Saturday, April 7, 2012

Hattara Dai Sardaunan Kano!!!



Mallam (Dr) Ibrahim Haruna Shekarau Sardaunan Kano wazirin Raya kasar Nufe, kuma tsohon gwamnan kano, basarake, jigo a siyasar jihar kano da Najeriya. Hakika mallam shekaru bashida bukatar fassara a siyasar Najeriya, tun daga Patakwal har Jibiya, haka kuma, tundaga Badagary har zuwa Nguru, sunan Sardauna ya kewaya tun lokacin yana gwamna, ballana tana kuma, mutumin da ya yi takarar shugaban kasa, a babbar jam’iyyar adawa.

Ya maigirma Sardauna! Hakika kana daga cikin mutane kalilan da Allah ya yiwa wata irin baiwa marar misaltuwa a tarihin siyasar Kano da Najeriya. Allah ya baka zalakar harshe da iya magana da bayani wanda duk mai sauraronka da budaddiya kuma kyakkyawar zuciya dole ya gamsu da kalaman bakinka, hakika wannan, wata baiwa ce da Allah ya yiwa mutane kalilan, sannan kuma, Allah ya kimsa maka nautsuwa da takatsantsan a tsakanin jama’a, domin a irin yadda Allah ya yi maka ni’ima ta kasancewa mai mulki ba kowa ne za’a taba mutuntakarsa ya yafe ba.

Ya mai girma Sardauna, kamar yadda tarihinka ya nuna, ka shiga siyasa ba tare da kana da wasu kudade na kuzo mu gani ba, duk da cewa a zamanin da muke ciki, tsarin jari hujja shike tafiyar da siyasa; haka ka fito takarar gwamna baka da kowa sai Allah kamar yadda kake cewa, kuma cikin ikonsa ya yi maka jagora, kana matsayin tsohon malamin makaranta kayi takara da gwamna mai-ci, da yake Allah shi ne malikul mulki ya kwace daga hannunsa ya damka maka, wannan ma wata baiwace da duk kasar nan babu wanda Allah ya yiwa irin wannan gamdakatar din, ya mai girma Sardauna, ka zama gwamna a wani lokaci da ya zowa da wasu da bazata, wadan da suke ganin cewa kai din ba kowa bane, kuma ba komai bane, sannan, wasu kuma ya zo musu suna masu kyautata zato zuwa ga mamallakin mulki.

Ya maigirma Sardauna, hakika Allah ya haskaka jihar kano da mulkinka. Jihar kano kamar yadda kowa ya sani kusan itace jagorar sauran jihohin Arewacin Najeriya, kuma jihace ta malamai musamman bangarori uku, wato ‘yan darikar Kadiriyya da darikar Tijjaniyya da kuma ‘yan Ahlussunnah ko Izala kamar yadda sunan yafi shahara, haka kuma kano, jiha ce ta ‘yan kasuwa tun usuli, jihar kano tayi fice a fannoni daban daban, sannan kuma Allah ya azurtata da salihin mutum irin Sardauna, hakika mun shaida cewa lokacin da kake gwamna kayi kokarin kamanta adalci ga musamman bangarorin dariku da muke dasu, wannan kuma, bazai hana wasu su fahimci akasin haka ba. Ka taba kusan dukkan bangarori, domin hattana nakasassu wadan da ba’aciki lura dasu a cikin al’umma ba ka jawo su ajiki inda ka nuna suma mutanene kamar kowa, wanda yafi wani shine wanda ya fi tsoron Allah, sannan kuma, a lokacinka ne mutane masu addini suka sami gata a harkar tafiyar da gwamnati, haka kuma ayyukan da ake ganin babu ruwan hukuma da su ka nuna lallai hukuma tana da ruwa da tsaki da su, kamar harkar makarantun allo da alarammomi, sanna kuma, idan ana batun ayyukan raya kasa nanma babu mai ganin baikenka, tabbas kano ta haskaka kuma ta tserewa saura ta bangarori da dama.

Ya mai girma Sardauna, lokacin da wa’adin mulkin ka na biyu ya zo karshe, jama’a da dama ciki da wajen jihar kano sunata yimaka kiraye kiraye akan ka fito takara, wasu na ganin ka fito takarar sanata wanda shine mukamin da tsaffin gwamnoni suka fiya tsayawa bayan gama wa’adinsu, wasu kuma, suna ganin ka fito takarar Shugaban kasa bisa irin yadda suke kyautata zato a gareka cewa zakayi adalci ga al’ummar Najeriya kamar yadda ka nuna a jihar kano, domin ansamu fahimtar juna da sauran kabilun kudancin kasarnan da al’ummar jihar kano a lokacinka, da kuma mabiya addinin kirista, inda har ka nada mutane wadanda ba ‘yan kanoba a cikin gwamnatinka, sannan kuma ga zaman afiya da aka samu a kusan tsawon wa’adin mulkinka. Wannan kira da al’umma suka ringa yi maka ya yi tasiri kwarai da gaske baga kai kadaiba harda sauran magoya bayanka, hardai daga karshe ka yanke shawarar tsayawa takarar shugaban kasar Najeriya.

Tabbas, ya mai girma Sardauna, kayi takarar Shugaban kasa. Kuma Allah shi ne masanin abinda bamu sani ba, wasu suna cewa, boyayyar alakace tsakaninka da gwamnatin PDP domin ka kawo cikas ga kuri’un Arewa, wanda ga duk mai hankali yasan da cewa tsarin mulkin Najeriya ne ya baka wannan dama ta tsayawa ko wane irin mukami, kuma babu wani laifi da kayi da ka tsaya wannan takara, wanda kuma yace kudi aka baka ka tsaya takara wannan tsakaninka ne da shi dakuma Allah, domin Allah shi ne masani kuma mai hikima, yasan abinda yake boye da sarari. Bayan ka kewaya kusan jihohin kasarnan domin yakin neman zabe, nasan wannan wani babban aiki ne da zaibaka damar ganin halinda yankunan kasarnan mabambanta suke ciki. Bayan da akayi zabe kuma sakamako ya fito, ance kaine kazo na uku a ‘yan takarar da suka fito daga yankin Arewa, wato na hudu kenan a kasa baki daya, Goodluck Jonathan shine wanda akace ya sami nasarar wannan zabe, sai Gen. Muhammadu Buhari a matsayin na biyu da Mallam Nuhu Ribadu a matsayin na uku da kuma kai maigirma Sardauna a matsayin na hudu. Wasu na cewa daman nasan za’a rina wai ansaci zanin mahaukaciya, wasu kuma na fadin maganganun da basuda hakikanin masaniya akansu, haka dai jama’a sukayi ta fashin baki akan wannan takara da ka tsaya, Allah dai shine masanin abinda yake fake.

Ya maigirma Sardauna, kamar yadda ka sani, tsarin siyasarmu tsari ne na jari hujja, kamar yadda ake yi a Amerika. Da yawan kananan magoya baya a yanzu suna ganin lokaci na gaba mai zuwa ka sake gwada sa’a a wannan takara ko Allah zaisa a dace; a wannan gabace nake so nayi kira ga Sardauna da cewa lallai yayi hattara da masu yi masa wannan kiran, domin shakka babu maganar takarar Shugaban kasa magance babba kuma mai bukatar abubuwa da yawa, musamman abin da akafi sani a siyasance da kayan aiki, nasan da cewa lokacin da katsaya takara ka samu gudunmawa daga ‘yan uwa da abokan arziki da magoya baya da yawa, saboda kana kan kujerar gwamna a lokacin da kake neman wannan takara. Ya maigirma Sardauna lallai yanzu kai ba mutum bane da za’a baiwa shawara akan harkar takarar shugaban kasa, saidai ka baiwa wani, duk da haka, zamuyi karambanin isar da namu sakon gareka.

Ya maigirma Sardauna a lokacin da Bashir Tofa ya tsaya takarar Shugaban kasa, a zaben 12 ga watan yuni da akafi sani da june 12, kusan yana da goyon bayan gwamnatin soja ta General Babangida a wannan lokaci amma duk da haka bai kai ga nasara ba, ko shakka babu, bama gafala da cewa wannan wani hukunci ne na ubangiji, a wancan lokaci Bashir Tofa yana da goyon baya a jihohi da dama na kasarna, sannan duk da haka Bashir Tofa ya cigaba da gwada sa’arsa domin neman wannan takara, amma Allah bai bashi nasaraba ko da kuwa tsallake matakin farko na jam’iyya, haka abin yazo har lokacin da kukayi takara tare da shi ka kuma samu galaba akansa, akaikaice wannan yana nuna cewa lallai farin jinin Alhaji Bashir Tofa ya ja baya ainun daga yadda aka sanshi a 1993. Kuma wannan yake nuna cewa kusan yanzu a siyasar Najeriya musamman ta shugaban kasa duk mutumin da ya yi takarar farko bai samu nasaraba to idan ya sake nema farin jininsa na dusashewa idan aka auna farkon fitowarsa, idan muka kalli Gen Muhammadu Buhari zamu tabbatar da haka, domin farin jinin Buhari a 2007 ya ragu kafin 2011, wannan kuma yana nuna irin yadda siyasar kasarnan ta dauki wannan salon.

Ya maigirma Sardauna, yanzu kai ka zama uban kasa, kuma uban al’umma. Hakika Najeriya tana bukatar mutum irinka, domin Allah ya baka daukaka a tsakanin sauran takwarorinka tsaffin gwamnoni, don babu wani da ake cin-cirondo dominsa sai kai, wannan kuma yake nuna cewa lokaci zaizo, kana gidanka a mundubawa Najeriya zata nemi agajinka, domin sanin kowa ne, idan al’amura suka rincabe dole a bukaci mutane wadan da zasu iya magana a sauraresu, wadanda kuma suke da zalakar harshe, wanda kuma maganarka tanada matukar tasiri a tsakanin magoya bayanka da kuma sauran al’ummomin kasarnan.

Maganar takarar shugaban kasa a nan gaba, ya mai girma Sardauna tana bukatar a tsaya ayi mata duba na tsanaki. Shakka babu kamar yadda na fada kai ba mutum bane da za’a baka shawara akan wannan batu saidai ka bayar, kuma nasan yanzu kana iya rubuta babban littafi mai sufulai da yawa idan ambaka maudu’i akan hakan, don haka ga masu yin kira cewa ka fito takara a 2015, lallai a duba wannan batu, kai tsaye bazance kada maigirma sardauna ya sake yin takara ba, haka kuma bazan ce kada yaki tsayawa takaraba, amma dai abinda masu iya magana ke cewa kana kallon tarihin rayuwar wasu domin samun yadda zaka inganta taka, hakika wadanda suka gabaceka zasu zama ishara a gareka, da sauran al’umma.

Daga karshe, ina mai yin fatan alheri a gareka, kuma ina rokon Allah yacigaba da yi maka jagoranci, ya shiga tsakaninka da makiyanka da kuma mahassada, Allah ya zaba maka abinda ya ke shine mafi a’ala a gareka da kuma al’ummar jihar kano da Najeriya baki daya, wassalam ka huta lafiya.

Yasir Ramadan gwale

yasirramadangwale@yahoo.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

Friday, April 6, 2012

Hukumar Hizba Ta Jihar Kano Kada Wankin Hula Ya Kaiku Dare



Umarni da kyakkyawa da Hani ga mummuna, kusan shi ne jigo ko kashin bayana aikin Hukumar Hizaba ta jihar kano. Kamar yadda muka sani, wannan jigo na aikin Hizba, kusan Hadisi ne na manzo salallahu alaihi wasallam, aka fassarashi, kuma ya kasance hadafin hukumar tun lokacin da aka samu matasa masu kishin addini ‘yan sa kai suka assasata, da nufin motsa zukatan masu kishin addini, da kuma neman gwamnati ta aiwatar da shari’ar Musulunci a jihar kano a shekara ta 2000 kamar yadda akayi a zamfara; aikin hukumar Hizba kamar yadda muka sani ba sabon abu bane a musulinci.

A wancan lokaci, matasan da suke aikin Hizba a jihar Kano, suna yi ne na sa kai, wato babu wanda ake biya ko anini, hasalima sune suke yin karo-karo domin samar da kudin gudanarwa a unguwanni da kananan Hukumomi, anga mutane irinsu marigayi Sheikh Jafar Mahmoud Adam sanye da kayan Hizba a wajen wa’azozin neman kafa shari’a a wurare irinsu Majalasin Triumph da Masallacin Umar Bin Khattab da sauran gurare a fadin Jihar kano.

Bayan duk abin da ya faru ya faru na gwagwarmayar tabbatar da shari’ah a kano, kuma akaci nasarar kafata, gwamnatin Injiniya Rabiu Musa kwankwaso a wancan lokacin, batayi nisan kwana ba, wannan ce ta bada kofa ga gwamnatin Mallam Ibrahim Shekarau, da daukin jama’a na ganin aiwatar da sharia a kano. Da mallam Shekarau ya zo ya nemi majalisar dokoki ta jihar kano tayi dokar da zata kai ga kafa Hizba a Hukumance ta yadda babu wani da zai iya yi mata barazana ko katsalandan, gwamnatin tayi kokari wajen gyara tare da tsarkake Hukumar hizba tare kuma da mayar da ita tayi dai-dai da zamani, wannan ta sanya akayiwa dakaru kusan 9000 a mazabu da kananan hukumomi da kuma jiha rejista tare da sama musu albashi na kusan Naira 15000 a kowane wata, tare da babban kwamanda guda daya, a mtsayin jagora. Kusan aikin Hizba yana tafiya kafada da kafada ne da Hukumar Shari’ah ta Jihar Kano. Kusan duka aikinsu mai taimakon sashe ne, wajen ganin al’amuran shari’a sun inganta, tare kuma da dawo da tsoron Allah a zukatan jama’a. Madallah da wannan aiki na Hukumar Hizba mai dumbin lada.

Yanzu kamar yadda kowa ya sani, babban aikin da Hukumar Hizba ta sanya a gaba shi ne na aurar da zawarawa kusan 1000 a jihar kano. Mallam Muhammad Aminu Ibrahim Daurawa, shi ne babban kwamandan Hizba na jihar kano, tare kuma da manyan mataimakansa guda uku da kuma takwararsa ta bangaren mata da sauran masu taimaka musu, da kuma kwamandoji na kananan hukumomi 44 na jihar Kano. A wani lokaci a can baya a lokacin da Gwamnan jihar Gombe Muhammad Danjuma Goje ya gayyaci Mallam Aminu Daurawa zuwa buda baki da Azumi a gidan gwamnati, ya yi wasu kalamai na gugar zana ga ita hukumar Hizba ta jihar kano, sannan kuma a wasu wa’azozi nasa ya zargi hukumar da gazawa wajen iya tafiyar da aikinsu.

Hukumar Hizba tayi wannan tanadi ne, na rage adadi na yawan zawarawa dake lungu da sako na jihar Kano. Hukumar tayi tanadi, na baiwa duk wanda zaiyi wannan aure sadaki da kuma kayan daki da wasu kayayyaki na koya sana’o’i ga matan da za’a aurar, Kamar yadda aka ce hukumar, tana kokarin tantance zawarawa mata da kuma maza wadanda za’a daura wannan aure da su. Kusan rahotanni sun nuna cewa da yawan matan da za’a aurar basu san wanda za’a aura musuba; kamar yadda wakilin BBC na jihar kano ya zanta da wasu da suke jiran tantancewa ya fada. Tambaya ga hukumar Hizba, shin tayaya ake tsammanin dorewar auren da mata da mijin basu gama fahimtar juna ba? Ganin cewa ba ‘yan mata bane balle a ari bakinsu a ci masu albasa, sannan kuma, shin idan andaura wannan aure wane tabbaci suke da shi na cewa auren bazai sake mutuwa ba? Menene matsayin mutumin da hukumar ta yiwa auren kuma daga baya ya saki matar? Ina matsayin kudadan da aka kashe domin hidimar wannan aure? Misali ka dauka cewa duk wanda zaiyi auren hukumar zata taimaka masa da 10,000 a matsayin sadaki, kaga kenan zata kashe kusan Miliyan 10, a sadaki kawai, sannan sukuma bangaren matan, da kayan daki da na sana’a ka dauka cewa za’a kashewa kowacce 50,000, kaza za’a kashe akalla miliyan 50, sannan kuma da kudin da hukumar zata kashe wajen aiwatar da wannan aure.

Duk wadan nan kudade zasu fito ne daga asusun gwamnatin jihar kano, wanda ya nuna cewa lallai kudin al’umma ne! Shawarata anan ga hukumar Hizba shi ne da wadanan kudade da za’a kashe, da mutum 200 farko aka inganta aurensu tare da baiwa mazajen jari ko kayan sana’a wadan da zasu iya daukan dawainiyar wannan aure, domin idan hukumar Hizba batayi hankali ba garin neman gira sai ta rasa idanu, kamar yadda sukace shi mijin za’a taimaka masa da sadaki, ita kuma matar za’a taimaka mata da kayan sana’a, shin me wannan yake nunawa? Ita matar ita zata rike kanta kenan? Zata dauki dawainiyar kanta da mijinta kenan? Idan har banyi kuskureba haka batun yake, cewa matan za’a taimakawa da kayan sana’o’i tabbas sunan wannan aure sakakke domin babu yadda aure zaiyi karko a irin wannan yanayi na mace ita ke da gida. Lallai hukumar hizba ya kamata tayi duba na tsanaki a kan wannan batu.

Sannan, wannan batu na auren da hukumar zatayi, idan basubi a hankali ba shi ne zai dauke hankalin hukumar kusan tsawon wa’adinsu. Domin tabbas su shirya jin koke da korafe-korafe ga wadan da aka aurar, domin a irin yanayi na mallam Bahaushe, duk abinda ya samu a bagas kamar yadda turawa ke cewa at aplata gold bai cika bashi muhimmanci da kimar da ta dace da shi ba, kaga kenan, angama da wannan kaso na mutu 200 ana shirin na wasu 200, sannan ga na farko sun fara zuwa da korafi, ina sake jaddadawa tabbas sai hukumar ta sami korafi musamman daga matan da aka aurar, domin duk matar da ta sami matsala ba gidan ubanta zata nufaba, hukumar zata nufa, kaga kenan ana yunkurin daura wani daga gefe guda kuma ana kokarin sasanta na baya don gudun sakwarkwacewa, Allah ya kiyaye.

Idan kuma muka shiga cikin hukumara Hizbar, zamuga irin yadda korafi ya yi yawa na korar da yawa daga cikin ‘yan Hizbar da wannan gwamnatin ta gada daga gwamnatin baya ta Mallam Ibrahim Shekarau. Daman kuma an zargi gwamnatin PDP ta Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso tun farkon hawanta cewa za ta kori ’yan Hisba bisa zargin sun taka rawa wajen goya wa gwamnatin Malam Ibrahim Shekarau baya a lokacin zaben da ya gabata, tare da kokarin ganin wannan gwamnati ba ta kai ga nasara ba. Domin yanzu haka rahotannin da suke fitowa daga hukumar suna nuna cewa ansauke dukkan kwamadoji na kananan hukumomi 44 da wannan gwamnati ta gada, sai dai kuma, kamar yadda mataimakin kwamanda ya kare wannan batu da cewa tunda ansamu sabon kwamanda a jiha ya zama tilas, a kananan hukumomima a samu sabbin kwamandoji, yace wannan al’adace ta sauyin kowace irin gwaamnati.

Sannan kuma, hukumar ta bullo da wani shiri na tantance dakarunta inda ta ce ta yi hakan ne don tsabtace hukumar, amma sai wadansu daga cikin ’yan Hisbar suka ki a tantance su bisa zargin an shirya haka ne da boyayyiyar manufa ta a ci musu mutunci suna zargin cewa akwai shugabannin Jam’iyyar PDP na kananan hukumomi a cikin aikin. Hakika mun kyautata zato ga sabon babban kwamanda Mallam Aminu Daurawa, amma kuma kada wannan ya tabbata cewa suma suna siyasa in da rahotanni suka nuna kamar anayin bita da kulli ga ‘yan Hizbar, domin yanzu zancen da akeyi ance ankori kusan mutum 2,357 daga aiki a kananan hukumomi 23 da suka hada da Makoda da Madobi da Warawa da Fagge da Albasu da Tsanyawa da Sumaila da karaye da Rogo da sauransu. Sannan ba’a bayar da bayanin cewa su wadan nan da aka kora ma’aikatan bogi bane, idan har wannan ba bita da kulli bane me ye dalilin da zaisanya a kori wadan nan mutane daga aiki? alhali da yawa daga cikinsu sun dogara da wannan aiki da sukeyi kasancewar suna da iyalai.

Kamar yadda suka ce, an zargi da yawada daga cikin ‘yan Hizbar da sanya baki a siyasa. Musamman kwamandoji na kananan Hukumomi da ake musu kallon sun dafawa gwamnatin da ta gabata ta mallam Ibrahim Shekarau, amma kuma kamar yadda Mataimakain babban kwamanda na jiha Dr Maigida Kacako yace hukumar bata hana kowa yabi ra’ayinda yake so a siyasa ba, amma kada ya yi amfani da aikin Hizba a siyasa, idan har da gaske hukumar take, suke akan wannan batu, to da alama suna tufaka suna warwara. Allah shi ne maSani mai hikima.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@yahoo.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

Thursday, April 5, 2012

James Ibori: Makaho Baisan Ana Ganinsa ba . . .


James Ibori: Makaho Baisan Ana Ganinsa ba . . .

James Ananebo Ibori kamar yadda aka sanshi, bayanai sunce, yana daga cikin hamshakan attajirai a Najeriya na gani na fada. Shi dai dan siyasa ne, kuma me mai fada aji a tsakanin mutanansa da jam’iyyarsa ta PDP, domin kusan anyi ittifaqin duk kasarnan babu wani mahaluki da ya taimaka da irin kudin da ya baiwa tsohon shugaban kasa Mallam Umaru Musa ‘YarAdua, domin yakin neman zabe kamarsa, bayanai sunce ya taimaka da kazaman kudade da sun shallake hankali da tunani. Wannan ce ma ta sanya aka nada babban yaronsa kuma na hannun damansa Mista Mikel Kaase Aandoakaa a matsayin babban Atoni janar kuma ministan shari’a, na Najeriya, inda ya yi ta cin karensa babu babbaka a gwamnatin YarAdua, bayanai sun tabbatar da cewa, kusan yana daya daga cikin masu juya gwamnatin tarayya daga nesa, inda yaransa ko makusantansu sukayi dumu dumu a harkar gwamnatin tarayya.

Bayanai sun tabbatar da cewa Ibori ya nemi kariya ne da gwamnatin marigayi YarAdua domin boye irin kazamar satar da ya dibga, don haka ne yasa aka tabbatar masa da wannan kariyar da yake nema ta hanyar nada na hannun damansa a matsayin ministan sharia, domin bashi kariya daga gurfana gaban kowane irin kwamitin bincike. Ana zargin Ibori, da yin sama da fadi, da dukiyar al’ummar jihar Delta dake yankin kudu maso kuduncin Najeriya, kuma yankin da yake samar da albarkatun manfetur da dangoginsa.

James Ibori shi ne gwamnan Jihar Delta daga 1999 zuwa 2007, bayanai sunce, ya wawure kudi da suka kai sama da dalar amurka miliyan $250 kwatankwacin kudin kasar ingila Fan miliyan £157 a kudin Najeriya sama da Naira Biliyan 45, saboda kariyar da yake da ita na tsarin mulkin Najeriya na gurfana a gaban kotu a lokacin da yake gwamna, wannan ta sanya tsohon shugaban hukumar EFCC Mallam Nuhu Ribadu, ya baza koma, domin kamo wannan gawurtaccen barawo, anci nasarar kama Mista Ibori a lokacin da wa’adin mulkinsa ya kare kuma yake shirin bajakolinsa a gwamnatin da kusan za’a iya cewa shine jigonta, hakika bayanai sunce Mallam Ribadu ya yi matukar kokari wajen ganin antatse mista Ibori domin maida kudin da ya sata zuwa aljihun gwamnati, inda shi da kansa Iborin ya yi kokarin baiwa Ribadu cin hancin dalar amurka miliyan $15, sai dai, da yawan manazarta suna ganin wannan ce ta sanya akayiwa Mallam Nuhu Ribadu wulakancin da ba’a taba yiwa wani mutum a Najeriya ba kawai don yana kokarin ganin ankame tare da garkame manyan barayi, irinsu Ibori, da farko anfara yiwa Ribadu bitada kulli, ta hanyar cewa, ya koma makaranta ya karo ilimi a kuru dake Jos, aka maye gurbinsa da Madam Farida Waziri, kuma bayanai sun tabbatar da cewa umarnin da aka fara baiwa ita waziri shi ne ta saki Ibori, wannan ta bashi dama inda ya sanya aka dinga yiwa Mallam Nuhu Ribadu wulakanci da bita da kulli na fitar hankali, wannan ta sa Ribadu ya bar kasarnan ba don yana so ba, inda ya tafi gudun hijira zuwa kasar Birtaniya don kare kansa. Kuma saboda karya ake wajen yakar cinhanci da rashawa, wai kotu ta wanke Ibori daga tuhume-tuhumen da EFCC ta ke yi masa.

Kwatsam babu zato babu tsammani, aka kwashi tsohon shugaba YarAdua ranga ranga zuwa kasar Saudiyya domin neman magani. Bayanai sunce halin da shugaban kasa a wancan lokacin yake ciki sun tsananta, Wannan ce ta sanya hantar Ibori da ‘yan kanzaginsa ta kada, kuma cikinsu ya duri ruwa sosai, domin da aka samu tirka-tirkar yiwuwar nada mukaddashin shugaban kasa ministan Sharia Mista Aandoakaa yana sahun gaba wajen adawa da nada Goodluck Jonathan a matsayin mukaddashin shugabansa, da hakarsu ta kasa cimma ruwa Ibori ya gudu kasar Dubai inda shi kuma Aandoakaa ya nufi kasar Amerika domin sunsan bazasu kwashe da dadi da mista Jonathan ba ganin irin cinkashi da wulakancin da sukayi masa, yana matsayin mataimakin shugaban kasa. A gefe guda kuma hukmar ‘yan sandan Birtaniya(Metropolitan Police) suna neman Ibori ruwa a jallo inda akaci nasarar damkeshi a shekarar 2010 a kasar Dubai, tare kuma da tasa keyarsa zuwa kasar Birtaniya domin fuskantar shari’ar zambar kudaden Haram.

A lokacin da Mallam Nuhu Ribadu yake binkitar almundahanar da Ibori ya tafka, ya hada kai da hukumar ‘yan sandan duniya ta INTERPOL domin taso keyarsa duk inda ya shiga, haka kuwa akayi anci nasarar kama Ibori inda aka tasa keyarsa zuwa kasar Birtaniya domin yi masa shari’a akan zarginsa da hallata kudaden haram da suka shallake hankali, alokacin da ya gurfana ya amsa laiffufuka 10 acikin 22 da ake zarginsa da aikatawa, wannan kuma ta tabbatar da ya karyata kansa kamar yadda a baya yaki amsa wadan nan laifuka, ya yarda cewa yayi almundahana da dukiyar jihar Delta kuma ya halatta dukiyar Haram; mai gabatar da kara Sasha Wass ta shaidawa kotun lardi ta Southwark crown court dake birnin landan cewa James Ibori ya amsa laifi 10 daga cikin 22 da ake tuhumarsa da aikatawa na almundahana da dukiyar jihar Delta a lokacin da yake Gwamna.

Wass taci gaba da shaidawa kotu cewa Ibori ya yi amfani da takardun haihuwa na karya, domin boye laifin da ya aikata a baya, da ya hana masa rike kowanne irin mukami na gwamnati, a lokacin da yake neman takarar gwamnan jihar Delta, ta kara da cewa muna murna da wannan amsa laifi da Ibori ya yi domin wannan shi ne zai kawo saukin shari’ar da ake yi masa, kuma tace za a kwace tare da mika kadarorin da ya mallaka a kasar Birtaniya, zuwa jiharsa ta Delta kamar yadda dansandan da ya gabatar da kara Paul Whatmore na hukumar ‘yan sandan birnin landa wato Metropolitan police ya nema, dan sandan yace zasu ci gaba da sanya ido akan kadarorin da Ibori ya mallaka a kasar ta Birtaniya.

James Ibori dai kafin zamansa gwamna, a shekarar 1999 yana zaune ne a Primrose Hill a Arewacin Landan a Birtaniya, kuma yana aikin akawu ne a DIY store in Ruislip, Middlesex, bayanai sun tabbatar da cewa ibori ya mallaki katin fitar da kudi na Credit Card, da yakai kimanin dalar Amurka $200,000 a wata, kuma ya mallaki wasu irin dirka dirkan motoci masu dankaren tsada da ake kira Range Rover, kuma wani karin abin mamaki a lokacin da Ibori yake a tsare a Landan yayi yunkurin sayan wani karamin jirgi mai cike da kayan alatu da yakai kimanin fan na ingila miliyan 20.

Saboda irin facakar da yake tafkawa a kasar Birtaniya, da kasashen turai hukumar ‘yan sandan birtaniya karkashin sashin proceeds of corruption unit (POCU) suka fara bincikarsa tun a shekara ta 2005 tare da hadin gwiwar hukumar EFCC ta Najeriya wadda Mallam Nuhu Ribadu ya jagoranta a wancan lokacin. Haka itama a nata bangaren kungiyar nan ta DFID tace ta sanya ido akan James Ibori musamman ganin irin yadda yake ta jibge makudan kudade a kasashen Turai da Amurka da Dubai.

Irinsu james Ibori yanzu suna nan jibge a Najeriya. Sun dibga mahaukaciyar sata kuma suna shiga siyasa da nufin samun kariya domin boye irin mummunar satar da suka dibga. Don haka duk wani shugaba na gari da ake fatan samu a Najeriya matukar ba wanda zai iya yakar cin hanci da rashawa bane, to, ya zama aikin banza, domin haka irinsu Ibori zasu cigaba da cin karensu babu babbaka a karkashin gwamnatin da suka taimakawa da dukiyar sata. Allah ya bamu shugabanni na gari, masu kishin kasa kuma wadan da zasu iya yakar cin hanci da rashawa, Allah ya kawo mana Su.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@yahoo.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com