Tuesday, July 26, 2016

Zamani Riga


ZAMANI RIGA 

A lokacin Gwamnatin Malam Ibrahim Shekarau, Gwamnati ta kuduri aniyar gina katafaren Hotel a Lamba One Ibrahim Taiwo Road, inda yanzu aka mayar makarantar Sakandare. Gwamnati tayi la'akari da yanayin Jihar Kano a matsayin ta na cibiyar Kasuwanci a Arewacin Najeriya dama Yammacin Afurka da kasashen dake kudu da Sahara, amma duk da wannan bunkasa da buwayar da Kano tayi a harkar kasuwancin saye da sayarwa, Kano din babu masauki wadatattu domin saukar baki. Wannan na daya daga dalilin da Gwamnatin Kano ta bayar a wani tsari da suka yi da aka kira Kano Economic Road Map.

Anyi wannan kuduri ne da kyakkyawar niyya dan habakar kasuwancin Kano. Kasancewar gari kamar Kano babu wani katafaren Hotel dan saukar baki irin na Alfarma. Dan haka ne aka sanya wannan damba ta samar da Five Star Hotel Lamba one Ibrahim Taiwo Road. Amma sai wannan abin ya samu mummunar fahimta daga kungiyoyin al'umma da wasu daga cikin shugabannin al'umma a jihar Kano. Inda aka dinga sukar lamirin gina wannan hotel, ana cewa Gwamnati zata gina wajen badala a kusa da cikin birnin Kano.

A haka wasu mutane suka je fadar mai martaba Sarkin Kano Marigayi Alh.  Ado Bayero suka gaya masa karya da gaskiya akan wannan yunkuri na Gwamnati. Daga ciki dalilin a da suka baiwa Sarki Allah ya jikansa, har da cewar wai za'a gina Hotel mai tsawo da baki zasu dinga zuwa suna gane sirrin Kano. Da wasu zantuka marasa tushenmu masu kama da abin dariya. A haka suka gamsar da Sarki Marigayi, dan haka ya ja Hankalin Gwamnati karkashin Malam Ibrahim Shekarau da ta jingina wannan shiri na samar da wannan hotel.

Meye Hotel? Hotel fa ba wani abu bane illa masauki. Kuma akan haka ake gina dukkan wani Hotel, masauki ne domin amfanin baki da zasu shigo su yi wani uzuri, ko kuma samar da wajen yin taruka da sauransu. Amma sai muka yiwa Hotel guguwar Fahimta. Wasu da dama da an ambaci Hotel kawai sai suce wajen fasikanci ne da aikata badala. Hotel masauki ne da mutum zai biya kudi ya kwana. Wanda duk ya kama ya aikata fasadi ko barna ba zai zama adalci a hukunta Hotel da aikin da wani yayi a cikinsa ba.

Yanzu a jiha Kamar Kano, idan ka cire Hotel din Tahir Guest Palace babu wani Hotel da yake biye da shi a daraja. Sauran duk basu wuce alallaba ba. Wannan mutum fa me Tahir ba dan kasarnan bane, amma mu kalli irin mahaukatan kudin da yake samu a Harkar Hotel. Shin yaushe ne zamu yi kishin kanmu wajen bunkasa tattalin arzikin kasarmu da jihar mu? Duk wanda yake matafiyi yasan muhimmancin Hotel, amma duk da haka muna yiwa Hotel Kallon wajen aikata fasadi da barna.

A irin haka muke yiwa komai fassara. Yana da kyau al'ummarmu mu fadada tunani, mu wanke zuciyar mu ta hanyar duba duk wani abu na zamani da yake da Maslaha a rayuwar yau da gobe. Amma kuskure ne mu dinga kafewa akan abinda ba muda cikakkiyar fahimta akansa. Allah ya sakawa Malaminmu Sheikh Dr. Sani Umar Rijiyar Lemo da alheri, domin a lokacin da ya bayar da fatawa akan daukar hoto ba laifi bane, na san wasu da dama da suka kafa akan Hoto Haramun ne suka sauka daga kan wannan ra'ayin.

Lallai wannan gari namu mai albarka da muke fatan Allah ya tsare mana shi ya yaukaka arzikin sa,  yana bukatar Malamai masu zurfin Ilimi irinsu Dr. Sani da Dr. Bashir da zasu dinga haskawa al'umma abubuwa musamman wadan da zamani yazo da su kuma ake da gajeran tunani akansu, domin shi zamani riga ne, idan yazo dauka ake a saka ba mayar da kai baya ba. Allah ka haskaka zukatanmu wajen karbar gaskiya da kuma aiki da ita.

Yasir Ramadan Gwale 
26-07-2016

Sunday, July 24, 2016

Meye Ake Nufi Da Film Village?


MEYE AKE NUFIN DA FILM  VILLAGE? 

Wannan tambaya ce da dan uwa Malam Misbahu Saminu Madabo yayi a Shafin sa na Facebook. Sakamakon tattaunawar da naga ana yi a karkashin posting din nasa yasa na bashi amsa kamar haka:
Alkali Misbahu Saminu MadaboMadabo sannu da kokari. Daga wannan tambaya da kuma maganganun da masu koment ke yi ya nuna da dama kawai sunan suka sani amma sam basu fahimci meye ake nufi da film Village ba.

Amma a zance na hakika Film Village da Gwamnati zata gina, wani waje ne da zaka kirashi ma'aikata da za a tanadar masa abubuwan bukata irin na abinda aka yi domin sa.  Misali, idan Gwamnati ta gina Film Village zai zama tamkar garin aiki ne. Wato duk wanda zai shirya film zai je wannan waje ya biya Gwamnati kudin amfani da wajen sannan a bashi iznin shiga, wajen zai kunshi lambu da dakunan daukar hoto da wajen tace sauti ko Studio, da kuma nau'I na Kyamarori da suturu da abubuwan da masu film zasu bukata, za tanadar da komai, amma fa duk abinda mutum zai yi amfani zai zama sai an biya kafin fara amfani da shi.

Bayan haka kuma, Gwamnati fa ba wai kawai wajen zata gina ta dankawa masu shirya film sai yadda suka ga dama ba, ba haka bane, wajen zai kasance akwai jami'an tsaro da zasu dinga sanya ido akan masu shiga da fita, dan tabbatar ba sace ko lalata kayan da aka sanya dan amfanin wajen ba. Jami'an tsaro anan ba ina nufin zata zuba sojoji ko 'yan sanda ba, za a samarwa wajen Security ne da ya dace da kuma wanda aka ga yayi daidai.

Sannan kuma, a cikin wajen dai za a bayar da damar bude kantuna na sai da abinci da kayan ciye ciye. Wanda wannan gwamnati na da zabi ko dai kantuna su zama nata ma'ana abinda ake sayarwa ko kuma a baiwa mutane shaguna su kuma su zuba kaya a ciki.

Gwamnatoci na samar da irin wannan waje ne, dan kebe masu yin a abin da kuma samar masa da tsarin da zai bawa hukuma damar samun cikakken kudin shiga. Amma fa mutane su sani, duk wannan abinda za ai tilas Gwamnati zatai ne bisa la'akari da yanayi da kuma al'adunmu da suka dace da addini. 

Misali idan Gwamnati ta gina, zata ce dokokin jihar Kano sun haramta sha da sayar da giya. Dan haka zai zama doka a wannan waje ba za a sayar da giya ko shanta ba, dan haka wanda duk aka kama ya karya dokar shan giya ko sayar da ita a wajen zai fuskanci hukuncin da aka tanadar wa hakan. Wannan ya hada da sauran abubuwan da Musulunci ya hana, kuma dokokin Jihar Kano suka tabbatar da haninsu kamar Zina, Luwadi, Sata, Sane, kwace fada da sauransu.

Bugu da kari, akwai wajen shakatawa na Gwamnati dake Yankari a Bauchi, a wannan waje akwai dakunan kwana da wajen ganin na mun daji da kuma wajen linkaya. Kaga ai Gwamnati ce ta samar amma dokokin wajen sun dace da mutanan Bauchi da Arewacin Najeriya. Sannan kuma akwai irin wannan wajen shakatawa a Cross Rivers da ake kira Obudu, a wannan waje sha da sayar da giya ba laifi bane, sabida a jihar shan giya da sayar da ita ba laifi bane. Amma kuma abinda zamu gane shi ne dukkan su da wannan film Village Gwamnati tayi ne dan samun kudin shiga, ba wai dan kawai bukatun wasu tsiraru bane.

Bayan haka kuma, Gwamnati ba wai kawai zata zura ido ayi duk abinda aka ga dama ba, tilas akwai dokokin da za ai domin wajen. Dan ita Gwamnati zai zamar mata wajen samun kudin shiga. Tunda kasashe irinsu India da Turkiyya da Masar suna da irin wannan waje, kuma yana daga cikin abubuwan samar musu da kudin shiga.

A dan haka, mutane su sani, wannan waje zai zama ne kamar gidan tarihi na Arewa dake Kaduna. Gwamnati ce ta gina, amma ana zuwa a kama hanyar dakuna a kwana, sannan kuma akwai dakunan taro wanda za a biya a gudanar da wani sha'ani.

A Takaice wannan shi ne Film Village kuma shi ne abinda Gwamnati zata gina a Kano. Duk wanda yace ba haka bane, to bai fahimci meye Film Village ba. 

Dan gane da batun lalacewar tarbiyya kuwa. Duk wanda misali ya karbi wannan waje dan gudanar da wani sha'ani kuma ya karya doka to akwai tsari na hukunci. Sai dai kuma wanda zai yi ba a sani ba, amma wannan ba zai sanya a hukunta wajen da aikin wasu tsiraru ba tunda ba manufarsa batawa ba.

Kamar Musulmi ne yaje ya aikata ta'addanci yasa Bom ya kashe mutane. Wannan ba zai zama dalilin da zai sanya a hukunta Musulunci da cewar shi ya horar da shi wannan aikin ba. Duk kuwa da cewar wanda yasa Bom din ya kashe Mutane Musulmi ne. Dan haka, ba zaka hukunta Film da aikin da kaga wani yayi da bai dace ba. Allah shi ne mafi sani.

Yasir Ramadan Gwale 
24-07-2016

Thursday, July 21, 2016

Meye Illa Ko Amfanin Samar Da Film Village?


MEYE ILLA DA KUMA AMFANIN SAMAR DA FILM VILLAGE A KANO?

Naga mutane da yawa na magana kan batun kaddamar da Film Village da akai a Kano kwanaki. To gaskiya ni kam ban fahimci wace irin Illa mutane suke magana da wannan abu zai yi ba. Misali ada can da babu wannan film Village din an fasa shirya tare da gudanar da Fina-finai a Kano? Ina Jama'ah suke lokacin da masu sana'ar shirya film suka fitar da Clip na Video suna kiran magoya bayan su da su zabi APC da 'yan takarar ta a 2015! Bana kare sana'ar Fina-finai, amma meye laifin Gwamnati dan ta samar musu da muhalli na shirya film? Kamar yadda nace ni a karan kaina ban fahimci Illar da mutane suke magana ba, amma ina fatan wanda suka sani su fahimtar da ni.

A ganina a yadda mutane suke ta korafin lalacewar al'amura a harkar Fina-finai, shin samar musu da wannan matsuguni ba zai bada damar samar da sauye sauye wadan da zasu bada sararin kawo gyara a harkar ba? Wannan fahimtata ce, gani nake hakan zai baiwa Hukumomi damar fahimtar hakikanin inda matsala take da kuma kawo gyara a harkar, tunda a zamanin yanzu babu wani dan siyasa da baya fatan samun goyon masu shirya film. Wanda suna amfani da wakoki da suke tsuma zukatan magoya bayan dukkan jam'iyyun siyasa.

Harkar filming din nan fa sabida muna kallo ne shi yasa har muke shaida kurakurai da abubuwan da basu dace ba a ciki. To ina ganin ba Condemnation ya kamata ayi ba, kamata yayi a duba hanyoyi na kawo gyara a harkar. Kamar yadda tsohon Gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau ya kawo sauye sauyen da suka tsabtace harkar film a zamanin mulkinsa. Kowa ya shaida yadda Shugaban hukumar tace film ta Kano Malam Rabo Abdulkarim ya sha Gwagwarmaya wajen kawo sauyi da gyararraki a harkar shirya film a Kano. To misali, idan akace suna killace a muhalli guda daya kuma akwai tsayayyen shugaba a harkar ai tilas a kawo gyara. Amma wannan tunani na ba mamaki ina kan kuskure, a fahimtar da ni.

Yasir Ramadan Gwale 
21-07-2015 

Gaskiya Da Rikon Amana Da Aiki Tukuru Suka Janyowa Malam Nuhu Ribadu Martaba Da Daukaka


GASKIYA DA RIKON AMANA DA AIKI TUKURU SUKA JANYOWA MALAM NUHU RIBADU MARTABA DA DAUKAKA 

Malam Nuhu Ribadu mutum mai gaskiya kamar Littafi. Ka duba yadda gaskiya da rikon Amana da aiki tukuru suka janyowa Malam Nuhu Ribadu martaba da daukaka. A kakar zaben 2015 Malam Nuhu Ribadu ya shiga tsaka mai wuya, wadda ta janyo dukkan jam'iyyun APC da PDP suka yi ta kokarin ganin shi ne zai zamar musu dan takarar Gwamnan Jihar Adamawa. Cikin ikon Allah mai aukuwa ta auku, Allah ya kaddari Malam Nuhu da samun tikitin tsayawa takara karkashin jam'iyyar PDP. 

Yanzu kuma bayan dan wani lokaci jam'iyyar APC ta fahimci irin wawar asarar da ta yi ta Malam Nuhu Ribadu, dan haka suka yi ta aika masa da wasiku na fatan alheri da fatan ganin ya koma APC. Mu muna da masaniyar dukkan abubuwan da suka wakana wanda suka janyo ficewar irinsu Malam Nuhu Ribadu da Sardaunan Kano Malam Ibrahim Shekarau fi cewa daga APC jam'iyyar da suka kafa ta da hannunsu,  suka koma PDP. 

Malam Nuhu Ribadu na da damar zab'in abin da yaga yafi masa daidai kuma zai fi zama Maslaha a gareshi da al'ummarsa da kuma mu da muke tare da shi. Ni a nawa ra'ayin bana fatan Malam Nuhu Ribadu ya fita daga PDP ya tsallaka APC. Ina fatan ya cigaba da zama a PDP domin ko ina muna bukatar wakilcin mutane na gari. Amma idan ya yanke shawarar komawa APC wannan yayi hukunci ba wanda raina zai so ba, amma  ina masa fatan alheri. 

Na gamsu dari bisa dari akan nagartarsa da kishin sa da son sa da gaskiya. Allah ka taimake shi kayi riko da hannunsa, ka tabbatar da shi akan gaskiya komai rintsi.  

Yasir Ramadan Gwale 
21-07-2015

Monday, July 18, 2016


MEYE AIBU NA SALON DAUKA HOTON DAB? 

A satin da ya shige naga kusan hankalin mutanen Social Media gaba daya ya karkata kan wannan salon daukar hoto. Naga da yawa daga cikin bayanan da akai tayi na sukar abin da cewa 'WAI' bautar Iblis ne. Amma a zahirin gaskiya babu wani wanda na gamsu da hujjojinsa akan cewa hakan bautar shedan ne. Yana da kyau mutane su sani a rayuwa fa komai Halal ne, sai abinda Shari'ah tayi togaciya akansa, kamar sata, sane, bizi, zara da sauran kaba'ira. Allahumma sai kuma abinda ya shafi koyi da Wanda ba Musulmi ba a abinda ya shafi Ibada. 

A wannan zamanin na yayi, kusan komai ana kwaikwayo ne daga ko dai masu shirya Fina-finai ko 'yan kwallon kafa ko mawakan disko da sauransu wadan da ake kira da Celebrities. Tun daga yanayin dinkin da sanya sutura da yin aski da gyaran fuska da sauran kwalliyar gayu ta kece raini duk ana kwaikwayo ne a wajen su. To meye yasa sai akan salon daukar hoton DAB mutane suke ta magana basu yi kan sauran ba? Watakila sabida ance bautar shedan ne. To abin tambaya shi ne, meye bautar Iblis ko shedan? Shin yanzu ne a 2016 Iblis ya nuna yadda za a dinga yi masa Bauta? Da can walawa mabiyansa yayi?

Yana da kyau mutane su dinga lura da yanayin rayuwa da kuma sassauyawar zamanin da yadda ake samun canji daga lokaci zuwa lokaci. Kowane zamani kan zo da nasa salon, a da can a tara gashi him da sanya fankacecen wando da katuwar Radiyo shi ne cinyewa. A wannan lokacin idan ka baiwa gaye tsukakken wando ta kasa ba zai saka ba, amma kuma yanzu shi ne gayu sabida ana yayinsa. To haka zamani kan zo da salo iri iri.

A ganina dan masu Sha'awa sunyi irin wannan daukar hoto ba wani abin kausasa harshe bane. Yayi ne kuma zai wuce kamar yadda komai kan zo ya wuce. Yanzu irin yadda 'yan mata kan yi kwalliya a Shekara 20 da suka wuce idan mace tayi ba zata iya fita ba, sabida zata zama abin tsokana da zolaya. Amma yanzu gayu ne sai mace ta zambada hoda tai ta yawonta tana tunkahon tayi gayu na kece raini.

Sai dai kuma, yana da kyau mu sani muna da kyawawan dabiu da halaye da suka wadace mu wajen yin kwalliya. Amma wannan ba zai zamu aibu ba dan mutane sun dinga tafiya da zamani matukar ba a kaucewa Shari'ah ba. 

Yana da kyau mutane su zama masu saukakawa kansu ba masu tsanantawa ba. Abinda ba sabon Allah ba amma mutane suyi zafi akansa.

Yasir Ramadan Gwale 
18-07-2016

Saturday, July 2, 2016

OZONE LAYER : WANI Bargo Da Allah Ya Sanya Tsakanin Rana da Wannan Duniya Yayi Wagegiyar Hujewa


OZONE LAYER: WANI BARGO DA ALLAH YA SANYA TSAKANIN RANA DA WANNAN DUNIYA YA YI WAGEGIYAR HUJEWA

Jaridar The Guardina ta kasar Burtaniya ta wallafa Wani binciken masana 'yan kasashen Amurka da Burtaniya kwararru akan sanin kimiyyar sararin samaniya. Shi dai wannan bincike da aka buga a babbar mujallar kimiyya dake taskance binciken kwararru ta bayyana cewar wannan bargon da ake kira ozone layer da Allah ya sanya shi a matsayin kariya tsakanin wannan duniya tamu da kuma rana ya fara hujewa tun kusan shekarun 1980 inda bular ta dinga fadada tun daga wancan lokaci har zuwa yanzu, inda a wannan lokaci aka gano wagegiyar  hujewa a jikin ozone layer din.  Shi dai wannan bargo da ake kira ozone layer, Allah ya sanya shi ne a sararin samaniyar wannan duniya domin ya zama kariya ga halittun kasa daga sinadaran da suke zubowa daga zafin rana wanda zasu cutar da Bil-Adama ta hanyar sanyawa mutane cututtukan da ke da alaka da fata da kuma sankara. 

Allah Buwayi gagara Misali, ya sanya wannan abu tamkar bargo a sararin saman wannan duniya domin ya zama kariya gareta da kuma Bani-Adam. Wannan wagegiyar hujewa da ozone layer tayi, babbar barazana ce ga Bil-Adama. Ita dai wannan ozone layer masana sun fadi cewar samun sauyin da duniya take yi na d'umamar yanayi ne kan sabbaba hujewar ta. D'umamar duniya da ake kira da global warming ya taimaka matuka wajen cigaba da hujewar ozone layer. Dan haka ne a kusan ko da yaushe Majalisar Dinkin Duniya kan shirya manya manyan tarukan karawa juna sani domin a fadakar akan irin hadarin da wannan duniya take ciki a kuma tattauna yadda za a kaucewa d'umamar duniya da kuma sauye sauyen da ake samu na yanayi. Ta hanyar rage yawan hayakin masana'antu da manyan kasashen masu karfin tattalin arziki ke samarwa. 

Bayan haka kuma, majalisar dinkin duniya tayi ta bijiro da shirye shirye na daddasa bishiyu wadan da suke taimakawa wajen samar da yanayin da zai taimaka wajen rage wannan barazana da duniya ke fuskanta ta hanyar d'umamar yanayi. Sare dazuka da Bankawa tsirrai wuta na daga cikin abubuwan da suke sabbaba d'umamar yanayi da kuma cigaba da karuwar hujewar ozone layer, wanda hakan kan haifar da kafewar manya da kananan koguna ta hanyar gurgusowar hamada da kuma narkewa tare da zaftarewar daskararriyar kankarar da ke makare kudancin wannan duniya, yayin da a hannu guda hakan ke kara yawan ruwan da ke cikin manyan kogunan wannan duniya, abinda ke haifar da ambaliyar ruwa da kan haifar da asarar muhalli me girman gaske.

Binciken na kwararru ya nuna cewar samun karuwar d'umamar duniya da ake yi shi ne yake haifar da karin bulewar ozone layer, hakan kuma karin barazana ce ga lafiyar Bil-Adama dake rayuwa a wannan duniya musamman sassan duniyar dake fama da yanayin zafin rana. Domin ana samun karin sabbin cututtukan da suke da alaka da fata da kuma sankara fata mai wuya sha'ani. Sabida a dalilin wannan hujewa sinadarin Nitrogen na sulalowa ya gauraya da yanayin wannan duniya, wanda barazana ce mai girman gaske.

Yasir Ramadan Gwale 
02-07-2016