Saturday, December 31, 2011

Mallam Ahamadu Maigandu shi ne Gwarzona na shekarar 2011!

Assalamu Alaikum warah matullahi ta'ala wa barakatuhu.

Ya 'yan uwa ina gaisheku gai suwa irin ta addinin musulunci. kuma ina fatan alheri gareku baki daya. sanin kowannenmu ne cewa shekarar Musulunci tuni ta riga ta gabata, sannan kuma yau ne muke ban kwanan da wannan shekara ta miladiyya ta 2011. Kamar yadda muka sani gab da karewar wannan shekara wani muhimmin al'amari ya faru wanda dukkan 'yan uwa suka yi farin ciki da murna da faruwarsa, wato hadin kai da aka samu tsakanin bangarorin izala guda biyu Jos/kaduna.

Shakka babu wannan al'amari muhimmin abu ne. wannan hadin kai dai ya faru ne sakamakon rasuwar dan uwa kuma daya daga cikin jigo na kungiyar Izala reshen jihar kaduna. Jama'a da dama sun nuna alhinin wannan bawan Allah irin yadda aka ringa fadar kyawawan kalamai a gare shi ya nuna irin yadda ya zauna da jama'a lafiya. jama'a daga sassa da dama sunta tudada zuwa jiharsa ta Bauchi domin yin ta'aziya ga iyalansa da 'yan uwansa da abokan arziki. Da kuma nuna alhinin rashinsa.

Lokacin da Sheikh Sani Yahaya Jingir shugaban bangere na Jos ya nemi wannan hadin kai lokacin da ya kai ziyarar ta'aziyar Maigandu. shakka babu akwai jama'a da dama da suka kai ruwa rana domin samar da wannan hadin kai amma Allah bai sa hakarsu ta cimma ruwa ba, ina jin jina ga babban malaminmu sheikh Dr. Ahmad Gumi ganin irin shi ma yadda ya yi ta kokari a baya wajen ganin wannan hadin kai ya samu. Allah baisa wannan muhimmin al'amari zai samu ta bangarensa ba.

Shakka babu, wannan rasuwa ta wannan bawan Allah ba karamin alkhairi ta haifarwa dimbin musulmi ba. kowa dai yasan da cewa dole hankali ya tashi zuciya ta raurawa idanu su zubar da kwalla a ya yin da akayi rashi musamman na mutumin da yake hidima wa jama'a. Amma Allah cikin ikonsa ya sanya rasuwar wannan bawan Allah itace silar bude wani sabon babi na hadin kan al'ummar Musulmi a wannan kasa tamu. Tabbas iyalan Malam Maigandu da makusantansa sunji takaicin rabuwa da shi a lokacin da Allah ya rubuta rayuwarsa zata koma zuwa gareshii. kamar yadda Allah ya fada a cikin alkur'ani kowane mai RAI zai dandani mutuwa, mai gandu dai ya riga ya dandani tasa kamar yadda kowannemu zai dandana kamar yadda Allah ya yi alkawari. Amma kuma ta gefe guda kuma masu hankali sai suyi murna ganin cewa ta sanadiyarsa ne Allah ya samar da wannan babban muhimmin al'amari na hadin kan Musulmi Ahlussunnah a wannan kasa tamu.

Muna fatar wannan hadin kai da akasamu ya dore har iya tsawon rayuwarmu. kuma kamar yadda aka cimma matsaya kan Alkur'ani da sunnah shakka babu wannan shi ne zai hada kan al'ummar Musulmi baki daya, Allah ya cigaba da hada kanmu wajen yi masa da'a da biyayya da hani ga mummuna da kuma umarni da kyakkyawa.

Daga karshe ina addu'ar Allah ya jikan Mallam Ahamadu Maigandu ya gafarta masa yasa al'janna ce makomarsa. kuma 'yan uwansa da iyalansa Allah ya basu ladan hakuri ya cika a mizaninsu. kuma shima babban malaminmu kuma sabon shugaban wannan hadaddiyar kungiya Sheikh Sani Yahaya Jingir Allah ya saka masa da alheri kuma Allah ya yi masa jagoranci bisa wannan Nauyi da aka dora masa. Allah ya sadamu da alherinsa baki daya.

Mallam Maigandu wallahi kaine gwanina na wannan shekarar, Allah ya albarkaci zurriyarka ya kyautata bayanka.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@yahoo.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com


Saturday, December 17, 2011

Yadda Za A Magance Al’amuran Tsaro A Najeriya

Hakkin kowace gwamnati ne ta kare tsaron rayuka da lafiya da kuma dukiyar al’ummarta. Gwamnati itace ke da alhakin kulawa da dukkan al’amuran mutanan da suke karkashinta baki ne ko ‘yan kasa. kula da dukkan dangogin tsaro yana kan hukuma tuna daga tsaron kan iyaka, kula da shige da fice ta sama da ta ruwa. Tunda dukkan masu kayan sarki ko aikin damara suna karkashin hukumane kuma da dukiyar al’ummar kasa ake biyansu albashi. Kamar kuma yadda muka sani shugaban kasa shi ne shugaban kwanmandan askarawan kasarnan baki daya dukkan wani abu da yake da alaka da tsaro shugaban kasa shine mutum na farko akan wannan al’amari.

Sanin kowane dan Najeriya ne cewa sha’anin tsaro ya tabarbare a wannan lokaci da ake fuskantar matsin rayuwa. Al’amura na kara dagulewa a yayin da aikin yi ya yi karanci, jami’o’I da kwalejoji kuma suna ta kara kyankyasar sabbin masu kammala karatu, haka kuma jama’a na ta kara aure da haihuwa, al’umma na karuwa ita kuma gwamnati na ta kara fadada tunani wajen Karin samun hanyar kudin shiga. A daidai wannan lokaci ne kuma al’ummar kasa suka shiga cikin wani hali na zullumi da fargabar abubuwan da ka iya zuwa su zo wadan da suka shafi sha’anin tsaron rayuka da dukiyoyi.

Sanin kowa ne a ‘yan shekarun da basu wuce 15 ba ansamu hasarar rayuka da dukikoyi masu dimbin yawa ko dai ta hanyar fashi da makami ko rikicin kabilanci ko rikin addini ko sanadiyar tashin bam ko hadurra akan manya da kana nan hanyoyinmu koma ta wasu hanyoyin da ba wadannan ba wanda Allah ne ka dai yasan adadinsu a wannan kasa tamu mai al’umma kusan miliyan 167 da kuma kabilu daban da ban, bayaga tashe-tashen hankula da rigingimun kabilanci dana addini da suka sha faruwa kuma suke faruwa a daidai lokacin da kasar ta samu dimbin dukiyar da ba’a taba samuba tunda aka samu Najeriya a shekarar 1914, lokacin da aka hade kudu da Arewa a matsayin kasa daya al’umma daya.


Sannan ga kuma wata sabuwa da ke faruwa kamar yadda mukaji a makon da ya gabata cewa wasu kafofin yada labaran kasar nan suka ruwaito labarin yadda wasu tsagerun ‘yan kungiyar OPC masu rajin kare muradun yarbawa suka yi barazanar yaki da kungiyar boko haram a birnin Ikko. Hakanan a makon da ya gabatar ne muka ji yan tsagerun yankin Neja Delta suka yi tattaki da niyar yin zanga zanga a babban birnin tarayya Abuja, duk da jami’an tsaro sun yi nasarar dates su a garin Lokoja, hedikwatar jihar Kogi. Suma yan kungiyar MOSSOB, masu fafutukar ganin kasar Biafra sun kara nanata kudurin su na ganin ko dai dan kabilar Ibo a bashi dama a shekara ta 2015 domin ya hau kujerar shugabancin kasar nan ko kuwa a basu dama su kafa kasar su domin su cika burin jagoran su, Ojukwu da ya kwanta dama a yan kwanakin baya.

Duk dan Najeriya yasan da cewa kullum ana kara samun yawan aukuwar al’amura da suke nuna cewa tsaro yayi karanci a kasar nan. Kama daga abin da ya shafi fashi da makami da fyade da tashin bamabamai da karuwar hadurra akan manya da kana nan hanyoyi, dama rikicin kabilanci da na addini da ya ki ci yaki cinyewa. Duk wannan ‘yan Najeriya na sane dasu, kuma ana ta dogon turanci akan yadda ya kamata wadan da al’amarin yashafa su fuskance shi. Idan ana so ayi maganin tabarbarewar tsaro a Najeriya to kuwa kamata ya yi gwamnati ta dauki mataki kamar haka.

Abu na farko, dole ne duk inda aka samu labarin fashi da makami ko fyade ko daba ko kalare ko tashin Bam ko fadan kabilanci ko na addini, garkuwa da mutane, fasa bututun mai, da ta’addacin tsagerun Neja Delta, OPC, MASSOB, Boko Haram. Tilas ne gwamnati ta kame wandan nan mutane kamar haka, na farko Mai unguwa da kansila da dagaci da shugaban karamar hukuma da DPO na ‘yansanda da darakta ‘yansada na farin kaya na wannan karamar hukuma ko kuma yankin da abin ya faru. Akan cewa tilar su bada bayanin ya akayi abin da ya faru wanda yake da alaka da tsaro ya auku, saboda duk al’amarin tsaron wannan yanki yana karkashin kulawarsu ne, saboda sune wakilan hukuma ta wannan bangare a kuma wannan yanki. Domin a matakin farko wadan nan sune wa ‘yanda suke da hakkin kula da shiga da fitar mutane na yankin da suke ciki, wajibi ne gwamnati ta tuhumesu akan cewa kodai sunyi sakaci wani mugun mutun ko wasu miyagun mutane azzalumai sunzo da nufin cutar da al’umma, ko kuma dama da hadin bakinsu aka aikata dukkan ta’asar da ta afku. Tunda sune suke shugabantar al’umma a wannan yanki duk abin da ya faru su ake tunkara.

Abu na biyu, wajibi ne gwamnati ta gudanar da binciken na gaggawa kuma bisa gaskiya da adalci akan dukkan rahotannin da suka shafi tsaro. Dole ne kuma a hukunta dukkan wanda aka kama da laifi komai girman mukaminsa akuma bayyanawa jama’a suji. Sannan hukuma ta gargadi jami’anta akan sakaci da aiki da kuma hukuncin duk wanda aka samu yayi sakaci da aikinsa har aka samu Baraka ta gefensa.

Abu na gaba kuma, dole ne gwamnati ta samarwa jami’anta ina nufin na tsaro cikakkun harkokin jindadi da walwalarsu da ta iyalansu. Tundaga kyakkyawan albashi da kuma kayan aiki wadan da sukayi dai dai da zamani, wanda wannan shi ne zaiyi maganin cin hanci da rashawa akan harkar tsaro.

Idan har gwamnati ta gwada daukar wadannan matakai al’amura basu kyautata ba to tabbas kamar yadda masu Magana suke cewa da akwai lauje cikin nadi, akwai wadan da sukewa gwamnati zagon kasa ta fuskar tsaro, akwai baragurbi kuma dole gwamnati ta binkitosu tare da hukunta su ko su wane kuma komai girman mukaminsu.

Domin munyi imani dukkan wasu makamai ko na harbi ko masu fashewa da suke yawo acikin kasa gwamnati tana da masaniyar daga inda suka fito. Domin makami ba kamar abinci bane da ake shukawa a gona haka kuma ba kamar kaya bane da kowane dan kasuwa zai iya sana’antawa a masana’antarsa, tabbas duk inda kaga makami yana da alaka da hukuma ko ta kusa ko ta nesa domin yarjejeniyar mallakar makamai da kasashen duniya suka cimma ta Kyoto Da kuma ta Geneva ta tabbatar da haka. Ashe kaga kenan babu yadda za’ace hukuma batada masaniyar yadda makamai suke yawo acikin kasa ko a hannun jami’anta ko a hannun daidaikun mutane.

Idan kuwa aka bi dukkan wadan nan matakai al’amura basu kyautata ba to tabbas gwamnatin da kanta itace kanwa uwar gami, kawai ana yaudarar al’ummar kasa ne akan sukurkucewar tsaro amma da saninta akayi wasarari da harkokin tsaro don baiwa wasu dama suci karensu babu babbaka alabasshi daga baya a cimma wata boyayyar manufa. Dadin dadawa munsan cewa al’amuran da suka shafi tsaro a kowace kasa suna da bukatar sirri to wajibin hukuma ne ta san irin dabarun da za’abi wajen kyautata al’amura da suka shafi sha’anin tsaro kuma suke da bukatar sirri wanda munsan gwamnati tana nata kokarin. Munsan akwai dokar da gwamnati ta sanyawa hannu kwanakin baya ta ‘yancin neman bayanai wato Freedom of information Bill, munsan da cewa duk inda mutum ya kaiga neman labarai bazai binciki ya ake gwamnati take da makamai ba kuma nawa aka siya nawa aka batar.

Mun san da cewa duk wani makami da yake a Najeriya idan ba na gwamnati bane wanda ita keda al’hakin mallakarsa da kuma kulawa da shi, kuma babu ta yadda za’a yi ya fita batare da masaniyar wadan da abin ya shafa ba. To kuwan babu ta yadda zamu yarda cewa makamin nan ba shigo da shi akayi kodai takan iyaka ko kuma ta gabar teku ko ta amfani da jirgin sama wanda duk wadan nan gurare al’hakin gwamnati ne ta kula da su, idan kuwa tayi sakaci da wannan bangare to tabbas wannan ko wace irin gwamnati ce bata cancanci acigaba da bata goyon baya ba tunda bata iya tsarewa al’umma kasaba ta fuskar tsaro. Haka kuma babu wani mutum da zai iya kera makami ba tare da gwamnati tana da masaniya ba domin dukkan wani abu da ya shafi tsaro babu wanda yake da karfin iko akansa sama da hukuma.

Kamar yadda mukajicewa hukumomi na kokarin sanya na’urar binciken a kofar shiga majalisa mai gani har hanji wadda ake kira Fulbody scanner don kare ‘yan majalisa. To suma al’ummar kasa suna bukatar wannan na’ura don kare rayuwarsu da dukiyarsu, domin ‘yan majalisa ba su kadai bane ‘yan Najeriya ba muma talakawa muna da hakkin gwamnati ta kula damu ta dukkan bangarori ba sai ta fuskar tsaro ba kawai. Kuma bisa yadda mukaji shugaban kasa ya gabatar acikin kasafin kubin shekarar nan mai kamawa anware kudi kusan Naira Biliyan N921.91 a sha’anin tsaro muna fatar al’amura su kyautata wanda a cikin wannan halin ne abun takaici zaka iske ba wanda suka fi cutuwa da rashin tsaro da mummunan talauci da rashin aikuin yi da rashin hadin kai da shugabanci irin alummar Arewacin Najeriya.

Lallai muna kira ga gwamnati ta yi iyakar iyawarta wajen kawo karshen tashin bamabami da kuma rikicin kabilanci dana addini da yaki ci yaki cinyewa a birnin Jos da sauran sassan jihar filato da garkuwa da mutane da fyade da satar jarirai a asibitoci da satar mutane akan hanya da rikicin manoma da makiyaya da wadan nan makudan kudaden da aka fitar wajen sha’anin tsaro.

Idan ba haka ba kuwa abinda Bahaushe yake cewa abinda yaci doma bazai bar awe ba. Wanda wannan yake nuna irin juyin juya halin da yake faruwa yanzu haka a yankin tsibirin larabawa da Arewacin Afrika babu abin da zai hanashi wanzuwa a Najeriya, kamar yadda mukaji kwamitin da shugaban kasa ya kafa akan rikicin bayan zabe karkashin jagorancin dattijo Sheikh Ahmad lemu sunyi gargadi akan wannan batu. Lallai hukumomi su sani duk wadan can abin da suke faruwa a yankin kasashen larabawa rashin Adalci ya janyoshi, don haka adalci shi ne zai zaunar da kasarnan lafiya, kuma shi ne zai cigaba da zaunar da kasar nan a matsayin kasa daya al’umma daya. Muna tabbatarwa da gwamnati kamar yadda suka sani yanzu duniya tana tafiya ne bai daya. Allah ya taimaki kasarmu Najeriya ya bamu lafiya da zama lafiya.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@hotmail.com

http://yasirramadangwale.blpgspot.com

Saturday, December 10, 2011

Makarantun kwana: Annobar Madigo da Luwadi daga ina?

Ya ‘yan uwa barkanmu da sake saduwa, da kuma fatan za a gafarceni akan wannan maudu’I maras dadinji. Ya dan uwa mai karatu lokaci ne ya yi na mu fito mu fadi gaskiyar yadda al’amura suke, ina fatar za a yimin kyakkyawar fahimta, kuma za’a gafarceni bias furta wadan nan kalamai masu matukar nauyi . Zance na gaskiya makarntun kwanan kamar yadda muka sansu a lokacin baya yanzu abin ba haka yake ba.

Makarantar kwana, itace makaranta wadda tafi hada zumunci so sai tsakanin dalibai. Kuma idan banyi karya ba zumuncin ‘yan makarantar kwana bai cika baci ba ko lalacewa komai tsawon lokaci bayan kamala makaranta. Kusan idan ka dauki rayuwarmu gabaki daya zumuntace tun ta makarntar sakandare, mafi yawan dalibai basa wasa da wannan zamatakewa da sukayi a makarantun sakandare, musammanma idan akace makarantar kwana ce. Wannan ce ma ta sanya kake jin kungiyoyin tsaffin dalibai na aji kaza a makaranta kaza. Wanda da wuya kaji na daliban makarantu jami’a ko gaba da sakandare ba.

Kusan daliban makarantar kwana sukan ce duk wanda baiyi makarantar kwana ba to da sauransa a harkar karatun Boko. Domin rayuwar makarantar kwana wata irin rayuwa ce da take da tasirin gaske ainun, hakika duk irin yadda za a baka labarin makarantar kwana ba kamar kaje bane. Domin yara galibi wadan da suke gab da lokacin balaga kan samu kansu cikin wata irin rayuwa wadda babu uwa babu uba, sai dai kawai abokai da yayyi da kanne na makaranta. Annan ne akan kulla abota ta hakika kuma mai dorewa domin kuna tare ku kwana ku tashi ku ci-abinci koda yashe tare. Wannan irin rayuwa ba karamin dadi gareta ba.

Da can idan muna hira da yayyinmu mata ko maza idan suna bamu labarin makarantar kwana sai muji wata irin duniya ce mai dadi kamar kayi tsutsu kaje ka risketa, haka kuma idan ana baka labarin “seniority” sai kaji an zare maka sha’awar makarantar kwana, domin ana bada wanki da debo ruwa da wanke-wanke da tsallen kwado da kama kunne da sauransu wannan kan sa yara su tsoraci makarntar kwana.

Hakika lokacin da nayi makarantar kwana na tabbatar da dukka abubuwan da ake ta fadamin a baya lokaci mai tsawo. Na tuna wata rana da shugaban makaranta wato principal ya tara dalibai “juniors” da “seniors” wato manya da kanana inda yace “abin da nake so daku manyan dalibai hukumar makaranta bata hana ku baiwa kannenku wanki ba, amma abinda muke so daku idan kun bada wanki ku bada sabulu” munsha wahalar wanki da debo ruwa a wannan lokacin domin bama iya samun ruwa daga cikin makarantar Unity Karaye sai munje wani kauye da ake kira kusalla ko kuma munzo cikin garin karaye Torankawa ko kuma kofar zango sannan mu samu ruwa; galibi wannan yafi faruwa a zangon karatu na biyu da na uku lokacin da dukkan rijiyoyin makaranta sun kafe ga kuma rani yayi nisa damina bata soma ba.

A irin wannan rayuwa ta makarantar kwana babu lokacin da dalibi ya fi kauna kamar lokacin darussa da kuma lokacin barci domin sune lokutan da babu wanda zai kiraka ballantana ya aike ka. Zaka samu yara wadan da suke ‘yan ajin farko jss 1 zuwa jss 3 basa iya zama cikin dakunan kwananansu domin gudun duka ko kuma aike, dan ajin ss 1 shine wanda ya fara jiyo kanshin ‘yanci sau da yawa zaka samu sukan zauna acikin dakunansu. Laifi kankani dalibi zaiyi ayi masa hukunci kama daga tsallen kwado zuwa kama kunne ko hawan bango da sauransu, munsha tsallen kwado kamar sojoji.

Gaskiya idan zan iya fada makarantar kwana na daya daga cikin makarantun da suke gyara yara a wancan lokaci, domin ananne za’a koya maka gaida “senior” duk safiya haka kuma dole idan ya taho kaima ka taho ka dakata har sai yashige dalibai juniors sukanyi ladabi irin wanda basa yiwa iyayansu ko yayyensu, idan akayi sa’a wani daga haka shi ke nan ya mike da wannan tarbiyya.

Zance na gaskiya makarantun kwana na yanzu abin ba haka yake ba. Idan zan iya tunawa babbar matsalar da akafi fuskantar a lokutan baya bata wuce dalibai masu shan taba sigari ba da kuma dai sauran abubuwa na kuruci dangin hauka da ba a rasa ba a tsakanin dalibai.

A irin yadda nake samun labari yanzu shine duk abin da na sani da akeyi a baya na seniority yanzu ya zama tarihi domin yanzu gwamnatoci kan yi kokarin katange makarantun maza ba kamar da ba kawai da za a yanki daji ba, yanzu bayan katange makarantu akan samarmusu da famfunan tuka-tuka wanda wannan shi ya rage musu babbar matsalar ruwa. Sai kuma wata babbar annaoba da ta kutso kai gadan gadan cikin makarantun kwana kuma take ci kamar wutar daji itace dabi’arnan ta Luwadi ko kuma Madigo a makarantun mata.

A wani rahoton da na karanta yana cewa kusan kaso 12 na daliban Najeriya dake makarantun kwana suna aikata wannan danyan aiki na madigo da luwadi wanda kalmomin basu da dadin fada a baki ina fatar za’a gafarceni. Haka kuma wannan rahoton yace kusan kaso 15 na daliban jami’a suma sukan aikata wannan mummunan aiki na zakkewa juna da nufin biyan bukatar sha’awa. Banida cikakkiyar masaniyar wannan rahoton gaskyane ko kuwa akasin haka.

Kwanakin baya wata yarinya da bansanta ba ta rubutomin wasika daga wata makarantar kwana dake cikin birnin kano tana gayamin don Allah na fadakar akan wannan matsala da take faruwa a makarantun mata, ta fadamin a cikin wasikar cewa Wallahi lokacin da aka kaita hankalinta ya yi matukar tashi domin tace Wallahi rububinta aka ringa yi kamar ‘yartsana, tace ana yaudarar yara da kayan kyale-kyale da kuma nuna masu soyayya, tace idanma kika ki akan yi miki ta karfin tsaya ta hanyar rikeki da toshe miki baki, wannan yarinya ta sahidamin cewa tayi karyar rashin lafiya kawai don ta koma gida ta sanar da mahaifinta abin da ke faruwa, tace amma da tazo gida ta sanar da mahaifinta gaskiyar lamari sai ya karyata ta tare da cewa batason makarantarne shi yasa ta fake da wannan abu.

Tabbas wannan abu ba karya bane. Domin da zakayi hira da daliban makarantun kwana ka tambayesu gaskiyar wannan al’amari zasu sanar da kai cewa lallai wannan abin yana kara samun tagomashi a tsakanin dalibai. Domin binciken da na gudanar ya tabbatarmin da haka. Dalilan da kansa haka yaduwa cikin sauri sune kamar haka.

Abu na farko, kuruciya da kuma karfin balaga domin galibi akan kai yara makarantar kwana adaidai lokacin da suke kan ganiyar balaga ko kuma suke gab da balaga. Kamar yadda masana suka ce mafi yawanci mazakuta takan cika girmanta ne a shekaru 18 zuwa 22 wannan takan sanya galibi sha’awar yara takan motsacikin sauri. Haka kuma abu na gaba shine yanzu zamani yazo inda yawancin yara kan tafi da wayoyin hannu a boye masu dauke da fina-finan batsa masu yawan gaske, me kake jin zai faru alokacin da yara suke kan ganiyarsu ta balaga kuma ga fina-finan batsa a tsakaninsu?

Abu na gaba shine harkar wasan kwallan kafa, itama wata muhimmiyar hanyace da kanjefa mafiyawanci yara fadawa cikin wannan mummunar ta’ada domin ta haka ake yaudarar wasu da daman gaske, sannan itama kwallon kasashen turai ta Champions league da laliga da sirie A da sauransu sun taka muhimmiyar rawa wajen jefa da yawa daga cikin yaranmu cikin wannan yanayi. Domin akan kulla mummunan kawance tsakanin wannan yaro da wancan yaro. Wato abin yakai yanzu hattana irin mukaman da akan nada yara wato prefect sai annemi yaro ya bada kansa sannan akai sunansa domin tantancewa kuma wannan ana hada baki da wasu daga cikin miyagun malamai marasa kishi da tsoron Allah.

Haka suma makarantun ‘yammata suna da nasu hanyoyi na yaudarar kamar sayan kayan kwalliya irin na zamani da suturu masu dankaren tsada da sarka da yari da sauran abubuwan da ka iya jan hankalin yara mata cikin sauri.

Wannan babban kalubale ne ga iyaye. Lallai wajibin kowane uba ne ya tabbata ya kula da tarbiyyar ‘ya ‘yansa, musamman suturarsu da inda suke zuwa da kuma abokanan mu’amalarsu. Kusan yanzu yana daga cikin abinda iyaye basu cika dubawa ba shi ne abokanan mu’amalar ‘ya ‘yansu, domin zaka ga basu cika basu muhimmanci ba, wanda galibin mu Hausawa mukan dora laifin lalacewar ‘ya ‘yanmu akan abokai kowa ka tambayeshi zaice abokai suka lalata masa yaro haka idan da zaka tambayi uban lalatacce zai gayamaka cewa lalatattun yara suka bata masa yaro, amma duk da haka iyaye basa daukar wani mataki akan wannan batu.

Sannan, yana daga cikin hakkin hukuma ta tsarewa al’umma tarbiyya da kuma mutunci, hukuma itace zatayi tsari dangane da wannan abu da yake cigaba da yaduwa cikin sauri, haka kuma ma’aikatar ilimi da malaman makarantu yana da kyau su sanya ido sosai akan dalibai domin amana ce aka basu kuma su kanda sani sai Allah ya tambayi kowa dan gane da amanar da aka bashi tundaga iyaye har zuwa malami, kuma dole ne su duba hanyoyin da za’abi wajen ganin anshawo kan wannan matsalar tare kuma da hukunta duk wanda aka kama da aikata wannan laifi a bainar jama’a, wanda wannan inaganin itace kadai hanyar da zata iya kawo raguwar wannan aika-aika, zai zama darasi ko izna ga duk wanda yake aikatawa yaga yadda aka hukunta mai yi a bainar jama’a koda kuwa bulalace. Domin babu wanda zai so yaji cewa dansa ko ‘yarsa suna aikata wannan danyan aiki. Allah ya shiryi al’ummarmu.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@hotmail.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

Sunday, December 4, 2011

Me ya sa matasan Arewa ke gudun kana nan sana’o’i?


Rashin aikin yi a tsakanin matasa na daga cikin matsalar da take addabar kasashen duniya a yanzu. da yawan kasashen suna ta neman hanyoyi da za a kawo karshe ko kuma rage adadin marasa aikin yi, rashin aikin yi babbar barazana ce ga zama lafiyar kowace kasa, haka kuma barazanace ga tsaron lafiya da dukiya. Kusan kididdiga ta nuna mafiya yawan wadan da ke cikin wannan mummunan yanayi na rashin aikin yi matasane wadan shekarunsu suka kama daga 18 zuwa 30 a mafiya yawan kasashen duniya.

Najeriya kasace da Allah ya huwace mata al’barkatun jama’a wadan da galibinsu matasane maza da mata. Kusan kididdiga ta baya-bayan nan ta nuna cewa akwai kusan mutane miliyan 167 a Najeriya wanda wannan adadi ke karuwa cikin sauri a cewar masana, acikin wannan lissafi kusan sama da kashi 65% matasane ‘yan bana bakwai masu jinni ajika. Kuma mafiya yawan al’ummar Najeriya suna yankin Arewa ne.

Babbar matsalar Najeriya yanzu bata wuce rashin aikin yi tsakanin matasa ba kamar sauran takwararorinta kasashen duniya. Dalilan da suka samar da rashin aikin yi tsakanin matasa a Najeriya abayyane suke. Rashin ingantacciyar wutar lantarki kusan itace babbar matsalar da ta haifar da rashin masana’antu wanda hakan ya haifar da rashin aikin yi, domin da wutar lantarki ne galibin kamfanoni ke aiki wanda suke taka muhimmiyar rawa wajen rage adadin marasa aikin yi akusan galibin kasashen duniya. Yau a Najeriyya babu masana’antu a yankin Arewa da zasu iya rage adadin matasanmu kama daga wadan da suka kamala jami’a da kuma wadan da suka fito daga kwalejoji dama wadan da basu sami damar zuwa makaranta ba.

Kididdiga ta nuna cewa gwamnatin PDP karkashin shugabancin tsohon shugaban kasa Olushegun Obasanjo ta kashe kudi sama da dalar amurka Biliyan 16 kimamin Naira tiriliyan 1.3 akan wutar lantarki acikin shekaru 8, amma babu ita babu dalilinta kuma kudin shiru kamar an shuka dusa. Abin tambaya anan shi ne shin ina wutar ta ke? Kuma idan ba’ayi aikin ba kamar yadda muka gani ina kudin suke? Akwanakin baya ‘yan majalisa sunyi dambarwa akan wannan batu amma yanzu shiru kake ji,abun da yake nuna anci bulus kenan.

Idan muka dauki misali da kasar Brazil ta kashe kudi kimanin dalar Amurka biliyan 5 wajen samar da wutar lantarki mai karfin megawatt 120,000 acikin shekara 3 kacal, haka itama kasar Afurka ta kudu sun kashe kudi kimanin dalar amurka biliyan 1 wajen samar da megawatt 5,000 acikin shekara daya kacal. Idan ka dawo nan gida Najeriya zaka ga cewa kudin da aka fitar ya ninka na Afurka ta kudu ninkim baninkim amma megawatt nawa aka samar mana? Lokacin da marigayi tsohon shugaban kasa Mallam Umaru YarAdua yazo ya kudiri aniyar ganin bayan matsalar wutar lantarki a Najeriya wanda ya durfafi aikin fafur wajen ganin ya cimma kudurinsa na samar da megawatt 10,000, Allah bai cika masa burinsa ba ya kwanta dama. Wannan shugaban da ya gajeshi cewa yay i zai dora daga inda ‘yar Adua ya tsaya inda ya nada kansa munistan makamashi da wutar lantarki amma babu wasu alamu da suke nuna da gaske ake akan wannan batu.

Idan kuma muka komo yankin Arewa a yanzu haka wutar lantarki da muke samu daga babban kamfanin rarraba wutar lantarki na kasa bai wuce megawatt 3,000 ba gaba daya yankin Arewa mai jihohi 19, wanda wannan kaso kusan shi ake baiwa jihar Legas ita kadai. Abin tambaya me gwamnatocinmu da ‘yan majalisun mu suke? Ina sarakuna da ‘yan boko ina tsofaffin sojojinmu ina sababbinsu ke ina kungiyar dattawan Arewa? Ina duk masu fada aji da muke dasu me sukayi akan cewa yankin Arewa ya samu wutar lantarki tabbatacciya.

Idan kuma muka koma batun aikin yi tunda yake Manya manyan masana’antun da muke dasu a kano da kaduna sun kwanta dama sakamakon sakacin magabatanmu akan wutar lantaarki me ya rage mana? Abin da muka gada iyaye da kakanni wato sana’o’in hannau, amma duk munyi watsi da su. Ina noma da kiwo duk mun watsar dasu sai tsurarun talakawa marasa galihu suke wannan yanzu.

Yankin Arewa mu muka fi kowane yanki albarkar jama’a a Najeriya amma mune muke da adadi mafi yawa na marasa aikin yi; wani abu da na gani ya bani mamaki shi ne inda naga Inyamuri na sana’ar pawa wato ya sayi saniya ya kai abbatuwa a yanka a rabawa Hausawa naman sukuma su sayar idan yamma tayi su hada masa kudinsa, kaga wannan shine cikakken koma baya awajen mutanan Arewa me ya hada inyamuri da sana’ar pawa? Kuma kaje kasuwar Hatsi ta Dawanau dake kano kasha mamaki inda zaka ga inyamurai na cin karensu da babbaka, inyamuri zai sayi wake da masara da gyero ya kai sito ya ajiye idan yayi tsada ya fito dashi ya sayar.

Mafi yawan matasa yanzu a Arewa basa son yin sana’ar hannu. Kowa ya nade hannun riga yana jiran ya samu na banza babu sididi babu sadada. Muna da dimbin matasa da suka kamala jami’a basu da aikin yi, amma kuma su baza suyi sana’a ba indai ta hannu ce kowa ya dogara da cewa sai aiki mai maiko ko kuma aikin da zakayi kudi nan da nan, don haka kullum sana’o’inmu kara komawa baya suke yi. Mafi yawan sana’o’inmu basu da bukatar kama hayar shago ko kanti basu da bukatar kudi da yawa amma zaka samu tashoshi na matasa agefen tituna acikin biranenmu na Arewa suna zaman banza.

Zance na gaskiya iyaye sun taimaka wajen kara yawan masu zaman banza a Arewa. Domin kuwa zaka ga yaro baya samun wani kwarin gwiwar cewa yay i sana’a tun yana karami, haka kuma anshagwaba yara talaka da mai kudi kowa ya shagwaba dansa kaga saurayi dan shekara 18 zuwa 20 harma 25 ana bashi kudin kashewa mu duk agurinmu yaro ne; wanda inda aka cigaba duk dan shekara 15 ya tashi daga sahun yaro ya koma saurayi. Misali a kasar Jamus duk dan shekara 18 dole ya fita daga gidan iyayansa ya nemi na kansa don fuskantar rayuwarsa. Idan banyi karya ba zaka iske matashi dan shekara 30 a Arewa yana zaune agida baya aikin fari bayan a baki kuma ana ciyar dashi da tufatar dashi kai harma da bashi kudin kashewa amma babu wani kwarin gwiwa da ake bashi nacewa yaje ya koyi sana’a.

Ka shiga ka suwanninmu kaga yanda matasanmu suka zama ‘yan kamasho. Mutum zai wanke riga ya fita kasuwa banda haram babu abin da ya tafi nema da sunan wai ya tafi kasuwa amma bashida rumfa ko kanti bashida jari kona kwabo, kawai yana ci ajikin talakawa ‘yan uwansa da daurin gindin wasu daga cikin ‘yan kasuwa. Bayan idan za’ayi Magana ta gaskiya shi kansa kasuwancin da muke takama da shi anyi rugu-rugu da shi ‘yan kasuwa nawa ka sani wadan da suka karye kodai sakamakon bashi ko fashi ko damfara ko zurmiya ko sanbanza da zulama? Suna da yawan gaske basa samun wani tallafi na kirki daga al’umma ko daga gwamnatoci. Yanzu kusan duk kasuwanninmu Sinawa da indiyawa sun mayesu idanma kaga muna kasuwanci to ba namu bane su mukemawa. Me ya janyo mana fadawa wannan hali?

Haka kuma gwamnatocinmu basuyi mana wani tsari na koyar tare da fadawa yara muhimmancin sana’a ba a makarantu tundaga sakandare har zuwa jami’a. ya kamata ace acikin jadawalin karatunmu akwai koyar da sana’o’I yaro tun yana makaranta akoya masa wani abu da zai iya yi ana gaba, haka suma jami’o’I ya kamata ace akwai wani tsari na karfafawa dalibai gwiwa idan sun kammala jami’a su dogara da kansu ba lallai sai mutum ya yi aikin gwamnati kona kamfanonin sadarwa ko wani muhimmin aiki zai zama wani ba.

Na karanta a wani shafi na Makarantar kimiyya da fasa wanda Abubakar salihu baban sadiq yake kula dashi. Inda ya kawo wata kasida da marigayi steve jobs wanda shi ne shugaban kamfanin Apple inc Kafin rasuwarsa dai ana kirga shi daga cikin mutanen da suka yi tasiri mafi girma a duniya wajen habbaka harkar sadarwa da kere-kere, musamman kan wayar salula, da kwamfuta, da na’urorin sadarwa nau’uka daban-daban, da allon shigar da bayanai na kwamfuta (Keyboard), da lasifika da dai sauransu. A yadda shi wannan mutum ya bada tarihinsa ya ce shi bai samu damar yi ko kammala jami’a ba, ya maida kai waje sana’ar hannu ne a karshe ga yadda Allah ya mai dashi. Na kawo wannan ne a matsayin misali kawai.

Ya kamata yanzu duk da wasu gwamnatoci suna kokarin koyawa matasa sana’o’i tare da basu jari, ya kamata wannan shiri ya shiga cikin jadawalin koyar da karatu tundaga matakin sakandare har jami’a kamar yadda yake a shekarun baya.

Yanzu idan ka dauki harkar kiwon kaji da kiwon kifi kawai wata babbar sana’ace da zata rike mutane da yawa, misali ka kalli yawan jama’ar kano da kaduna da sokoto zaka iya kididdigar kwai nawa ake ci a wadan nan garuruwa ko kuwa kifi nawa ake ci? Amma wani abin ban Haushi da takaici shi ne kaso sama da 50% na kwan da muke ci bama iya samar da shi a Arewa sai anshigo mana da shi daga kudu duk da albarkar da Allah ya bamu ta ruwa da kasa mai yabanya.

Mu kanmu yanzu a Arewa sai kaga cewa kamar wani mulkin mallaka ake yi mana domin irin gonakan da tsohon shugaban kasa Obasanjo ya sa aka sayarwa da manoma ‘yan kenya da zambabwe a jihohin Taraba da Kwara ake amfani da matasanmu su noma kuma akwashe a fita dasu daga baya a sarrafa wani abu a kawo mana a farashi mai dan karen tsada bayan mu muka sha wahalar. Allah ya kyauta.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@hotmail.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com