dauki wani irin mummunan salo, ta yadda zakaga makwabci babu ruwansa da ladabtar da dan makwabcinsa don gudun kada ran mahaifin yaron ko mahaifiyarsa su baci, abin mamaki idan makwabci ya daki dan makwabcinsa sai kaji uwar yaron ta aiko "wai me wane ya yi aka dake shi" da yawan wannan takan sanya da yawa daga cikin makwabta ko inkula da duk wani abu da yaro zaiyi matukar ba dansu bane; ada yadda muka sani mutum daya zai iya yiwa yaran unguwa ladabi kuma kaji iyayensu suna godiya, ba tare da bin bahasin abinda yaro ya yi aka dokeshi ba.

'Yan Siyasa: Ina fatar kana biye da ni sau da kafa ya dan uwa mai karatu, kamar yadda nace 'yansiyasa sun samu galibin matasa suna da son jiki da rashin son wahala da kuma tsananin son kudi da son hutu, shi yasa yanzu zakaga kansiloli da 'yan majalisu na jiha dana tarayya da shugabannin kananan hukumomi suna yawan kafa rumfuna a mazabunsu da kuma yin odar sabbin bencina domin duk a cigaba da kashewa matasa zuciya da sage musu gwiwar amfanar lokacinsu na kuruciya, ba karatu ba sallah, sai yawan zagi da gulma da kinibibi, idan wani ya wuce da sabuwar riga ace ya cika girman kai, idan kuwa akaga mai sabuwar mota ace masa barawon gwamnati suna zaune babu abinda suke har maraice ya riskesu. Kaga 'yan siyasa sunyi amfani da lalacin da iyaye suka sanyawa 'ya 'yansu suka sake lafkarda su.
A ganina wadan nan da ma wasu suna daga cikin dalilan da suka sanya matasan wannan al'umma suke cikin halin da suke ciki na lalaci da son jiki da mutuwar zuciya. Lallai ne idan muna son gyara sai mun koma baya munga me ya gyara al'ummar farko har ta kasance abin misali yanzu a garemu sannan zamu sami hanyar da zamu gyara halin da muke ciki, duk kuwa da dimbin ilimin da ake dashi wanda ya ninka na dacan ninkin banikim.

Lallai lokaci ya yi da zamuyi tunanin fitar da kawunanmu daga cikin wannan mummunan kangi na lalaci da mutuwar zuciya da ko inkula da tsananin son 'ya 'ya da baya amfana musu da komai sai da na sani a gaba, kuma wannan hali shi ne ya haifarmana da karuwar mugun talauci, ta yadda munaji muna kallo sana'o'inmu da muka gada iyaye da kakanni wasu sukazo daga nisan duniya suka kwace mana sakamakon fatali da mukayi das u. Nawane wadan da suke zuwa garuruwanmu babu ko sisi kuma su kayi sana'ar da mukaki koya su koma garuruwansu suna masu arziki! Idan kunne yaji . . .!


Yasir Ramadan Gwale
yasirramadangwale@gmail.com
http://yasirramadangwale.blogspot.com