Friday, October 23, 2015

Ranar Ashoora


RANAR ASHURA: A Galibin kasashen larabawa da gabashin Afurka, watan Zul-Hajj ya kare a 29 ne da ya gabata, inda a lissafi yau Juma'a ta zama 10 ga sabon watan Muharram Hijira 1437 (Ashura). Yayin da a Najeriya watan Zul-Hajj ya cika kwana 30 dan haka yau Juma'a ta zama 9 ga watan Muharram  (Tasu'ah). Malamai da dama sun sha yi mana bayani akan ranar Ashura da falalar azumtarta a addinin Musulunci, a gefe guda kuma, Malamai kan fadakar akan wata gagarumar Bid'ah wanda b'ata ne mabayyani da 'yan Shiah suke yi kuma suke jingina shi ga Musulunci. Dan haka, kamar yadda malamai suka sha fadakar da mu kusan duk Shekara a irin wannan lokaci, duk abinda 'yan Shiah suke yi bata ne kuma kafurci ne, ba Musulunci bane, ba kuma koyarwar addinin Mu lunch bane. Waki'ar da ta faru ga Jikan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam Alhussain Ibn Aliyu Bin Abi-Talib, Malamai sunyi bayani da dama akai, wannan kokarin jingina kansu da Hussain Ibn Ali Allah ya kara yarda da su shi da mahaifinsa, karya Shiah suke ba suda Alaka da su ko ta kusa ko ta nesa, hasalima su Shiah suka kashe jikan Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam. Ya Allah ka bamu cikakken Ladan wannan ibada. Ya Allah al'ummar Musulmi na fama da wani mugun ciwo na Shiah Allah ka darkakesu ka wargazasu, Allah ka dammarasu ka hana musu yaduwa, Allah ka kare al'ummar Musulmi daga wannan masifar ta Shiah. Allah ka amshi wannan Ibada da muka yi domin neman yardarka. 

Yasir Ramadan Gwale 
23-10-2015

Wednesday, October 21, 2015

Dr. Goodluck Jonathan: Sabon Malamin Siyasar Kasar Tanzania


Dr. GOODLUCK JONATHAN: SABON MALAMIN SIYASAR KASAR TANZANIA 

Wani hanin ga Allah baiwa ne,  inji 'yan magana. Idan ya karbe ta can sai ya baka ta nan. Yanzu dai ance Mista  Goodluck Jonathan shi ne zai jagoranci wata kakkarfar tawagar kwararru domin sanya ido akan yadda za'a gudanar da zaben Shugaban kasa a Tanzania. Tuni rahotanni suka nuna irin kyakkyawar tarba da maraba lale da akaiwa Mista Jonathan a Arusha, ba da jimawa ba kuma aka ce Jonathan ya shiga aiki ka ' in da na ' in wajen yin kira ga 'yan siyasa da masu takara a Tanzania da su sanya kishin kasarsu akan ra'ayinsu. 

Ba shakka har yanzu ina samun nutsuwa da gamsuwa cewar tsohon Shugaban kasa Dr. Goodluck Jonathan ba yadda da yawa suka dauke shi haka yake ba. Ina ganin mutum ne mai saukin kai da saukin Mu'amala. Ya iya jure yadda da kaddara mai matukar wahala a sahun mutane irinsa. Yayi abinda Shugabanni da yawa a Afrika har da Nigeria basu yi ba, dan haka ne, duniya ta jinjina masa, kuma, aka yaba masa, bisa wannan namijin kokari da yayi na karbar kaddarar faduwa zabe. Har hakan ta kaishi ga samun wannan mukami. Haka zalika, har yanzu sabon Shugaban kasa Muhammadu Buhari bai dena yabawa wannan namijin kokari na Mista Jonathan ba.

Goodluck Jonathan ya nuna misali a Afrika wajen nuna kishin kasarsa da nuna cewar maslahar 'yan Nigeria tafi maslaharsa. Ko da kuwa za a gwale shi ace yaga babu sarki sai Allah shi yasa ya karbi kaddara, hakika yayi abin da ya saya masa mutuncin da kudi ba zasu iya Saye ba. Muna fatan Kullum 'yan Najeriya su kasance abin misali a Afrika wajen nuna kyawawan halaye da mutunta ra'ayin mafiya rinjaye. Ina fatan Allah ya masa jagoranci a wannan aiki yasa 'yan takara a Tanzania suyi koyi da shi (Goodluck Jonathan) wajen karbar dukkan sakamakon da yazo na gaskiya daga hukuma. Allah ya taimaki Najeriya. 

Yasir Ramadan Gwale 
21-10-2015

Thursday, October 15, 2015

Malaman Sunnah Sun Ki Jin Magana ta . . .


MALAMAN SUNNAH SUN KI JIN MAGANA TA . . .

Na karanta bayanin wani dan yaga riga a facebook, yana kalubalantar Malaman Sunnah, akan, dan me, ya jima yana kiransu da su shiga harkokin siyasa, amma sunki, a cewar sa,  ya sha gaya musu, ba sau daya ba, kuma ba sau biyu ba, amma sunki jin kiran sa.  Ya kuma kalubalance su a akan dan me basu taimakawa Shugaban kasa ba a lokacin da yake yakin neman zabe. 

A cewar sa,  ya auna ya gano, sam Malaman basu fadakar da mabiyansu ba a akan su zabi Buhari, yace yayi ta kira amma Malaman sukai shakulatun bangaro da batun sa. Ya cigaba da cewar yana da masaniyar cewa fa 'yan Siyasa suna baiwa Malaman kudi da motoci, kuma yace da idonsa ya hango wasu a Umra, Goodluck Jonathan Mai Nasara,  ya kai su dan suyi wa Najeriya addu'ah. 

A cikin soki burutsun nasa, yace, ku Malamai ku sani fa, dan kafi mutum ilimin addini ba shine yake nuna ka fishi kwakwalwa ba. Sannan ya yabawa Adamu Adamu a kokarin sa na ganin kasar sa ta fita daga halin cin hanci da karbar rashawa da samun mafita a harkar tattalin arziki, ya yabawa Adamu Adamu akan wannan kokari nasa, a daidai lokacin da ya kwarewa Malamansa da yake jingina kansa garesu cewar basu ji irin kiraye kirayen da ya dinga yi musu na su ja hankalin mabiyansu su zabi Buhari ba.

Wannan dan hauragiya yayi ta rambatsu yana aibata Malaman Sunnah da yake jingina kansa garesu, duk kuwa da ta bayyana a fili wasu daga cikinsu da yake muzantawa sun tsunduma kansu cikin siyasa tsundum kuma jam'iyyar da yake wa fatan taci zabe, kuma taci din. Wannan dan harbatamati yayi ta soki burutsu da hayaniya da nuna rashin kunya ga Malaman Sunnah. Kalaman sa na rashin ladabi, ba boyayyu bane musamman ga Babban Malamin Tafsiri na Kaduna Sheikh Dr Ahmad Abubakar Mahmud Gumi da aibata shi da nuna cewa shi yafi Malamin Sanin addini da sanin Sunnah.

Irin wadannan yan jagaliya basa bukatar Nasiha ko Jan hankali,  a biyo masa ta inda ya shigo zai Fi gane wannan yaren. 

Wannan somin tabi ne.

Yasir Ramadan Gwale 
15-10-201

Monday, October 12, 2015

Mugun Nufin 'Yan Shiah Akan Musulmi Da Sunan Aikin Hajji


MUGUN NUFIN 'YAN SHIAH AKAN MUSULMI DA SUNAN AIKIN HAJJI 
 
Su 'yan Shiah ba gaskya bace da su, ba kuma gaskiya suke bi ba, illah kawai makauniyar biyayya da suke yiwa kasar IRAN. Shi yasa sau da yawa zaka samu mabiya Shiah suna b'oye shi'ancinsu, sai fa wadan da asirinsu ya tonu babu yadda zasu yi. Sabinin mu mabiya Sunnah bamu tab'a b'oye Aqidarmu ba, bama shayi ko shakkar wani ko wasu su kiramu da sunan Aqidarmu ko su jinginamu zuwa gareta, ba zaka tab'a ganin wani Ahlussunnah yana kyamar a ce masa 'Dan Izala ko Wahabi ba, domin munyi Imani da Allah kuma mun kyautata masa zaton cewar ba zai tabar da mu ba, dan haka ne muke da yakini cewar ba'a kan hanyar b'ata muke ba.

Ko su kiramu Wahhabiyawa ko 'yan Izala ko duk wani suna da zasu jingina mana, mun yarda kuma mun Amince cewar mu din mabiya Sunnah ne, bama b'oyewa, bama kuma, kin amsawa. Amma har anan Facebook mun sansu da yawa, suna Shiah amma suna b'oyewa, basa son ko kadan a sani. Kaga wannan hujja ce ta cewar sun yi Imani Aqidarsu ba gaskiya bace, kuma b'ata ce, domin indai gaskiya mutum yake bi, baya tab'a shakkar bayyana hakikanin abinda yake bi na Aqidah.

A sabida haka, mabiya Shiah sun san ba gaskiya suke bi ba, kuma ba suda wata manufa, Illa ta kare muradun kasar Iran da yin biyayya ga duk abinda ta zo musu da shi; yasa suka dauka kowa ma haka ne. A dan haka ne, sai suke kokarin Jinginamu ga Sa'udiyya a matsayin masu biyayya a gareta Ido rufe kamar yadda suke yiwa Iran Biyayya Ido rufe.

Amma a zahirin gaskiya mu mabiya gaskiya ne, mabiya Sunnah, ba wai Saudiyya muke wa biyayya Ido rufe ba. Sai dai a bayyane take a zahiri a garemu cewar kasar Sa'udiyya kasa mai tsarki, kasa ce ta Sunnah, kuma tafi kusa da kwatanta gaskiya da bin Sunnah da yada da'awar Sunnah, dan haka muke tare da su a duk wasu abubuwa da basu sabawa Sunnah ba.

Kasancewar Daular Sa'udiyya daula ce ta Sunnah, shi yasa a mafiya yawancin lokaci al'amuransu sukan dace da koyarwar Sunnar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam. Sanin kowa ne, kasar Sa'udiyya bata goyi bayan Gwamnatin Mursi a Masar ba, amma da yawanmu mukai hannun riga da ita akan batun Mursi. kuma kusan kowa yaji matsayarmu ta bakin Sheikh Dr. Sani Umar Rijiyar Lemo dan gane da abinda akaiwa mursi.

Amma duk da haka su 'yan shiah sai basa ganin wannan, suke nunawa duniya cewar mu din ido rufe muke biyayya ga Sa'udiyya kamar yadda ba suda wata manufa sai abinda Iran tace, SUNA MATA BIYAYYA DA DUK ABINDA TA ZO DA SHI. yana daga cikin manufar Iran mayar da Musulunci yayi kamanceceniya da Kiristanci, domin dusashe haskensa, wannan shi ne mugun nufinsu, shi yasa mukaji a wannan lokacin, suka dinga kiran tilas aikin hajji ya koma karkashin kulawar dukkan musulmi ba wata kasa guda daya ba. Duk wanda kaji da wannan furuci, ya sani ko bai sani ba, da yawun Iran yake magana.

Asali su kiristoci mafiya rinjaye suna karkashin Fadar Vatican ne, wadda Paparoma yake jagoranta. Wato Paparoma ba wai kawai shugaban addini bane, domin ita kanta Vatican kasa ce, kuma duk wani Paparoma shi ne shugaban kasar Vatican, a sabida tsarin da suke da shi na yin hadakar kiristoci baki daya wajen tafiyar da duk wani al'amari da ya shafi fadar vatican, shi yasa zaka ji an wayi gari mutumin kasar ARgentina ko Germany ko Poland zai iya zama Paparoma kuma Shugaban kasar vatican.

To misalin irin wannan shi ne manufar Iran akan Musulunci, su mayarda musulunci kamar Kiristanci, ta yadda za'a wayi gari watan wata rana ace mutumin IRAN, HEZBOLA shi ne zai zama shugaba ko sarki da yake kula da biranen Makkah da Madina, shi yasa a wannan lokaci 'yan korensu da 'yan kanzaginsu ke ta yayata cewar tilas shiryawa da gudanar da aikin hajji ya zama mas'uliyya ce ta dukkan musulmi ba Sa'audiyya ita kadai ba. Wannan ita ce manufarsu.

Me kake jin zai faru idan Makkah da Madina suka kasance karkashin jagoranci 'yan Shiah mutanen Iran? Dan haka duk wani me kururwar cewar tilas shirya gudanar da aikin hajji ya zama karkashin kulawar musulmin duniya, to wallahi ya sani ba tunaninsa bane, kuma ba ra'ayinsa bane, wannan shiryayyen al'amari ne da Iran ta shirya, take amfani da 'yan barandanta na sarari da na boye, suke yad'a wannan kururuwar da masu raunin tunani zasu ji kamar akwai gaskiya a cikinta. Babu gaskiya ko ta kwabo illa kokarin sauya tafarkin addinin Allah na gaskiya.

Domin duk lokacin da aka ce ai musulmi ne gaba daya zasu saka hannu akan gudanar da Hajji, to za'a wayi gari kuma, suce ai makkah da madina na musulmi ne duka, dan haka dole musulmi su yi musharaka wajen tafiyar da jagorancin wadannan birane masu tsarki. ya Allah kada ka cika musu wannan buri nasu, ya Allah kada ka basu dukkan wata dama akan al'ummar musulmi. Allah ka taimaki Sunnah da Ahlussunnah ka rusa Shianci da kafurci da duk masu mara musu baya, na sarari da na boye.

Yasir Ramadan Gwale
12-10-2015