Thursday, February 4, 2016

Ziyarar Da Na Kai Cibiyar Addinin Musulunci Ta Al'umma Dake Garin Baltimore


ZIYARAR DA NA KAI CIBIYAR ADDININ MUSULUNCI TA GARIN BALTIMORE

Daga Barack Obama

A yau, cikin ikon Allah na samu zarafin kai ziyara ga katafariyar cibiyar addinin Musulunci ta al'umma dake garin Baltimore. Naga Masallaci inda dubban Musulmi Amerikawa ke haduwa da juna da iyalai dan gudanar da Ibada kamar ko wane irin Masallaci a Amurka, cibiyar waje ne inda dangi da makwabta kan hadu tare da juna suna gudanar da ayyukan Ibada na addini, ga makaranta da yara kan koyi Ilimin addini da zamantakewa, sannan ga sashin bayar da agajin gaggawa, naga mutane da dama da suka bayar da lokacin su kyauta domin aikin hidimtawa al'umma.

Wannan ziyara tawa, wata muhimmiyar dama ce a wajena da zan ganewa ido na yadda Musulmi ke aiwatar da alamuransu na addini, sannan na karfafa musu guiwa wajen taimako da ayyukan sa-kai, sannan kuma na tuna musu cewar Musulmi da yawa sun bayar da gudunmawa mai dumbin yawa a baya domin ciyar da wannan kasar tamu gaba. Kuma wannan ne Babban dalilin da yasa kasarmu abin alfaharinmu ta daukaka a duniya, domin kowanne dan Adam yana da 'yanci da kuma ikon yin addinin sa.

Al'ummatai da dama na Musulmi musamman daga cikin Manoma da 'yan Kasuwa da masu sana'o'i da dama suka taimaka wajen gina tare da bunkasa habakar wannan kasa tamu. Su ne suka taimaka wajen ilmantar mana da 'ya 'yanmu, da yawansu daga masu aikin jiyya da likitoci sun hidimtawa al'umma a wannan kasa ta Amurka. Wasunsu da dama sun samu lambobin Yabo bisa wasu ayyuka da suka na bajinta, ciki kuwa har da karbar lambar Yabo ta zaman lafiya wato Nobel Peace Prize.

Haka kuma, dumbin matasan Musulmi Amurkawa sunyi abubuwa na bajinta da suka Shafi fasaha da kimiyya da kirkire kirkire. Wannan ce ta sanya a koda yaushe mukan hadu domin nuna jinjina da godiya ga irin wadannan matasa, daga cikinsu kuwa, akwai irinsu Mohammed Ali da Kareem Abdul-Jabbar, wanda suka sanya farin ciki da annashuwa da dama a zukatan al'ummarmu. Daga cikin Musulmi a Amurka akwai, 'yan kwana-kwana wanda suke sadaukar da rayuwarsu dan kashe duk wata gobara. Sannan ga kuma 'yan sanda mata da maza wanda suke aiki tukuru dan kasarmu.

Yanzu haka, Musulmi da dama anan Amurka na cikin zullumi da damuwar taka musu hakki ko cin zarafinsu. Iyaye da 'ya 'ya na ta karakaina cikin tsoron taka musu martaba da mutunci, to ya ku ina mai tabbatarwa da duk wani Musulmi a Amurka ba Baltimore kadai ba cewar mu duka Amurkawa ne, kuma mu al'umma daya ne, dan haka duk wanda zai kaiwa Musulmi hari anan to ya sani mu duka gaba dayanmu ya kaiwa hari.
Dan haka, duk wani tsagera ko mara kunya da zai ci zarafin Musulmi akan addinin sa to ya sani ya shirya fada da mu ne baki daya, kuma zamu tsaya kai da fata wajen ganin bamu bari anci zarafin Musulmi a Amurka ba, kawai dan sunce su Musulunci zasu yi. Haka nan kuma, zamu yi fatali da duk wani tsarin siyasa da zai cuzgunawa Musulmi, zamu yi magana da murya daya, ba tare da mun cutar da wani ko wasu al'umma ba akan addinin su. Kuma yana da kyau duknamu mu sani cewar gaba dayanmu daga Allah muke kuma gareshi zamu koma.

A saboda haka, ina amfani da wannan dama na tabbatarwa da dukkan Musulmin Amurka maza da mata cewar, kowannenmu yana da iko da 'yancin da doka ta bashi a matsayinsa na dan kasa. Ku din nan ba wai kawai Musulmi bane ko Amerikawa a'a ku Musulmin Amerika ne, kuna da cikakken 'yancin yin walwal karkashin koyarwar addinin Musulunci. Na gamsu kuma na yadda, al'ummar Musulmi a Amurka mutane ne masu zaman lafiya da fatan Adalci ga kowa.

Wannan shi ne dalilin kawo muku wannan ziyara domin na karfafa muku guiwa, ku sami yakini akan abinda kuka yi Imani da shi, babu mai cin zarafinku sabida addini mu zuba masa ido. Dan haka, idan muka cigaba da kasancewa al'umma daya, zamu sami karfi kuma rauni ba zai riskemu ba. Dole ne kuma mu mutunta bukatun juna. Na gobe, shukran.

Yasir Ramadan Gwale
04-02-2016

Daga Kalaman John Danfulani


DAGA KALAMAN JOHN DANFULANI

"A cikin al'ummar Najeriya su waye suke da yara sama Miliyan 12 da suke yawo kwararo-kwararo suna bara dan neman abinda zasu Ci? " Tambaya mai nuna kalubale!

Wannan maganar ta tsaya min a Rai. Kuma duk da zagi da cin mutunci da John Danfulani yayi mana, ya manta cewa shima dan Arewa . Idan ya ce mana Almajirai to a wajen mutanan kudu har da shi a cikin Almajiran.

A gefe daya kuma maganganun da ya fadi gaskiya, akan yawan barace barace da muke. Ya kamata mu tambayi kanmu Me yasa bama ganin mutanan Kudancin Kaduna suna yin bara? Shin ko ba su da Nakasassau da talakawa ne? Me yasa sai mu ne kawai muke bara da rokon da ?

Ya kamata, indai mun ji haushin maganganun John Danfulani muma mu kalubalance su ta hanyar mayar da martani da Alkinta rayuwar dukkan Almajirai mu maida su gaban iyaye su. Idan ba haka ba kuwa, to abinda Danfulani ya fada a kanmu haka yake, gaskiya ne; kuma bai kamata mu tada jijiyar wuya ba.

Zance na gaskiya Almajirai sunyi yawa a ko ina, mai makon abin ya ragu kullum sai ka ruwa yake. Almajirai na kwarara cikin birane kamar sun yi kwace, yaushe muke tunanin samun adalci daga na sama a lokacin da muka kasa yiwa na kasa da mu.

Har kullum abin da yake bani mamaki, idan har mutanan da muke kira "Arnan Arewa" zasu killace al'ummar su duk da talaucin su, su hana su Bara, su samar musu da abinci da sana'a, me yasa mu da muke musu tunkaho da Arziki da wadata kullum yaranmu suke yin Bara, wanda har cikin gidajen irinsu John Danfulani yaranmu ke shiga yin ?

Gaskiya dai lokaci yayi da hukumomi da kungiyoyin al'umma da Limamai da masu unguwanni da Sarakuna zasu tashi tsaye haikan a Arewa domin Yaki da yin barace barace. Almajiri ma d'a ne ya kamata yayi karatu a gaban iyayansa kamar 'ya 'yan kowa.

Lallai d'abi'ar Barace barace na daga abinda ke zubar mana da k'ima da mutunci. Ai wannan ya isa abin takaici ace Arnan Arewa ne zai kalubalance mu da cewa mu Almajirai ne. Wallahi ina jin takaicin hakan.

Ya kamata Jami'o'in da muke da su a Arewa su tashi tsaye su yi aiki tukuru wajen yin Nazari da binciken yadda za'a kawo karshen Bara a Arewacin Najeriya da kuma a tsakanin Al'ummar Arewa musamman Hausawa da Fulani da Barebari. Allah ya bamu ikon gyarawa.

Yasir Ramadan Gwale
04-02-2016

Tuesday, February 2, 2016

Hattara Dai Shugaban Kasa Muhammadu Buhari


HATTARA DAI SHUGABAN KASA MUHAMMADU BUHARI

Sama da mutane 86 rahotanni suka tabbatar da cewa sun rasa rayukan su a garin Dolari dake kusa da birnin Maiduguri kwana biyu da suka gabata. Wannan rasa rayuka ya faruwa ne bayan gida je sama da 300 da aka kone kurmus a garin da kuma daruruwan dabbobi da suka halaka. Wannan abu yakai a jallin da Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai tsaida duk abinda yake gabànsa dan zuwa da kansa ya ganewa idan sa irin mummunar asarar da akai, tare da jajantawa al'ummar garin wannan masifa da ake fama da ita, daidai lokacin da ake cewar anci galabar 'yan ta'adda.

A wannan halin da mutanan garin Dolari suke ciki na juyayin da alhinin rashin da sukai, a lokacin da Shugaban kasa ke karakaina tsakanin kasashen Afurka. Kwastam sai muka ji ance Shugaban kasa ya sake daukan jakarsa zuwa kasashen Turai. Na tabbata duk muhimmancin wannan taro da Shugaban kasa zai halarta a Faransa bai kai muhimmancin Taron G20 da akai a kasar Turkiyya ba a watan nuwanba Shekarar bara, ana tsaka da fara wannan muhimmin taro wanda kasar Faransa jigo ce a cikin kasashen G20, a 13 ga watan nuwamban ranar fara wannan taro aka kai wani Hari a Faransa, wannan tasa shugaba Hollande ya bayar da sanarwar soke halartar taron G20, duk kuwa da irin muhimmancin da taron yake da shi a wajensa.

A Takaice dai Rayuwar al'ummar da Shugaban Faransa Hollande yake Shugabanta tafi duk wani taro a duniyar nan muhimmanci a wajensa. Alal hakika wannan shi ne irin Misalin shugabanci na adalci da kaunar al'umma da kishin kasa. Wannan shi ne nauyi da kuma amanar da ya kamata duk wani shugaba ya kula da ita, martabar rayukan al'umma yafi duk wani taro da za ai muhimmanci. Shugaban kasar Faransa da bai san Allah ba, bai san tsananin AzabarSa akan wadan da suka ci amanar shugabanci, bai kuma san tanadin da Allah ya yiwa shugabanni Adalci ba, yayi haka! Ina ga Shugaban da yasan Allah yasan girman AzabarSa da kuma tanadin ga shugaba Ajali?!

Amma dai mu anan gida Nigeria abin ba haka yake ba. Shugabannin mu basu cika baiwa rayuwar al'ummar su muhimmanci ba. Halartar taruka da harkokin gabansu yafi muhimmanci a wajensu. Abin mamaki hatta nan makotanmu Jamhuriyar Nijar, shugabannin kasar sun fi mutunta al'ummar su akan namu shugabannin. Misali a turmutsutsun da ya faru a hajjin da ya gabata Alhazan Nijar 34 ne kacal suka rasu a wannan ibtila'i. Duk da haka, sai da Shugaban kasar yaje har Filin Jirgin saman kasar a lokacin da Alhazan kasar zasu fara dawowa, yayi musu ta'aziyar rasuwar 'yan Nijar da suka rasu a wannan turmutsutsu. Sannan kuma a al'adar Gwamnatoci na nuna juyayin ta hanyar sassauto da tuta dan girmama rayuwar wani ko wasu da aka rasa, Shugaban kasar ya bada hutun kwana uku a duk fadin Nijar dan Jajantawa iyalan wadan da suka rasu. Sannan aka sassauto da tutar kasar kasa dan girmama wadan da suka rasu a hukumance.

A ta bangaren Nigeria kuwa, Shugaban da ake gani shi ne mafi soyuwa a zukatan al'ummatai sam bai yi haka ba. Duba da cewar sama da mutun 100 ne 'yan Nigeria suka rasa rayukansu a wannan turmutsutsu babu wani abu mai kama da nuna jajantawa a hukumance. Haka kuma, duk da irin asarar rayuka da akai a Borno da Yobe da Adamawa tun daga hawansa Mulki har ya zuwa yau Shugaban kasa bai taka da kafarsa yaje musamman domin ganewa idansa da kuma Jajantawa wadan da suka rasa yan uwansu da dukiyoyinsu ba.

Yana da kyau Shugaban kasa ya sani, alhaki duk al'ummar kasarnan na wuyan sa, wajibin sa ne, ya kare mana abubuwa guda hudu. Rayuka, Dukiya, Hankali da kuma Addini. Lallai ya zama wajibi Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi hattara kuma ya maida hankali wajen yin abinda ya kamata dan kula tare da Jajantawa mutanan dan suke cikin bala'i irin wannan. Shugaban kasa Muhammadu Buhari zai kasance abin tambaya ranar gobe kiyama akan irin wannan mummunar kisan gilla da akewa al'umma babu gaira babu dalili.

Akwai takaici kwarai akan yadda shugabanninmu basu cika damuwa da abubuwa na wajibin su ba, su gwammace shiga duniya ana ta ruwa ana hirarraki. Ya Allah ka bamu ikon cin wannan jarabawa da kai mana, ka jarrabemu da shugabanninmu, ka jarrabi shugabanninmu da mu. Allah ka bamu mai kyau a duniya ka bamu mai kyau a Lahira.

Yasir Ramadan Gwale
02-02-2016