Friday, August 26, 2016

Jakadan Sa'udiyya A Najeriya Ya Zubda Hawaye Don Tausayin Wata Mata


JAKADAN SA'UDIYYA A NAJERIYA YA ZUBDA HAWAYE DON TAUSAYIN WATA MATA

Mai Girma Jakadan Sa'udiyya a Najeriya, Sheikh Fahad Abdallah Sufyan, ya kadu matukar kaduwa sakamakon wani rahoto da ya karanta wanda Jaridar Daily Trust ta wallafa a ranar 13 ga watan Agusta 2016. Rahoton an yi masa taken, "Meet Kaduna Lady Who's Raising 5 Abandoned Babies" wato labarin wata mata da ta kula da rayuwar yara biyar tsintattu. Jakadan ya kadu ainun bayan karanta wannan Rahoto, inda ba da bata lokaci ya bukaci Ustaz Abubakr Siddeeq wanda shi ne Limamin Masallacin Abuja da yake Fassara huduba da Turanci, inda ya tambaye shi ko yaga rahoton da Jaridar ta buga. Inda Ustaz Siddeeq yace bai karanta ba. Nan da nan Jakadan ya turawa Ustaz Siddeeq hoton shafin jaridar da ya dauka a wayarsa ta Whatsapp dan ya duba ya gani. Jakadan ya kuma, bukaci Ustaz ya binciko  wannan mata tare da shirya masa yadda zai gana da ita ido da ido.

Labarin dai na wata mata ce mai suna Hajiya Uwani Yusuf Waziri, wadda aka fi sani da Uwar Marayu.  Wannan mata mazauniyar unguwar Kaji ce a jihar Kaduna. Tana da 'ya 'ya goma sha daya, duk da irin halin da take ciki, ta dauki gabarar kula da tarbiyyar yaran da aka tsinta ta rike su a matsayin 'ya 'yan ta. A duk lokacin da aka tsinci jariri a unguwannin Rigachukum ko Barakallahu ko Hayin Na Iya a kasan gada ko cikin Lambatu akan kai su gidan Hakimi, nan take shi kuma Hakimi zai tura da jairin da aka tsinta zuwa gidan Uwar Marayu. 

Ina cikin garin Kaduna a lokacin Jakada Sheikh Fahad Abdallah Sufyan ya bani wannan umarni.  Dan haka abin sai ya zo min da sauki wajen tuntubar yadda zan hadu da wannan mata. Dan haka ne na samu abokina Dr. Mahadi Shehu wanda shi ne Shugaban Kamfanin Dialogue Global Links tare da gudunmawar Maryam Ahamadu - Suka wadda ta hada wannan rahoto da tallafawar Rufa'at Maccido muka kai ga wanna mata.

Bayan da muka yi katarin gamuwa da Hajiya Uwar Marayu, muka sanya ranar Laraba 17 ga watan Agusta 2016, domin ganawar wannan mata da Jakada Sheikh Fahad Abdallah Sufyan da Misalin karfe 11 na safe a Birnin Tarayya Abuja. A lokacin Maryam da Hajiya Uwar Marayu sun zo tare da daya daga cikin marayun da wannan mata take raino mai suna Zainab, wadda take cikin zanin goyo. Mai Girma Jakadan Sa'udiyya Sheikh Fahad, ya yi mana tarba ta musamman a ofishinsa,  ya marabcemu da Shayin Larabawa na Gahwa da Dabino. A lokacin nayi kokarin zubawa kowa da kaina, amma Jakadan yace kar na damu zai zubawa kowa da kansa dan girmama Uwar Marayu. Bayan ya gama zubawa kowa Gahwa, ya kalli Zainab a cikin zanin goyo yace, yanzu wannan jariri bai yiwa kowa laifi ba na zuwan sa duniya amma an yasar da shi. 

A lokacin da Jakada Sheikh Fahad, yake bayani idanunsa sun cika da kwalla, zuciyarsa ta raurawa. Yayi ta kokarin yin magana amma ina kukan da yake a zuciya yaci karfinsa, inda ya kasa hadiye hawayen da suke kwaranya a kumatunsa. Ganin haka,  sai na Mikawa Jakada audugar share Gumi dake kusa da ni, dan ya goge hawayen da suke guda a kuncinsa. Dukkanmu da muke zaune a wannan waje, muka kasa jurewa, zukatanmu suka raurawa hawayen tausayi ya dinga bayyana a fuskokin mu, adaidai lokacin, Zainab dake cikin zanin goyo da bata san meke faruwa ba, ta fa she da kuka, abinda ya kara tsinka mana zukata, nan dai Uwar Marayu ta shayar da ita Madarar da ke tare da ita, wadda ke zube a cikin Bulumboti. 

Haka nan, Sheikh Fahad Abdallah, yayi karfin hali ya fara magana cikin murya mai cike da nuna tausayi da damuwa. Yace, masu Imani sune suke jibantar lamarin 'yan uwansu musamman wadan da suke cikin tsananin bukata. Kamar marayu da mata da aka mutu aka barsu da yara. Wadannan sune suka cancanci a taimaka musu. Ya k'ara da cewar, Manzon Allah Tsira Da Amincin Allah su k'ara Tabbata a gareshi ya ce, Ni da wanda yake jibantar al'amarin Marayu kamar yatsu ne guda biyu, Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam yana mai nuni da yatsunsa biyu. Ya cigaba da bayani yana cewa; Watarana wani mutum yazo wajen Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam, yake ce masa, Ya Rasulullahi zuciya ta na fama da kunci da damuwa haka kurum, Manzo yace da shi, ka jibinci al'amarin Marayu ka ciyar da su daga abinda kake ci, Allah zai saukaka maka lamarinka, zuciyarka zata samu nutsuwa. 

Jakada Sheikh Fahad, ya cigaba da cewa, Hajiya Uwar Marayu kin cancanci jinjina da Yabo,  kuma kin cancanci ayi koyi da ke, kin zama zak'ak'ura a cikin matan Najeriya. Ya cigaba da bayanin cewar, duk wanda ya yayewa wani damuwa,  Allah zai yaye masa damuwa ranar tashin Alkiyama. Ke uwar marayu ce, ina tunasar dake Hadisin Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam da yake cewa zamu shiga Aljannah tare da shi, yayi mata nuni da yatsunsa biyu; duk wanda ya jibanci al'amarin Marayu. 

Bayan da ya gama gajeriyar tunasarwa. Ya mikawa Hajiya Uwani Uwar Marayu wata gagarumar kyautar da ya bukaci kada a bayyanawa duniya kyautar da yayi mata. Sannan ya yiwa Marayun da take raino Goma ta Arziki. A hakikanin gaskiya zan iya cewa wannan kyauta da yayi musu Takai ta kawo duk da ya roki Alfarmar kada na bayyana abinda ya bayar, amma ya yiwa Uwar Marayu kyauta mai girma. "Wanda duk ya taimaki wani, shima Allah zai taimake shi ya jibanci lamarinsa."

Wannan abinda Jakadan Sa'udiyya ya yiwa wannan mata Hajiya Uwani Uwar Marayu ya kamata ya zabarurar da al'ummar mu wajen tausayawa Marayu musamman jariran da ake haifa kuma a yasar da su akan titi ko cikin Lambatu. Mu yawaita kyauta da sadaka domin bamu san Me Allah ya yi mana tanadi na alheri ba. Allah Ta'ala ya fada a cikin Sura Ta Biyu Aya Ta 268, Shaid'an yana tsoratar da ku da talauci da fatara, yana kuma yi muku bushara da rayuwa mai tsawo. Allah kuma yayi muku alkawarin Rahama da sakamako mai gwabi. Allah shi ne Masani mai hikima".

Hanzari: Wannan bayani Ustaz Abubakr Siddeeq ne yayi a shafinsa na Facebook da Blogspot. Ni kuma na fassara shi zuwa Hausa. Allah yasa mu dace.

Yasir Ramadan Gwale 
26-08-2016

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari


SHUGABAN KASA MUHAMMADU BUHARI 

Muhammadu Buhari Shugaban kasa ne kuma Shugaban mu ne, muna so masa Alkhairi kamar yadda muke so wa kanmu. Bama fatan Allah ya azabtar da shi a dalilin hidima da ya yiwa wannan kasa, muna fatan Allah ya sauka ka masa lamura ya bashi lafiya da ikon sauke nauyin da yake kansa. Bama aibata shi ko yi wasa mummunan fata, ko samun sakamako mai muni a karshen Gwamnatinsa, a ko da yaushe fatanmu shi ne, Allah ya saukaka masa lamura, ya aiwatar da ayyukan alkhairi ga wannan kasa tamu. Samun Nasarar sa shi ne cigaban mu, idan yayi Nasara kasarmu ce ta cigaba, idan kasarmu ta cigaba mune muka cigaba.

Bamu gushe ba, muna masa uzuri muna masa kyakkyawar fata. A kullum burin duk wani dan kasa na gari ne a ce kasar mu Nigeria ta samu cigaba fiye da dukkan kasashen Afurka. Ba muda wata kasa da za mu yi alfahari da ita da ta wuce Nigeria, dan haka duk wanda yake rike da ragamar jagorancin ta tilas ai masa biyayya da fatan ya samu Nasara wajen cimma manufofin sa na Alkhairi da yayi nufin wanzar da su a tsakanin wannan al'umma tamu.

Muna da masaniyar cewar babu wani shugaba da yake da hankali da kuma yasan me yake, da zai yiwa al'ummar sa mugunta da yi musu fatan shiga mawuyacin halin ni 'ya su. Kullum Shugabanni na gari buri suke da fatan saukakawa al'umma da kawo musu cigaba mai dorewa. Muna da masaniyar halin da tattalin arzikin kasarmu ya shiga na koma baya, wanda muke fatan ya zama Rahama a gare mu nan ga. Muna kuma fatan shugabanni na yanzu da masu zuwa nan gaba su himmatu wajen Alkinta dukiyar kasa domin amfanin jama'a. 

Amma duk da wannan buri da fata da muke yiwa Shugaban kasa, tilas ne mu fito mu nuna damuwar mu akan irin wannan mawuyacin hali da muke ciki. Ba laifi bane, dan wasu ko wani yayi korafin halin da yake ciki na tsanani, dukkan dan kasa yana da 'yanci daidai da kowa wajen bayyana gamsuwa ko rashin ta kan kowace irin Gwamnati. A dan haka muke kira ga Shugaban Kasarmu da yayi duba na tsanaki akan irin mawuyacin halin da al'umma suke ciki, a aiwatar da sauye sauyen da zasu kawo sauki a rayuwar al'umma ba tare da tsanantawa ba.

Hakkin Gwamnati ne kare muradun kasa da na al'umma. Amma kula da Al'umma shi ne akan gaba. Mutane suna cikin hali na yunwa, Masallatai da Majwmi'u sun zama tamkar wajen bara da roko, haka duk wata matattara ta jama'a, ta zama wajen roko. Mutane a cikin galabaita suke rokon abinda zasu ci dan su samu rayuwa. Khalifan Musulunci na biyu Umar Bin Khaddab Allah ya kara yadda a gare shi, yakan zama cikin zullumi da damuwa, akan kada Akuya tayi tuntube ko ta rasa abinda zata ci karkashin jagorancin sa Allah ya tambaye shi. Akuya fa tsoro yake kada Allah ya tambaye shi hakkin ta, sabida tsananin tsoron Allah.

Misalin irin zullumin da Umar Bin Khaddab ya kamata shugabannin su dinga kasancewa, domin samun kubuta a ranar gobe kiyama. Yanzu kai kadai a gidan ka, a tara maka iyalanka su yi maka tambaya akan hakkin su, sai ka shiga cikin tashin hankali da damuwa dan baka san me zasu ce ba. To ina ga tambayar ranar Alkiyama ace al'ummar Nigeria na batun hakkin su kan Shugabanni?  Ya kamata Shugaban kasa Muhammadu Buhari yaji tsoron Allah wajen tafiyar da Gwamnatinsa. A saukakawa al'umma mawuyacin hali. Allah ya bamu dacewa.

Yasir Ramadan Gwale 
26-08-2016

Thursday, August 25, 2016

Mai Martaba Sarkin Kano Muhammadu Sunusi Na Biyu Ya Tsage Gaskiya Akan Gwamnatin Buhari


SHIGA LAFIYA ALFANDA: MAI MARTABA SARKI MUHAMMADU SUNUSI II YA TSAGE TA

Ba shakka Mai Martaba Sarkin Kano Muhammadu Sunusi Na Biyu ya tsage gaskiya mai mugun daci  game da kudurorin wannan Gwamnati kan batun tattalin arzikin Kasa. Lokaci yayi da wannan Gwamnati zata bi shawarwarin kwararru domin ceto tattalin arzikin kasarmu daga halin tangal tangal din da yake. Idan ba haka ba kuma, labarai marasa dadi ne zasu ci gaba da faruwa. Abin kam akwai ban tsoro matuka idan aka cigaba da tafiya a haka. 

Ga kadan daga abinda mai martaba Sarki yace,  "misali a lokacin da Babban Bankin kasa CBN yake sayar da Dollar akan farashin hukuma na 197 amma mutane na saya 300 a kasuwar bayan fage, idan na zauna a gidana na dauki sailula ta ina da adadin mutanan da zan kira da zasu samo min zunzurutun kudi har Dollar Miliyan Goma a farashin hukuma na 197 ni kuma na sayar a farashin kasuwar bayan fage na 300, kunga kenan zan ci kazamar riba a wannan harka, domin na samu riba sama da Naira Biliyan Daya. Haka na nuna cewar idan na samu Dollar Miliyan goma sau hudu na ci ribar sama da Naira Biliyan hudu, Bugu da kari zan yi haka ne fa ina dakina ba tare da naje ko ina ba.

To a irin wannan yanayi ne fa ake cewar an shirya tattalin arzikin Ć™asa domin ya amfani talaka. Ku gaya min ta ina Talaka yake amfana, idan ba masu kudi bane suke sake kudancewa? Ya zama tilas Gwamnati tayi abinda ya dace domin ceto tattalin arziki daga lalacewa. Idan ba haka ba kuwa, Talaka zai sake shiga matsanancin talauci masu arziki kuma na kara kudancewa." 

Wadannan sune kadan daga cikin kalaman Mai Martaba Sarkin Kano Muhammadu Sunusi wanda Galibin jaridun yau suka wallafa. Don haka ya zama tilas Gwamnati tabi shawarar kwararru domin fitar da kasar nan daga halin da take ciki.

Allah ya taimaki Sarki ya kara masa lafiya da karfin fadar gaskiya komai dacinta. 

Yasir Ramadan Gwale 
25-08-2016