Sunday, December 21, 2014

Siyasar 2015 An Kai Arewa An Baro


SIYASAR 2015 AN KAI AREWA AN BARO

Shi fa yaki irin na siyasa dan zamba ne, dole ayi shirin tunkararsa indai da gaske yakin za'a yi. Dole kayi nazarin kanka a karon farko, kasan waye kai me zaka iya, meye karfinka, meye rauninka, meye manufarka, me kake san cimmawa; sannan kuma, sai ka nazarci abokin fito na fito, meye karfinsa, meye yake nema da zai iya cin lagonka da shi, wanda daman kai tuni ka gama sanin wadan can hanyoyi ka gama nazartarsu, dan haka ko da abokin fito na fito ya taso maka kana da dukkan dabaru da kai tanadi na kare kanka daga duk wani yunkuri irin nasa. Dole kuwa kai haka, domin kaine ka taro yakin ba shi ne yazo ya sameka ba, dan haka ne aka Ruwaito Manzo SAW idan zai fita Yaki yakan nufi Gabas alhali kuma inda zai tunkara a yamma yake, wannan dabara ce ta yakin da ake neman cin nasara da gaske.

Manyan 'yan Siyasa daga Arewa tun lokacin da aka fara fuskantar 2015 sukai ta batun dole sai mulkin Najeriya ya koma Arewa. Alhali babu wani shiri da akayi dan hakan, wace Manufa Arewa take da ita gamammiya idan Mulkin ya dawo Arewa? duk da dai kawai yaudara ce kawai ake yi da sunan Arewa, kuma galibi Talakawa sune ke bata lokacinsu da sunan Arewa, dan nasan babu wani dan siyasa da zai ce yana yin siyasar Neman Mulki kuma yace da sunan Arewa yake yi. Shi yasa galibin masu kiran Arewa, kodai 'yan Siyasar da ba neman Mulki suke ba, kawai basa san a manta da su ne shi yasa suke kiran Arewa, ko kuma wasu mutane ne da ba zasu iya sanyawa ako hana komai ba. Daman kuma Talaka maganarsa bata cika tasiri ba a wajen masu mulki.

Shin masu fatan mulki ya dawo Arewa wane tanadi suka yiwa hakan? Idan Mulki ko Shugabancin Najeriya ya dawo Arewa me suke san cimmawa, ko kuwa kawai muna san Mulki a suna ace wane dan Arewa shi ne Shugaban kasa alhali kuma babu wani abu da zai iya kullawa! Na farko dai tun ran gini tun ran zane, wadan da suka ginamu akan kabilanci sunyi kuskure. Shi yasa aka wayi gari babu wani da yake batun Najeriya a siyasance, dan kudu fatansa dan kudu ko da kuwa babu wani abu da za'a tsinanawa mazabarsa, haka shima dan Arewa, ai bincike ya nuna cewa da dama daga cikin mutanan kudu maso kudu suna cikin mawuyacin halin rashin aikin yi da rashin karatu, duk kuwa da cewa sitiyarin da ke jan Najeriya dan garinsu ke tukashi.

A ganina da wahala Mulkin Najeriya ya iya dawowa Arewa a hannun jam'iyyar hamayya, idan maganata gaskiya ce, to Gwamnonin nan guda biyar ko bakwai da suka tada kayar baya a PDP kuma daga karshe suka fice suka koma APC sune suka kai Arewa suka baro! Wannan dai ra'ayi da tunani na ne, kuma gwargwadan abinda na gani na fahimta. Sai nake ganin kamar muna da saurin mantuwa, mun rudu da yawanmu alhali kuwa a Najeriya ba'a zaben gaskiya a matakin Shugaban kasa! Batun Arewa da Yarabawa kuwa aganina wani abu ne adukunkune mai rikitarwa, dan kuwa mai yasa ba'a dauko Kayode Fayemi da ya fadi zaben Gwamnan Ekiti an bashi mataimakin Buhari ba? Duba da cewa sananne ne kuma anga kamun ludayinsa, amma aka dauko tsohon kwamashina alhali ga Gwamna da yake da dukkan kwarewa ta Mulki! Wannan fa wata katuwar ayar tambaya ce, amma duk aka ja baki akai gum... Zan cigaba In sha Allah.

Yasir Ramadan Gwale
21-12-2014

Sunday, December 14, 2014

Kwangwaratuleshans Janar Muhammadu Buhari


KWANGWARATULESHANS JANAR BUHARI

Assalamu Alaikum Warahmatullah. Sunana YASIR RAMADAN GWALE, ina mai yin amfani da wannan dama wajen taya Janar Muhammadu Buhari murnar lashe zaben fidda gwani a karon farko da aka kasa a faifai Janar yayi takara kuma ya lashe zabe. Ba shakka na san Zainab na cike da murnar samun wannan Nasara, ina kara tayata murnar samun wannan Nasara da GMB yayi.

Ina fatan Janar Buhari a matsayinsa na jagora zai rungumi kowa da kowa dan tafiya tare. Nasarar Buhari nasara ce ga Dimokaradiyya, a koda yaushe dimokaradiyya na alfahari da irin wannan damar da ake baiwa al'ummah dan bayyana ra'ayinsu na tsayawa zabe. Haka nan kuma ina taya Gwamnan Kano Rabiu Musa Kwankwaso murnar zamowa na biyu a wannan zabe, ba shakka Kwankwaso yayi kokari ya nuna iya siyasarsa, da yawa na ganin Atiku Abubakar ne zai zo matsayi na biyu, amma kwankwaso ya shammaci mutane. Ina kuma taya Atiku Abubakar din alhinin samun wannan matsayi na uku, na tabbatar ba haka ya so ba amma hukuncin Allah shi ne abin karba, kuma ya burgeni matuka da ya nuna jarumtaka ya karbi faduwa! Wannan ita ce kaiwa makura a dimokaradiyya duk da ba laifi bane neman hakki idan har wani yana ganin anyi masa ba daidai ba.

A daya gefen kuma ina taya tsohon mawallafin jaridar Leadership Newspapers Pharm. Sam Nda-Isiah murnar samun kuri'u guda goma ba shakka, na aminta da irin kishin kasa da kaunar Najeriya da Sam yake da shi, ina masa fatan Allah ya bashi wata dama da zai hidimtawa al'ummar Najeriya.

Haka kuma, Janar Buhari zai kuma fuskantar Shugaban Kasa Dr. Goodluck Jonathan dan yi wannan karon battar a karo na biyu. Tun a zaben da ya gabata na 2011 da yawan 'yan Najeriya masu bibiyar harkokin siyasa sun san lagwan kowa tsakanin Buhari da Jonathan. Fatana shi ne Allah ya saukaka mana al'amuranmu ya zabar mana shugabanni na gari adalai a dukkan matakai na shugabanci. Kuma in sha Allah zan taimaka da Naira 10,000 ga kwamatin yakin neman zaben Janar Buhari na BSO.

Ina taya murna ga 'yan uwanmu abokanmu 'yan Buhariyya musamman wadan da suka tayamu murnar samun Nasarar Malam Nuhu Ribadu da Malam Salihu Salihu Sagir Takai dama wadan da basu tayamu murna ba, da kuma masu yi mana mummunan fata, har da masu yi mana tadiya da mugun baki irinsu Mansur Manu Soro duk muna musu murnakuma muna yi musu adduar fatan alheri. Allah ya taimaki kasarmu Najeriya ya bamu nasara, ya amintar da mu ya bamu lafiya da zaman lafiya.

Cc: Ibrahim Sanyi-Sanyi, Muhammad Aliyu Dutsin-Ma, Kwamared Baban Shareek Gumel, Affan Buba Abuya, Sagir Musbahu Daura Dole, Hussein Abdussalam, Attahiru Muhammad Marnona, Abubakar Aminu Ibrahim, Bashir Ahmad, Sunusi ShehuSunusi Musa, Auwalu Lawan Aranposu, Hamza Ibrahim Baba, Abdulrashid Ahmad, Baba Bala Katsina, Ibrahim D Itsenyabi, Khaleel Nasir Kiru, Lawal Muazu Bauchi, Yamai Muhammad, Hk Yaradua, Husain Husain Kyar'adua, Uba Danzainab.

Bcc:....

Yasir Ramadan Gwale
14-12-2014

KHRTAOUM: Ban Kwana Da Ismail Lamido


KHARTOUM: BAN KWANA DA ISMAIL LAMIDO

Da fatan an sauka gida lafiya Malam Ismail Lamido. Allah ya saka da alheri da wannan takakkiya kuma ya bar zumunci. Muna godiya mara adadi ga Jagoranmu Sardaunan Kano Malam Kano Shekarau CON. Allah kuma ya bamu Nasara a wannan zabe. Allah ya baiwa Malam Saluhu Sagit Takai Gwamnan kano kuma ya yi masa jagoranci zuwa ga adalci da daidaito. Allah ya taimaki jihar Kano da Najeriya.

Yasir Ramadan Gwale
13-12-2014

Thursday, December 11, 2014

Taya Murna Ga Malam Shamsu Abbaty

L-R Shamsu Abbaty da abokinsa

TAYA MURNA GA MALAM SHAMSU ABBATY

Congratulations Malam Shamsu Abbaty. Allah ya sanya alheri ya yiwa rayuwarka albarka. Ba shakka yau muna cike da farinciki da farincikinka ka, zamu kasance cikin sahum masu murna da fatan alheri a wannan rana. Allah ya yi maka jagora ya ya sanya maka albarka.

A madadin Ni Yasir Gwale da Auntynka Zainab Gwale muna tayaka murnar wannan saukar karatu da ake yi a yau a Kamfala Uganda.

Yasir Ramadan Gwale
10-12-2014

Tuesday, December 9, 2014

Alhamdulillah Takai Yaci Zabe


ALHAMDULILLAH TAKAI YACI ZABE

Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin Sarki da ya nuna mana wannan Nasara ta Malam Salihu Sagir Takai da ya zama dan takararmu na Gwamna a Kano. Muna kara mika godiya ga Daliget da suka zabi cancanta. Allah ya bamu nasara a babban zabe mu kada madu bacci. Allah mun gode maka.

JIGAWA: Muna taya murna ga Malam Aminu Ringim bisa nasarar da ya samu. Allah ya nuna mana babban zabe lafiya.

KADUNA: Muna taya Dallatun Zazzau Malam Ramalan Yero murnar samun nasara da yayi. Allah ya baka Nasara a babban zabe Dallatu.

Yasir Ramadan Gwale
09-12-2014

Alhamdulillah Malam Nuhu Ribadu Yaci Zabe


ALHAMDULILLAH MALAM NUHU RIBADU YACI ZABE

Alhamdulillah muna godiya ga Allah madaukakin sarki da ya nuna mana wannan Nasara. Haka kuma muna kara mika godiya ga Daliget na Adamawa hakika kun zabi wanda ya dace. Muna murna da wannan zabe da kuja yiwa Malam Nuhu Ribadu. Alhamdulillah Allah mun gode maka. Allah ka nuna mana babban zabe lafiya kuma muna kara rokonka Ya Allah ka baiwa Malam Nuhu Ribadu nasarar lashe babban zabe mai tafe. Masha Allah.

Muna kuma fatan kara samun Nasara ga Malam Salihu Sagir Takai a nan gaba kadan.

Yasir Ramadan Gwale
09-12-2014

Sunday, December 7, 2014

Jinjina Ga Jami'an Tsaron Najeriya


JINJINA GA JAMI'AN TSARON NAJERIYA

Ba shakka wannan Nasara da jami'an tsaron Najeriya suka samu na kame wannan jirgi cike da kayan yaki da ake kyautata zaton makiya zaman lafiyar Najeriya ne suke taimakawa 'yan ta'adda da miyagun makamai wajen jefa rayuwar al'umma cikin mawuyacin hali, wannan Nasara da jami'an tsaron suka samu na kame wannan jirgi abin a yaba ne tare da karfafa musu guiwa wajen jajircewa akan aikinsu. Muna yabawa da wannan aiki na kokarin tabbatar da zaman lafiya, da kuma kwa-kwulo wadannan miyagu azzalumai 'yan ta'adda wadan da suka dauki zubar da jinin al'umma a matsayin wani aiki na yau da gobe.

Addu'armu bata tsaya kadai akan Allah ya tona asirin irin wadannan miyagu ba, Muna kara yin adduah akan Allah ya yi mana maganin duk wani abu da yafi karfinmu, Allah ka yi mana maganin duk wasu miyagu azzalumai 'yan ta'adda da suka addabemu. Allah ka rusa shirinsu ka wargaza sha'aninsu. Allah ka darkakesu, ka dawo mana da dawwamammen zaman lafiya.

Allah ka taimaki jami'an tsaronmu da suke aiki babu dare babu rana wajen ganin an samu zaman lafiya a garuruwanmu. Haka nan kuma, muna kira ga Gwamnati da ta basu dukkan kulawa wajen ganin sunci lagon 'yan ta'adda. Allah ka taimaki kasarmu Najeriya ka bamu lafiya da zama lafiya.

YASIR RAMADAN GWALE
07-12-2014

Tuesday, December 2, 2014

HATTARA GWAMNATIN KANO: Jihar Kano Bata Karkashin Dokar Ta'baci


HATTARA GWAMNATIN KANO: Jihar Kano Bata Karkashin Dokar Ta'baci

Ranar juma'ar makon da ya gabata 28 ga watan Nuwamba, rana ce da al'umma da yawa a cikin Birnin Kano ba zasu taba mantawa da ita ba. Wannan ita ce ranar da aka kai hari mafi muni a tarihin hare-haren da 'yan ta'adda makiya Allah makiya san zaman lafiya suke kawowa Kano. An kashe dattawa da matasa da yara a lokacin da suke Ibada dan yin munajati tare da ubangijinsu. Ba shakka wannan al'amari muninsa yakai muni. Ina kara yin adduah ga wadan da suka rasa rayukansu a wannan rana, Allah ya jikansu ya gafarta musu ya sa al-jannah ce makomarsu. Masu raunuka kuma Allah ya basu lafiya, ya sa ciwon ya zama kaffara a garesu.

Lokacin da wannan al'amari ya auku, Mai girma Gwamnan jihar Kano wanda shi ne Shugaban Tsaro na jihar Kano (Chief Security) baya Kano yana can kuryar kudancin Najeriya, shima Mai Martaba Sarkin Kano Alh. Muhammadu Sunusi II shima baya kasar baki daya, haka zalika Kwamashinan 'yan Sanda  na jihar Kano shima baya Kano! Cikin kaddarawar Allah wannan mummunan kaba'ira ya faru.

Faruwar wannan mummanan harin ta'addanci da awa hudu misalin karfe 06:04 Uba Danzainab ya sanar mana a facebook bikin da ake a ofishin mataimakin Gwamna na cike form din takararsa ta zama Gwamna Kano! A irin wannan lokaci da al'umma ta shiga cikin damuwa da rudani, akai wawar asarar rayukan al'umma, masu mulkin da ya kamata ace sunfi kowa nuna  damuwa da rayukan al'ummarsu sama da komai, amma a kyale al'umma a shiga al'amuran siyasa? Yanzu wannan daidai ne?

Haka nan shima Gwamnan Kano Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, duk da cewar baya Kano lokacin da abin ya faru, sai washegari Asabar da safe sannan muka ji cewar Gwamna yaje Masallacin kofar Gidan Sarki da Asibitin Murtala dan jajantawa wadan da abin ya shafa tare da ganin irin girman barnar a Masallacin Gidan Sarki, amma bamu ji cewa ya halarci jana'izar wadan da aka binne a makabartar Dan Dolo a safiyar asabar din ba.

A wannan ranar ne kuma tsohon mataimakin Shugaban Kasa Alhaji Atiku Abubakar ya bada sanarwar soke bikin da wasu abokansa suka shirya masa na murnar samun karin shekara da yayi (BirthDay), ya bada sanarwar cewar ya soke bikin ne domin jimami tare da taya al'ummar Kano alhinin abinda ya faru. Ba shakka ko domin siyasa Atiku yayi hakan ya kyauta, domin ya nuna cewa jinin al'ummah yana da kima da daraja a wajensa.

Haka kuma, wani abin mamaki da ya kuma faruwa a lahadin da ta biyo bayan asabar din, sai muka samu sanarwa a facebook daga Baba Dantiye cewar Gwamna Kano yaje bikin auren wasu Yarabawa a jihar Legas! Yaushe za a ce Gwamna wanda shi ne yafi kamata yafi kowa nuna damuwa akan rayukan al'ummar jihar Kano, amma ace har ya fice ya tafi yawan bukukuwa? Shin hakan na nufin tsohon mataimakin shugaban kasa yafi Gwamnan Kano mutunta rayukan al'ummar Kano?

Shin yanzu idan mun zargi Gwamnatin tarayya akan rashin nuna damuwa da rayukan al'umma, su kuma Shugabanninmu na jihohi mu ce musu me? Tsakanin Gwamnatin tarayya da Gwamnatin Kano wa yafi kamata ya fi nuna damuwa da raukan al'ummar jihar Kano?

Lallai ya kamata mu sani cewar Jihar Kano fa bata karkashin dokar ta baci, dan haka Gwamnan Kano shi ne shugaban tsaro Chief Security na jihar Kano, shi ne wanda yake da ruwa da tsaki akan duk abinda ya shafi tsaro a cikin kano musamman cikin birni. A irin wannan halin da aka samu kai aciki, Gwamna baya gari, Sarki baya gari, Kwamashinan 'yan sanda baya gari, shi kuma Magaimakin Gwamna yana can yana bikin ciken form din tsayawa takara. To dan Allah waye ya damu da rayuwar al'ummar da ake shugabanta?

Ina mai amfani da wannan damar wajen yin kira ga Gwamnatin Kano da Mai Girma Gwamnan Kano Engr Dr. Rabiu Musa Kwankwaso da Mataimakin Gwamna Dr. Abdullahi Umar Ganduje, akan su fito su nemi afuwar al'ummar Kano akan wannan rashin ko in kula da aka yi a daidai lokacin da Kano ta fada cikin bala'i. Rashin yin hakan shi ne zai tabbatar mana da cewar masu mulkin ba gaskiya suke ba akan kula da rayuwar al'umma, sunfi damuwa da sha'anin mulkinsu da siyasarsu sama da rayuwar al'ummar da suke shugabanta.

Ina sake amfani da wannan damar wajen kara yiwa al'umma ta'aziyar wannan ibtila'i da ya samemu Allah ya jikan wadan da suka rasu a sanadiyar wannan hari. Marasa lafiyan cikinsu Allah ya basu lafiya ya sa hakan ya zama kaffara a garesu. Masu kai wadannan hare-hare Allah ka sansu kana ganin Allah kai musu abinda yafi dacewa da su. Allah ka amintar da mu a garuruwanmu.

Yasir Ramadan Gwale
02-12-2012

Monday, December 1, 2014

MAganar Gaskiya Dangane Da Kahse-Kashen 'Yan Boko Haram


MAGANAR GASKIYA

Rabin gaskiya ba gaskiya bane. Ba zaiyuwu ba ace akwai magana rabi gaskiya rabi karya. Kodai ta zama gaskiya zalla ko karya zalla. Dole mu tunawa kanmu tarihi dan fuskantar gaskiyar al'amari.

Wadan da suka kashe sahabin Manzon Allah kuma surikinsa, Usman Ibn Affan Alaihis-Salam, Musulmi ne masu fatan samun shiga al-jannah, sun kashe shi yana karanta al-Qurani zancen Allah. Haka zalika, wadan da suka kashe Malam Jaafar Adam Rahimahullah ranar juma'ah yana limancin Sallar Asuba, Sallar da munafukai basa halatta inji Manzon Allah. Nayi imani wadan da suka kashe Malam Jaafar musulmi ne ba arna ba.

Dan haka babu wani dalili da wani zai fito yace mana WAI MUSULMI BA ZASU IYA KASHE MUSULMI A MASALLACI BA wannan ba gaskiya bane. Ya faru a baya kuma yana cigaba da faruwa a yanzu. 

Wadan da suke wannan kisan da ake kira Boko Haram dole mu yarda cewa su Musulmi ne, amma kasancewarsu Musulmi ba shi ke nuna halaccin abinda suka aikatawa ba, kuma aikinsu ba shi ke nuna haka duk Musulmi suke ba. Akwai Musulmin kirki na gari masu tsoron Allah; kuma akwai Musulmin banza gurbatattu marasa tsoran Allah.

Ba yadda zaka kore Musulmi daga Musulunci duk munin aikinsa indai ba shi ya kore kansa daga Musulunci ba. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yayi alqunutu yana kama sunan wasu Allah ya haneshi, ya gaya masa Subhanahu Wata'ala cewa shiriya a hannunsa take buwayi gagara misali.

Bambancin addini ko bambancin siyasa ba shi zai halatta mana kiyayya da gaba ba. Na gamsu cewa Shugaban kasa baya yin abinda ya kamata ace yayi a harkokin tsaro. Amma kai tsaye a ce shi ne ke kashe mutane wannan ba gaskiya bane.

Dole mu gayawa kanmu gaskiya. Shin tsakani da Allah akwai wani Musulmi ko dan Boko Haram ko ba shi ba da zai yarda ya daura Bom a jikinsa Bom ya tashi da shi dan bukatar Goodluck Jonathan ta biya? Shin arna irin na Najeriya zasu saka Bom a jikinsu su mutu dan bukatar Jonathan ta biya? Akwai wani mai hankali daga cikin Musulmi ko kirista da za ayi yarjejeniya da shi dan shi din ya mutu?

Ya kamata mu fadi gaskiya kuma mu yi adalci a maganganunmu. Idan har zamu dinga baiwa Boko Haram uzuri muna cewa basu bane wasu ne daban. To wallahi wannan abin ba zai taba yin sauki ba sai dai ya karu. Mun shagaltar da kawukanmu da zargin juna su kuma zasu mamaye garuruwanmu. Wanda ya sani ya sani wanda bai sani ba ya sani.

Indai ana san kawo karshen wannan kashe kashe dole abi hanyoyi na gaskiya dan magance matsalar. Amma ba zai yuwu ba a dinga siyasa da rayuwar al'umma. Ko mun yarda ko bamu yarda ba Khawarijawa sun sanyamu yakin da bamu shirya ba. Sarakuna ya kamata suyi abinda ya dace cikin hikima.

Adduah kadai ba zata magance mana wannan halin da muke ciki ba. A cikinmu babu Annabi Musa ko Abu Huraira. Manzon Allah SAW ba adduah kadai yayi ya kwanta Mala'iku sukai masa Badar ba.
Kayi tir ko kai Allah wadai wannan ba zai taba sauya gaskiya ba. Tana nan a matsayinta na gaskiya, haka nan ba zai taba sanya karya ta zama gaskiya ba.

Lallai jagororinmu subi hanyoyin da suka kamata wajen kare salwantar rayukan al'ummah da suke mutuwa ba gaira ba dalili. Allah ka nuna mana gaskiya mu fahimci gaskiya ce ka bamu ikon binta ka nuna mana karya mu fahimci karya ce ka bamu ikon kauce mata.

Yasir Ramadan Gwale
30-11-2014

Saturday, November 29, 2014

Malam Idi Mai Nika


MALAM IDI MAI NIKA

Tun ina yaro akan tura ni kai nika injin Malam Idi, kaf unguwarmu ba wani me injin nika sai Malam Idi, tun kafin Ganganci ta fara sayar da abinci muna kiran layin da sunan lungun malam Idi, sai bayan da ganganci ta fara sayar da abinci ne, kuma mutane suka rage cin tuwan gari, aka daina bukatar nika sosai sannan sunan Malam Idi ya bata, aka fi sanin layin da sunan layin ganganci kamar yadda ake kiransa a yanzu.

Dazu nake samun labarin cewa Malam Idi Mai Nika na daya daga cikin mutanan da harin Bom ya rutsa da su jiya a Masallacin Gidan Sarki. Ina yi masa adduar fatan Alheri da fatan samun rahama da daukaka, yayi dace ya rasu a ranar Juma'a, ranar da Manzon Allah SAW yace idin Musulmi ce da take kewayowa duk mako. Kuma kashe shi akayi a yayin da ya amsa kiran Ladan na Hayya AlaS-Salah. Sallar Juma'a. Hani'Allahka Ya Malam Idi Mai Nika.

Amadadin kaina Yasir Gwale da Zainab Gwale muna yiwa Malam Idi adduar fatan samun Shahada. Allah ya sa mutuwa hutu ce a garesu. Iyalansa su Malam Musa da abokina Isa ina mika ta'aziyata a garesu. Allah ya basu hakurin jure wannan rashi. Allah ya kyauta namu zuwan.

YASIR RAMADAN GWALE
29-11-2014

Hattara Jama'a: Idan Hankali Ya Bata Hankali Ke Nemoshi


Allah madaukakin Sarki, yana gaya mana a cikin littafinsa mai tsarki AlQurani sura ta 29 aya ta 2: Cewar "Shin tsammaninku dan kunyi Imani ba zamu jarrabeku ba?" Lallai ku sani al'ummar da ta gabace ku an jarrabesu da fitina da tsoro, da firgici da tsanani da tashin hankali. Allah Subhanahu Wata'ala yana da hikima a dukkan abubuwan da ya saukarwa bayinSa na alkhairi ko sharri, shi yasa ma yace daya daga cikin rukunan Imani shi ne yadda da KADDARA mai kyau da marar kyau.

Ba shakka wasu al'amuran kan faru dan jarraba masu Imani na hakika wadan da suke maida gazawa a garesu tare da kyautatawa Allah zato. Da yawa daga cikin Annabawa, wadan da sune zababbun zababbunSa Subhanahu Wata'ala, an kashesu, kisa na wuulakanci, Allah da ya fi kowa sansu da kaunarsu, yana kallo, amma saboda ya tanadar musu da wata daukaka ta sanadiyar hanyar mutuwarsu, ya sanya mutuwarsu ta kasance a irin halin da ta zo musu.

Allah buwayi ne gagara misali, da babu wani mahaluki da ya isa tambayar dalilin da yasa abubuwansa suke faruwa bisa ikonSa. Allah masani ne ga abinda duk yake boye a garemu ne, babu wani abu da yake fakuwa gareshi Subhanahu Wata'ala.

Mun kyautata zato ga Allah madaukakin Sarki, cewa yana gani kuma yana ji, yasan masu shirya dukkan kaidi da makida akan bayinSa masu kadaita shi da Ibada. Watakila Allah ya yi nufin daukaka darajar wadan da aka kashe a irin wannan yanayi na tashin hankali a ranar gobe alkiyama.

Ya 'yan uwa masu girma. kada mu taba yanke tsammani daga samun rahama da taimakon mahaliccinmu. Shi Allah Assami'u ne kuma Albasiru ne. Babu wani abu da yake kaucewa ganinsa.

Manzon Allah SAW ya fada mana cewa karshen Duniya kisa zai yawaita, tashin hankali zai yawaita, har ta kai matsayin da wanda yake kisa bai san dalilin kisan ba, shima wanda ake kashewa bai san me ya aikata ba aka kashe shi. Munji munyi Da'a a gareka Ya Rasulullah.

Ba shakka a halin da ake ciki a yanzu. kashe kashe sun yawaita a gurare da dama. Wannan kuma duk yana faruwa ne bisa kaddarawar Ubangiji Subhanahu Wata'ala.

Dan haka, yana da kyau a lokacin da mutane ke cikin tsananin firgici da damuwa su kame harsunansu daga furta kalaman da zasu zamar musu nadama a ranar alkiyama da bazata amfanesu ba. Muyi hakuri mu maida lamuranmu ga Allah, muyi gaskiya, muji tsoron Allah gwargwadan Iko, kar muyi shirka kar mu zargi Allah akan abubuwan da suke faruwa a garemu. Mu sani cewar Allah mai ji ne kuma mai gani ne.

Allah da kansa yace kuyi Bushara ga masu hakuri da juriya a lokacin tsanani. Ba shakka abinda yake faruwa a garemu ya wuce duk yadda muke kaddarashi, mu kyautata zato ga Allah, muji tsoron Allah a maganganunmu da ayyukanmu.

Allah da kansa ya korewa kansa zalinci, yace kuma sai ya sakawa duk wanda aka zalunta ko da kuwa wanda aka zalunta baice Allah ya saka masa ba. Ya dan uwa ka sani ko daidai da magana idan ka zalinci wani Allah ba zai yafe ba matukar ba wanda aka zalinta din bane ya yafe. Muji tsoron Allah, mu kiyaye harsunanmu wajen furta kalaman da zasu zama nadama a garemu ranar da nadamar ba zata amfanawa bawa da komai ba.

A madadin Ni Yasir Gwale da Zainab Gwale muna taya al'ummar da wannan ibtila'i ya rutsa da su alhinin wannan al'amari. Wadan da suka rasu Allah ya jikansu ya gafarta musu. Allah ka sa mu cika da Imani.

YASIR RAMADAN GWALE
29-11-2014

Friday, November 28, 2014

SHAIDU: Yadda Harin Boko Haram Yai Ta'adi Ga Masu Ibada A Kano

SHAIDU: Yadda Harin Boko Haram Yai Ta'adi Ga Masu Ibada A Kano

Naman mutane ya warwatsu a harabar Masallacin Juma'a na kofar gidan Mai Martaba Sarkin Kano Muhammad Sunusi II. Wani mutum ne da yayi jigida da bamabamai ne yai yunkurin kutsa kai cikin Masallacin a lokacin da Liman yake jagorantar Sallar Juma'a a yau dinnan. 

Gawarwakin mutane sun warwatsu a farfajiyar masallacin, ko dai wadan da harin bom din ya kashe kai tsaye ko kuma wadan da suka mutu ta sanadiyar harbin binduga ko kuma wadan da suka rasu sakamakon turmutstutsu. 

Sai dai wata majiya daga fadar Kano tace Mai Martaba Sarkin Kano Muhammadu Sunusi yana kasar Faransa a lokacin da wannan bala'i ya auku, majiyar tayi karin bayanin cewar Sarkin ya tafi Faransa ne domin binciken lafiyarsa, haka kuma, manyan 'yan majalisar Sarki sun halarci wannan Sallah tare da Liman a cikin masallaci.

Bom na farko ya tarwatse ne a daidai lokacin da liman ya fara Sallah. Wani dan kunar bakin wake ne da ya makare wata karamar Toyota da bamabamai ne ya yo kan masallata a daidai lokacin da liman ya kabbara Sallah, inda ba tare da wata wata ba Bom din ya tarwatse. Bom na biyu kuma ya tarwatse ne a kusa da sahun da mutane sukai dan bin Sallah, haka kuma, Bom na uku ya fashe ne a cikin harabar Masallacin.

Sannan kuma, wani da abin ya faru akan idansa yace yaga wasu matasa suna harbin kan mai uwa da wabi a tsakanin masallata, abinda ya haifar da guje-guje da turmutstutsu. Mutumin ya kara da cewar naga mutum biyu dauke da bindigogi sun nufi cikin masallacin suna harbin kan mai tsautsayi, daya daga cikinsu ma naga yana dura harsasai a cikin kwansan bindigar, a cewar Umar Farouk wani matashi da abin ya faru a gabansa.

Wani ganau kuma ya kara da cewar bayaga gawarwaki da suke yashe a kasa, yaga yadda guntattakin naman mutane da jini yadda suka dinga makalewa a jikin kofofi da tagogin shiga Masallacin. Mutumin yace, duk da tsawo da ginin masallacin yake da shi, yaga naman mutane makalkale a saman masallacin ga jini face-face ko ina yana diga.

Ya Allah muna tawassuli da kyawawan ayyukanmu wadan da ka karba daga garemu Ya Allah ka dube ba dan halinmu ba ba dan mun kasa ba. Allah ka dubi raunana daga cikinmu, da kananan yara da marayu Ya Allah ka kawo mana karshen wannan masifa da bala'i. Allah ka jikan wadan da suka rigamu gidan gaskiya a wannan hari. Na ruwaito daga shafin Jaafar Jaafar.

YASIR RAMADAN GWALE
28-11-2014

Kwankwaso Ya Shammacemu

KWANKWASO YA SHAMMACE MU

Yanzu dai dukkan kwannafi ya kwanta dangane da wanda Gwamna Kwankwaso zai zaba wanda zai yi takarar Gwamna a APC. Wannan dai zabi ne na mai girma Gwamna ba zaben fidda Gwani bane, kamar yadda aka ce a zaben da ya gabata Malam Ibrahim Shekarau ya zabi Malam Salihu Sagir Takai ba tare da anyi zabe ba. Daman ance Tarihi hakanan yake maimaita Kansa.

Sai dai wannan zabe da akaiwa Ganduje ba shakka ya shammaceni, dan banyi tsammanin haka. Amma kuma nayi Imani da Allah cewa Malam Umar Abdullahi Ganduje mutumin kirki ne mai kamala da sanin yakamata.

Duk a cikin masu neman takara a APC alal hakika nafi samun nutsuwa da Ganduje dan na san ba zai cuci al'ummah ba. Ina taya shi murnar wannan zabi da akai masa.

Ina kuma adduah tare da rokon Allah ya sa ya zamar mana karkatacciyar kuka mai dadin hawa a zabe, Malam Salihu Sagir Takai ya kada shi cikin sauki. Ina da kwarin guiwar cewa Dan Takararmu Malam Salihu Sagir Takai zai baiwa Ganduje ruwa a wannan zabe mai zuwa da tazara mai yawa.

Na kuma tabbatar cewa Malam Salihu Sagit Takai yafi Ganduje cancantar zama Gwamnan Kano a zaben 2015. Ina kuma da yakinin cewar zamu shammaci Kwankwaso a wannan zabe. KANO TAKAI MUKE FATA. ALLAH YA AMINCE MAKA MALAM SALIHU TAKAI.

Yasir Ramadan Gwale
28-11-2014

Sunday, November 23, 2014

Malam Nuhu Ribadu 54


MALAM NUHU RIBADU 54

Allah ya sanya Albarka a cikin wadannan shekaru masu cike da alfanu. A madadina Yasir Gwale da Zainab Gwale muna yiwa Malam Nuhu Ribadu da iyalansa adduar Allah ya sanya masa albarka a sauran rayuwarsa ya amfanar da al'umma da dumbin baiwa da falaloli da ya baiwa Malam Nuhu Ribadu. Allah ya kara maka wasu shekaru masu yawa cike da koshin lafiya, Allah ya cika maka burinka na alkhairi. Najeriya na nan na jiranka a 2019. Allah ya amince maka.

Yasir Ramadan Gwale
22-11-2014

Zancen Zuci


Har kullum tambayar da take raina ita ce, Shin yanzu idan aka samu 'yan ta'adda da suka labe cikin al'umma a London da Warshington da Tel Aviv shin wadannan kasashen zasu bada Umarnin a yi amfani da jirgi mara matuki yayi ruwan bamabamai daga sama a rurrusa makarantu da asibitoci da kantuna da gidajen jama'a sauransu duk da sunan yakar 'yan ta'adda? Mu kalli yadda Netanyahu ya ragargaza Ghazza da sunan yakar 'Yan Hamas; Ga kuma yadda ake rushe gidajen jama'a a Iraqi da Suriya duk da sunan yakar ISIS. An hada karya da gaskiya ta hanyar amfani Khawarij sun sani ko basu sani ba ana cutar da Musulunci da Musulmai.

Wadannan fituntunu ba zasu taba karewa ba sai dai ma sabbi su sake bullowa. Domin Manzon Allah yayi ishara da faruwar kashe kashe a karshen duniya da bayyana tsiraici da aikata alfasha a bainar jama'a da fashi da sata da kwace. Babu wani abu da baya faruwa a yanzu duk wani nau'i na aikin sabo ana yinsa a cikin al'ummar Musulmi. Mace ta kashe mijinta, Miji ya kashe matarsa; d'a ya kashe iyayansa, uba yayi zina da matar dansa, uwa tayi zina da mijin 'yarta. Dan Adam yayi zina da dabba, ayi zina tsakanin mace da mace, namiji da namiji. Duk wannan ba sai anje da nisa ba laifuka ne da sukai katutu a tsakanin al'ummarmu.

Wasu sukan dauka cewa Wai Musulmi ba zai iya kashe Musulmi ba. Duk wanda suke da wannan tunani yana da kyau su je su karancin tarihin Khawarij. Wanda ya kashe Sayyaduna Usman RA Musulmi ne, haka wadan da suka kashe Aliyu dan Abi Talib da Dalha da Zubair duk masu ikirarin Musulunci sukai wannan aika aika.


'Yan shiah masu kiran kansu Musulmi suka fille kan jikan Manzon Allah SAW. Ya dan uwa ka kyautata tsakaninka da Allah, kaji tsoran Allah a cikin lamuranka, ka bautawa Allah gwargwadan ikonka, kar kaci hakkin wani, kar kayi shirka In Sha Allah zaka samu mahaliccinka mai tsanani Rahama ne da Jin Kai. Allah ka yafe mana laifukanmu wadan da muka sani da wadan da bamu sani ba.

Yasir Ramadan Gwale
19-11-2014

Thursday, November 13, 2014

Sheikh Ahmad Abubakar Gumi

Sheikh Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi: Akramakalahu yanzu na fara Nazarin Nasihar ka.

Ba shakka Dan danon magani ba shida dadi ko kadan a wajen mara lafiya da ake kokarin ceto rayuwarsa, amma tabbas shi ne abinda yafi bukata. Sau da dama mara lafiya har danne shi ake yi a dura masa magani, amma yana shure-shure yana kukan kura yana nuna baya so, amma haka nan ake dura masa maganin yana baya so, baya so. Karshe kuma maganin da ya dinga fatali da shi a baya sai ya zama silar samun warakarsa. Ai ko likata ma yasan Allah ka bada lafiya ba garin magani ba. Amma kuma haka sunnar Allah take, idan anyi rashin l;afiya aka sha magani sai kaga an samu sauki garas. Dan haka magani komai dacinsa a danne mara lafiya a bashi ya sha ko yana so ko baya so, a gaba shi zai fi kowa murna da maganin da aka bashi.

SAI DAI KUMA: Shi fa magani yana da lokuta kayyadaddu kuma kididdigaggu, idan akai sa'a aka sha akan lokaci, cikin dace sai a samu waraka. Kai akwai yana yin da idan ma aka baiwa mara lafiya magani tamkar kara masa ciwo ake yi. Dan haka kiyaye ka'idar shan magani ita kanta na taimakawa mara lafiya. Haka nan shima mai bada magani.

HAKA KUMA, wasu suna ganin ita gaskiya dandanonta yayi kama da na magani mai daci. To dan haka idan har mun gamsu cewa ita gaskiya daci gareta, to meye na tada jijiyar wuya? Allah ya baiwa mara-laiya lafiya, ya karawa mai lafiya lafiya.

Yasir Ramadan Gwale
13-11-2014

Wednesday, November 12, 2014

Tashin Hankalin Da Ya Faru A Potiskum

TASHIN HANKALI: Ba shakka abinda ya faru a Potiskum a wannan makon na tayar da Bom a cikin dalibai abin tashin hankali ne matuka da gaske. Duk wadan da sukai wannan aika aikar sun cika cikakkun Azzalumai makiya Allah makiya san zaman lafiya. 

Wadannan yara ne da basu yi wani laifin da suka cancanci mutuwa ta irin wannan hanya ba. An zalinci yara an kawo karshen rayuwarsu a daidai lokacin da yaran da iyayansu ke fatan samun kyakykyawar rayuwa a gaba, ashe basu sani ba ajali na nan gaba garesu ba tare da cikar burinsu na samun karatu mai zurfi ba.

Ya Allah ka sani wadannan yara an zalincesu ba tare da hakkinsu ba. Allah kai mai ji ne kuma mai gani ne. Ya Allah ka sakawa wadannan yara akan ta'addancin da akai musu. Wadannan masu aikata ta'addanci Ya Allah ba zasu taba bacewa ganinka ba Ya Allah ka nuna kudurarka ikonka akansu. Ya Allah kaine kafi sanin abinda ya cancanci wadan da sukai aiki itin nasu, Allah ka sakawa wanda aka zalinta. Iyayan wadannan yara Allah ka basu hakuri da dangana.

Allah ka baiwa hukumomin tsaro da duk wanda abin ya shafa ikon cin lagon 'yan ta'adda. Allah ba dan halinmu ba, ba dan abinfa gabbanmu suke aikatawa ba, Ya Allah albarkacin raunana daga cikinmu Allah ka Amintar da mu a garuruwanmu.

Ina mai amfani da wannan dama a madadin Ni Yasir Gwale da Zainab Gwale muke mika sakon ta'aziya ga iyayan wadannan yara, da gwamnatin jihar Yobe. Allah ka yaye mana abinda ya damemu.

Yasir Ramadan Gwale
12-11-2014

Saturday, November 1, 2014

Takai 2015


KANO 2015: Malam Salihu Sagir Takai salihin mutum managarci. Allah ya sani kyakkyawar shaida da aka bayar akansa da halayansa na gari da suka bayyana zahiri a garemu ya sa muke tare da shi, kuma zamu cigaba da kasancewa da shi.

Muna fatan alheri ga wannan adalin mutum salihi managarci amanar Sardaunan Kano Munistan Ilimi Malam Dr. Ibrahim Shekarau CON. ALLAH ka amince Takai 2015. Kowa ya samu dama yace Kano Sai Takai 2015.

Yasir Ramadan Gwale
30-10-2014

Wednesday, October 29, 2014

APC: Kwankwaso Yaci Zabe A Bashi Abinsa

Gwamna Rabiu Kwankwaso

APC: KWANKWASO YACI ZABE A BASHI ABINSA

Jiya talata 28 ga oktoban nan muka shaida yadda Miliyoyin 'yan jam'iyyar APC daga ko ina a fadin Najeriya suka hallara a Habuja babban birnin tarayya dan nuna goyan bayansu ga takarar Gwamna Kwankwasiya Amanaa matsayin shugaban kasa wanda zai yiwa jam'iyyar takara. Wadan da suka samu halartar taron sun shaida mana cewar Habuja tayi cikar kwari babu masaka tsinke, duk inda ka duba Jan Kai kawai ake kwalli da shi, mata da maza.

Ance duk wanda yake takara a APC jiya cikinsa ya duri ruwa. Saboda kaddamar da takarar mai girma gwamna a jiya ta yamutsa hazo, kuma ta nuna a fili inda mutane suka karkata. Dan kuwa masu abin (jama'a) sunce sun ji sun gani Kwankwasiyya Nigeria. A sabida haka muke yiwa Shugaban Kasa mai jiran gado murna da fatan alheri. Duk da yake ni ba dan wannan jam'iyyar bane, amma ya zama dole a matsayina na dan Kano nayi murna akan irin yadda Najeriya gaba daya kwata ta hadu tace sai mutumin Kano. Wannan karamci ne akai mana kuma mun gode.

Ina kuma isar da sakon taya murna ga Shugaban kasa mai jiran gado. Ina kuma fatan idan lokacin rantsuwa yayi a aiko min da goran gayyata dan mu hadu a Habuja mu shaida rantsar da Gwamna Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin Shugaban Najeriya na goma sha shida. Kwangwaratuleshan ga abokina Auwalu Lawan Aranposu akan wannan Nasara da suka samu. Ina kuma fatan źa'a dinga kulawa da hakkin makwabtaka da zumuncin da ke tsakaninmu idan an shiga Villa.

Ina kuma amfani da wannan dama wajen yin jaje ga 'yan Bahariyya suKwamared Baban Shareek Gumel da Ibrahim Sanyi-Sanyi da fatan zasu dauki dangana. Shima dan uwana Sunusi Musa ina masa jaje da Atiku Abubakar bai samu wannan nasara ba, shima dan uwa Bashir Ahmad ina tayaka alhini da Sam Nda bai samu wannan nasara ba. Ina kuma fatan zaku hadu dan dafawa mai girma Shugaban kasa mai jiran gado domin ciyar da Najeriya gaba.

29-10-2014

Tuesday, October 28, 2014

ATIKU ABUBAKAR: Kadangaren Bakin Tulu


ATIKU ABUBAKAR: KADANGAREN BAKIN TULU

Kasancewar Turakin Adamawa Atiku Abubakar daya daga cikin 'yan takarar Shugaban kasa a jam'iyyar hamayya ta APC ta sa ya zamo kadangaren bakin tulu a cikin jam'iyyar; ance kadangaren bakin tulu idan an jefeshi za'a fasa tulu, idan an kyale shi kuma dole ayi hakuri asha ruwan a haka.

Fitowar Atiku Abubakar takara tare da Gen. Buhari yana yiwa magoya bayan Janar din barazana. Domin duk wani yunkuri na samar da wanda zai yiwa jam'iyyar takara ta hanyar sasantawa ko kwansansus, Atiku ba zai yarda da shi, abinda yake nuna dole sai anyi zaben fitar da gwani wanda daliget ake sa ran zasu yi.

Zaben fitar da Gwani kusan shi ake kallo a matsayin wata dama da shi Atikun ya makalewa. Domin wannan zabe na fid da gwani shi ne zai bada damar amfani da kudi wajen sayan masu zabe. Abinda ake ganin tuni Atiku ya tanadi jakar kudi dan wannan zabe. Ba shakka masharhanta na ganin cewar kudi zasu taka muhimmiyar rawa a wannan zabe. Kuma zasu taimakawa Atiku wajen iya samun nasarar zama dantakara.

Haka kuma, alamu na nuna cewar duk wani yunkuri dan kaiwa zuwa ga wannan zabe tamkar shatale takarar Buahri ne da ke zaman wanda yafi sauran 'yan takarar jam'iyar yawan magoya baya. Daga gefe guda kuma tsohon Shugaban kasa Olushegun Obasanjo na gargadin Apc da kada su sake su sanya Atiku a matsayin dantakararsu, abinda ke kara bayyana jikakkiyar da ke tsakani Atikun da tsohon mai gidansa Obasanjo.

Koma dai ya abin zai kasance. Lokaci ne zai tabbatar da waye zai fuskanci Shugaban Kasa Dr. Goodluck Jonathan a zaben 2015 da ke tafe.

Yasir Ramadan Gwale
27-10-2015

Monday, October 20, 2014

Cire Hula A Coci


CIRE HULA A COCI: Kwanakin baya da naga manyan 'yan Siyasarmu su Gen. Buhari da Atiku Abubakar da Gwamna Kwankwaso a coci sun ciccire huluna a gaban pasto abin ya bani mamaki matuka, kuma ya sanya min tambayoyi a raina dangane da wannan al'amari. 

Yanzu saboda Allah ace arne kamar mai Malafa ya sanya mutane masu kima da daraja shiga coci suna cire hula dan kawai neman Mulki ba dan yin kira zuwa ga addini ba! Shin yanzu idan su basu iya yadda zasu jawo shi Masallaci ba har sa bari shi ya yi silar shigarsu coci su cire hula duniya na gani?

Watakila wani yace ai ba kafurci bane dan sun shiga coci. Nima bance hakan ba, amma dai saninmu ne cewar sun shiga ne ba dan yin kira zuwa ga addinin Allah ba. Sun je ne dan siyasa, watakila da shi Gwamna Okorocha ba a APC yake ba da ba wanda zaka gani a cikinsu.

A kwanakin baya da Gen. Buhari da Gwamna Kwankwaso da Atiku Abubakar duk sun aurar da 'ya 'yansu amma babu wani arne da aka gayyato yazo cikin Masallaci akai daurin auren da shi, kuma Okorocha na nan duk sauran arnan duk suna nan, amma sai mu 'yan ina da biki zamu dinga binsu coci muna tafawa muna dariya, ai idan ni banyi silar zuwanka Masallaci ba a dalilin kawancen siyasa to ba yadda zakai silar zuwana coci na cire hula tunda ba wa'azi na je ba.
Na kuma ga yadda akai ta kokarin bayar da kariya da bada uzuri ga wadan da suka shiga kanisar, amma tambayar da taita yawo a raina ita ce:

Yanzu tsakani da Allah idan Malam Ibrahim Shekarau ne ya shiga coci ya cire hula a gaban pasto shin za'a bashi uzuri kamar yadda aka baiwa su Buhari da Kwankwaso da Atiku?

Idan har Uzuri ne mutum ya shiga coci ya cire hula a gaban pasto dan siyasa, to ba shakka uzuri ne babba mutum ya shiga PDP dan yin siyasa. Allah ka nuna mana karya ka bamu ikon kauce mata ka nuna mana gaskiya ka bamu ikon binta.

Yasir Ramadan Gwale
19-10-2014

Saturday, October 18, 2014

Kudin Form Din Takarar Janar Muhammadu Buhari


KUDIN FORM DIN TAKARAR BUHARI

Naji cewar Buhari ya sayi takardun cikewa shiga zabe akan kudi wajen Miliyan 27.5! Hakika wannan kudin yayi yawa sosai. Hakan kuma na kara nunawa al'umma cewa al'amarin Mulki ko Shugabanci a Najeriya ba na Talaka ba ne. Duk kokarin da ake yi shi ne na tsame hannun talakawa daga sha'anin Mulki.

Yanzu idan a Apc nake kuma zanyi takarar Shugaban kasa sai na biya wadannan Miliyoyi bayan kudin da zan batar na harkar yakin neman zabe? Apc ce fa ake ganin jam'iyyar Talakawa da ta zo dan sharewa talaka hawaye! Wannan karara lasisi ne ake baiwa zababbu su yi sata san ransu. 

Na zata kudin Form a Apc ba zai wuce 'yan dubunnai ba dan kusanto da abin ga talakawa, amma dai zatona ba gaskiya ba ne. Kuma ni abinda ya fara zuwa raina shin yanzu idan Buhari bai samu nasara ba shi kenan yayi asarar wadan can miliyoyi? Dan naji ance bashin Banki ya ciyo dan sayan takardun.

Wannan ta sanya na tuna kwanaki da naji wasu na ikirarin zasu sayawa Buhari takardun shiga zaben, shin kudin ne yayi musu tsada ko kuwa! Allah masani. Shin idan Buhari bai ci zabe ba magoya bayansa zasu taimaka masa biyan wannan bashin?

Bana yiwa Buhari mummunan fata. Adduah ta ita ce duk wanda zai fi zama alheri a garemu a wannan zabe Allah ka bashi.

Yasir Ramadan Gwale
17-10-2014

Saturday, October 11, 2014

APC-Buhari/Atiku/Kwankwaso Da Zaben 2015: Hanya Daya Tak Da Ta Ragewa 'Yan Adawa Daga Arewa

APC/BUHARI-ATIKU-KWANKWASO DA ZABEN 2015: HANYA DAYA TAK DA TA RAGEWA ‘YAN ADAWA DAGA AREWA

* wannan rubutu yana da tsawo, ina fatan duk wanda zai yi ta'aliki ya kasance ya karanta har karshe.

Dukkan dangin yabo da godiya da kirari sun tabbata ga Allah madaukakin sarki, tsira da amincinsa su kara tabbata ga shugaban Manzanni cikamakin Annabawa Muhammadu Dan Abdullahi; Allah yayi dadin tsira a gareshi da Alayansa da Sahabbansa da wadan da suka biyo bayansu da kyautatawa har ya zuwa ranar sakamako. Ina rokon Allah ya sa wannan abun da zan fada ya amfanemu baki daya, Allah kayi min jagoranci wajen fadin gaskiya.

Da farko yana da kyau mu mutanan Arewa Musulmi mu sani cewar dama ce muke da ita mukai sakaci ta kubuce mana, a dan haka ‘bari mukayi, masu magana kuma sun ce “ba’a yin ‘bari a kwashe duka”, ina fatan mai karatu zai kiyaye wannan magana da kyau! Idan muka duba Najeriya tun farkon kafuwarta har kawo yanzu, mu mutanan Arewa mun dad’e ana cin moriyar hakurinmu da kuma sakaci da sadaukarwarmu ba dan komai ba sai dan san zaman lafiya da zaman tare.

A baya anyi mana wawar Asarar Sa Abubakar Tafawa Balewa da su Sa Ahmadu Bello da sauransu wadanda ba dan komai aka kashe su ba sai dan Najeriya watakila kuma dan kasancearsu Musulmi daga Arewa. Mu ne mutanan Arewa saboda Alkawari da san zaman tare muka sadaukar da Shugabancin tarayya dake hannunmu muka dauka sukutum muka mikashi ga Obasanjo! Anyi hakan da kyakkyawar niyya ko akasin haka Allah shi ne mafi sani.

Tun bayan waccan dama da ta subuce mana, inda Obasanjo da aka bashi amana ya dinga gasa mana aya a hannu, har ta kai mun kai wani mataki da muke ta magagin yadda waccan dama da muka dauka da hannumu muka bayar muke fatan dawowarta hannunmu. Tun a shekarar 2003 da 2007 da kuma 2011 ake ta wannan fafutuka ta ganin cewar ikon tarayya ya koma hannunmu, domin da yawan mutanan Arewa munyi Imani cewar babu wani dan kudu da zai yi mana Adalci face idan har namu ya samu, shi yasa muka makance muke nema ido rufe.

A dan haka, kamar yadda na fada a baya cewar “ba’a yin bari a kwashe duka” inji ‘yan magana, to lallai ya kamata mu fahimci wannan magana da kyan gaske, mu kuma yi nazarin halin da muke ciki, mu kuma samarwa kanmu makoma ta gaskiya.

A dalilin neman waccan makoma, muka makance muka kasa tunanin meye abinda yafi kamata a garemu tunda mun kasance masu hamayya. Wannan ta sanya muke kiran “lallai mulki ya dawo Arewa” wanda wannan magana kuskure ce, da abinda yafi kamata shi ne mu ce lallai muna bukatar Musulmi ya zama Shugaban kasa na gaba, tunda yanzu wanda yake kai ba Musulmi ba ne.

Haka kuma, ba zai yuwu ba mu mika kukanmu ga Allah mahaliccinmu muna masu neman agaji da taimakonsa, sannan kuma mu sanya masa sharadi ba! Sharadin shi ne na cewar lallai sai dan Arewa (Buhari) ya zama Shugaban kasa! Tur kashi… ina fatan mai karatu yana biye da ni sosai kuma zai fahimci me nake nufi. Zanyi bayanin hakikanin abinda nake nufi nan gaba.

GEN. MUHAMMADU BUHARI: kamar yadda na fada a rubutun da na yi da yayi ishara zuwa ga wannan rubutun kuma nai alkawarin bayar da dalilai na. Anan yana da kyau mu mutanan Arewa Musulmi mu sani cewar ba wai Buhari ake ki ba, shi yasa aka ki bashi zabe a baya ba, a’a mu din ‘Yan Arewa Musulmi mu ne ake ki, mu ne ba’a so a zaman tarayya. Dan haka duk wanda yake zaton cewar a cire Buhari a kawo Gwamna Rabiu Kwankwaso ko Atiku Abubakar a matsayin dan takara shi ne ko ita ce mafita to bai fahimci al’amarin ba. Daman kuma masu magan sun ce "da dan gari akanci gari"

Ko an tsayar da Atiku ko Kwankwaso a wannan zaben da yake tafe, to abinda ya faru a baya shi ne dai zai sake faruwa, babu wani zani da zata canza, kamar yadda na fada mu dinne dai ba’a so. A dan haka ne duk wanda ya tsaya takara daga cikinmu yake shan mamaki.

ATIKU ABUBAKAR: Masu magana suka ce dama kwaya daya ce tal take zuwarwa wasu a rayuwa, idan sun yi azama sukanci amfaninta lokaci mai tsawo. Atiku Abubakar yana daga cikin wadan da suka samu dama mai kyau bayan zaben 1999, inda ya samu goyon bayan mafiya yawan gwamnonin Arewa na lokacin dan ayi wancakali da Obasanjo ya maye gurbinsa, amma Atiku ya barar da wannan damar.

Atiku ne fa saboda dadin Mulki ya dinga cinnawa gidansa (Arewa) wuta ya manta cewar idan sun gama Mulki zai baro Abuja ya dawo Arewa. Haka kuma, a baya ai Atiku Abubakar yayi takara a 2007 kuma anyi abinda akai, me ya iya yi? Don haka ko an sake tsayar da shi abinda akai masa a 2007 shi za a kuma yi masa, babu kuma abinda zai faru sai hanayi da hargowwa da ba zata iya canza komai ba.

GWAMNA RABIU KWANKWASO: Kwankwaso na daga cikin manyan na hannun damar Obasanjo a lokacin da Obj din yake sharafinsa. Ance har yanzu Gwamna Kwankwaso suna d'asawa da Obasanjo.

Gwamna Kwankwaso na daga cikin sabbin zubin da ake masa fatan tsayawa takarar Shugaban Kasa, da fatan zai yi abinda magabatansa suka kasa. Tauraruwar Kwankwaso ta fara haskawa ne tun lokacin da ta bayyana cewar akwai baraka tsakaninsa da Shugaban kasa, wanda wannan ta janyo masa farin jini da karbuwa a wajen mutane da yawa. Kamar Buhari da Atiku shima Kwankwaso babu wani abu da zai sauya idan ya zama dan takarar hamayya. Dan haka maganin kar ayi kar a fara.

Kamar yadda na fadi cewar Buhari zai fi zamarwa PDP karkatacciyar kuka mai dadin hawa idan ya zama dan takara, domin an san shi an kuma san logar kayar da shi zabe. Kuma PDP zasu fi kowa murnar kasancewarsa dan takara a wannan zaben, dan suna da lissafinsu a hannu. Haka kuma, yana da kyau mu sani cewar matsalar cin zabenmu mu ‘yan Arewa Musulmi a zaben tarayya a kudancin Najeriya take.

 Yana da kyau mu sani cewar PDP tana da girkakkiyar kuri’a a kudu, kuma tana da hanyoyin cin zabe sama da dubu na halal da na haram a kudancin Najeriya, a cikin jihohi goma sha bakwai (17) babu wata jiha da PDP ba zata samu sama da kashi 50 ba fiye da yadda hukumar zabe take bukatar kowane dan takara ya samu. Haka kuma, akwai jihohin da PDP tana cin zabe 100 bisa 100 ko mutum daya baya mutuwa kafin zabe. A Arewa kuwa babu wani dan takara dan Arewa da zai iya cin zabe a wata jiha 100 bisa 100!

Jam’iyyar PDP tana da tabbacin samun waccan kuri’ar ta kudancin Najeriya, zata sameta ta hanyar halal da haram. Wanda dan-takarar Arewa idan ya iya samun kashi ashirinda biyar a zabe na tsakani da Allah to shi ne ya iya samun jiha daya tak a kudu, itama sai anyi kamar ana yi.

A zaben daya gabata akwai jihar da Buhari kwata-kwata bai je yakin neman zabe ba. Sannan kuma, a bangaren PDP suna da masaniyar cewar Buhari na da karfi a Arewa, dan haka basu tayar da hankalin sai sun ci jihohin Arewa kamar yadda suka yiwa na kudu cin-dare daya, cin dari-bisa-dari ba, dan haka zasu dage ne wajen samun kashi 25, a lokacin da Buhari ko dan takarar Arewa yake murnar samun dubban kuri’u a Arewa, itama PDP ta baza komarta inda ta yakuto kashi 25 din da na Arewa ya kasa samu a kudu.

Zabe kuma ba zai taba cuwuwa a kudu ko Arewa kadai ba. Dole dan takara yana bukatar samun Nasara a jihohi 23 kafin ya samu Nasara, a yayin da mu a Arewa jiha 19 muke da ita muna bukatar jiha hudu kenan daga kudu. A hakanma da sauran rina a kaba! Domin a Arewa kana da jihar Plateau da Benue wanda ko ana ha-maza ana ha-mata dan takarar Arewa ba zai iya cin Plateau ba, har gwara Benue dan kiyayyarsu bata kai ta Berom ba.

A dan haka, duk wani yunkuri na tsayar da Buhari ko Atiku ko Kwankwaso takara a zabe mai zuwa tabbas karfafawa PDP guiwar cin nasarar wannan zabe ne. Watakila aji wannan magana bambarakwai, ba mamaki wani yayi fart da garaje yace karya ne… Amma dai abin da na sani shi ne lokaci ne kadai zai iya karyata wannan magana tawa ko da kuwa duk an taru an karyatani, dan haka indai da gaske muke kuma mun nufi Allah a wannan al’amari to dole Buhari da Kwankwaso da Atiku su hakura da duk wani batu ko yunkuri na yin takara a 2015 indai da gaske dan al’umma suke! Watakila mai karatu yace sam ba zata sabu ba, domin waye zai yi takarar kenan, ina nan dauke da amsar tambayarka mai karatu, kai dai biyoni kaji inda zan sauka.

KALMAR “IDAN” TAKWARA CE GA “DA”: Sau da dama in maganar wannan zaben ta taso, mu mutanan Arewa mukance “IDAN” har Yarabawa suka zabi dan takararmu to munci zabe! Wannan kalma ta “idan” tana nuna cewar bamu da wani tabbas kenan akan Yarabawa dangane da wannan zabe, duk kuwa da cewa tsakanin mu da su ‘yan Uba muke. Shi yasa idan abinda ya saba faruwa ya faru sai muyi amfani da kalmar “DA” ma’ana da anyi kaza da kaza ya faru.

Ina fatan mai karatu yana biye da ni, domin yanzu ne zamu yi bayanin mafitar wannan halin da muke ciki na tsahin Bamabami da kaskanci da karyewar tattalin arziki da koma baya ta fuskar ilimi da noma da kiwo da harkar lafiya da wutar lantarki da sauransu. Ga mafita nan tafe.

MECECE MAFITA A GAREMU? Wannan tambaya muhimmiya ce, da kowa zai so jin amsarta, ba shakka amsar wannan tambaya tana da sauki, kuma ita ce zata nuna makomarmu a wannan zabe da yake tafe. Watakila Allaah ne ya karbi adduarmu abinda ya faru na hadaka ya faru tsakanin ‘yan siyasa a Arewa da yankin Yarabawa suka hada kai dan samun mafita guda daya. Bari na sake tuna mana abinda na fada dazu a baya, amaganar da na ce “ba’a yin bari a kwashe duka” to lallai mu sani mu mutanan Arewa munyi bari dan haka ba dole ba ne mu kwashe duka, sai dai wanda zai kwasu wanda ba zamu iya kwashewa ba kuma mu barwa Allah.

Abinda nake nufi anan shi ne duk ‘yan Arewa dake san yin takarar Shugaban kasa a APC su hakura a dauko dan kudu Beyerabe Musulmi wanda ba Bola Tinuba ba, kuma ba Gwamna Fashola ba. Yana da kyau mu sani cewar a halin da muke ciki a yanzu mu ‘yan Arewa muna bukatar wanda zai yi mana Adalci ne a zaman tarayya, wanda ba zai zalince mu ba, wanda zai bamu hakkokinmu a matsayinmu na ‘yan Arewa Musulmi, kuma mutum wanda mu ‘yan Arewa ba zamu ji shakka akansa ba.

A dan haka mutumin da nake ganin zaifi karbuwa a wajenu fiye da duk wani Beyerabe shi ne Gwamnan jihar OSUN Abddul-Rauf Aregbesola! Eh tabbas shi nake nufi, gwamna Aregbesola a ganina shi ne mutumin da ‘yan Arewa ba zasu ji shakkar mara masa baya ba, kuma mutane da yawa zamu nutsu cewar zai yi mana Adalci idan ya zama Shugaban kasa.

Dalili akan haka shi ne, kamar yadda na fada a  baya, matsalar cin zaben dan Arewa a kudu take, na tabbata kuma nayi Imani idan ka kawo gwamna Aregbesola daga yankin Yarabawa kana da tabbacin samun kuri’ar yankin Kudu-maso-yamma gaba dayanta. Dan haka idan muka yi hakuri da damarmu muka barwa ‘dan kudu Bayerabe Musulmi to ba shakka Shugaban Kasa Goodluck Jonathan babu inda zashi, domin bayan ka rikita masa lissafi, to ka kassara shi duniya da lahira. Mu kuma tuan cewar a baya mun sadaukar da su Tafawa Balewa da Ahamadu Bello munyi hakuri da rashinsu, balle kuma hakuri da tsayawa zabe!

Idan akayi haka, mutane daga kudu irinsu Femi Fani-Kayode hankalinsu zai yi matukar tashi domin zasu yi ta yin ihun Muslim-Muslmin Tiket, wanda ihunsu da maganganunsu babu abinda zai karawa wannan tafiya sai karfi da kara samun yakini, domin Yarabawa zasu jajirce wajen ganin sun zabi Rauf tunda Yarbawa Musulmi su ne suke da rinjaye a yankin kudu maso yamma, tunda dan uwansu aka kawo. Daman tun asali ai su Awolowo ne suke nuna cewar Yarabawa ba ruwansu da addini dan kawai su danne yarabawa, amma wannan Magana ko kusa ba gaskiya bace, domin duk wanda yasan yarabawa ya san mutane ne masu san addini da san Musulunci. Mu kuma dole mu dawo daga rakiyar tuninmu na cewar Beyerabe ba musulmin kwarai ba ne, yana fifita Yare akan addini, wannan zato ne wanda shima kirkirarsa akai dan nesanta Musulmin Arewa da Musulmin Yarbawa.

A dan haka, anan Arewa mu kuma zamu hadu gaba daya mu zurarawa Rauf Aregbesola kuri’ah kan kace kwabo an fara lissafin Rauf a matsan shugaban kasa na gaba. Ina fatan ya zuwa yanzu mai karatu ya samu nutsuwa akan wannan batu, dan haka sai a samu mutum daga yankin Arewa-maso-yamma a bashi mukamin mataimakin shugaban kasa ko dai Gwamna Kwankwaso ko kuma wani zakakuri wanda zai iya tsolewa mutanan kudu-maso-kudu da kudu-maso-gabas ido.

A ganina wannan ita ce kadai hanyar da mulkin Najeriya zai dawo hannun dan Arewa a shekarar 2024, kaga daga nan sai muyi ta yi har illa masha Allah, inyamurai da mutanan kudu-maso-kudu sai dai suga ana yi. Kuma wannan ita ce mafitarmu a wannan zaben, tunda mufa mutanan Arewa bari muka yi, kuma ba zai taba yuwuwa ba ace sai mun kwashe duka, waton hannun karba hannun mayarwa. Dole ko mun so ko munki mulki ba zai dawo hannun dan Arewa ba sai da ‘yan dabaru.

Haka kuma, akwai wani kuskure da mu mutanan Arewa muke tafkawa amma ko a jikinmu, domin a 2011 a yankin Arewa maso yamma kadai akwai mutane kusan miliyan tara (9m) da suka yanki katin jefa kur’ah amma basu yi zabe ba, shin ina suka shiga? Mutuwa sukai ko me? Wannan kuri’ar fa tafi ta yankin Inyamurai baki daya, dan haka dole sai munyi abinda ake kira da turanci Mobilization na kuri’un jama’a har daren da za’a kada kuri’ah a samu wasu jajirtattun matasa su dinga bin mutane gida-gida suna jaddada musu cewar lallai asubar fari ta yiwa mutane a layin zabe, abi kauye-kauye, gari-gar, unguwa-unguwa, ina tabbatar maka mai karatu 2015 sai Musulmi ya zama shugaban kasa indai anyi haka da gaske kuma da kyakkyawar niyya.

Dan haka kamar yadda na fada wannan ita ce kadai hanyar da nake ganin zamu iya samun zabe a 2015, kauce mata kuwa ko mun yarda ko bamu yarda ba karawa PDP kwarin guiwar cin zaben Shugaban kasa ne. Buhari, Atiku, Kwankwaso kuwa sai mu yi musu addua tare da nuna godiya amma su yi hakuri da takara dama ce kuma ta wuce su. Yarabawa kuwa tuni ka sayesu ka biya kudin, domin muddin muka basu wannan damar dole su tsaya kai da fata wajen ganin dan-takara daga yankinsu yaci zabe. Ina fatan Allah ya nuna mana zaben 2015 rai da lafiya, ni da ku zamu zo nan facebook muna baiwa juna wannan labarin ko akasinsa.

Wanda zai karyata yana da iko, wanda zai gasgata shima yana da iko, amma ni dai nasan lokaci shi ne alkali, shi zai gasgatani ko ya karyatani. Dan haka mai hankali yi tunani.

Yasir Ramadan Gwale
11-10-2014

Tuesday, October 7, 2014

Jihad


JIHADI: Zai zama abin da daure kai ace anje ana dasawa mutane kayan fashewa kuma wasu su dinga ikirarin wai Jihadi suke yi idan sun mutu Allah zai tashe su a sahun su Hamza Ibn Abdulmuddalib saboda suna zaton sun mutu shahidai! Ko kusa wannan gurbataccen tunani ne, da gurguwar fahimta da zafin kan addini cikin matsanancin jahilcin addini, wanda irinsu Osama Bin Laden suka shuka shi yayi tsiro a zukatan wasu daga cikin fusatattun matasan Musulmi da basu gama fahimtar meye Addinin Islama ba. Shin meye Jihadi a Musulunci?
Yasir Ramadan Gwale
07-10-2014

Friday, October 3, 2014

Godiya Ta Musamman



GODIYA TA MUSAMMAN: Kusan tun kwana uku kafin jiya Malamina a CAS Alasan Sule ya rubuta sakon fatan alheri akan Timeline dina yake tuna min ranar da aka haifeni. Tun daga lokacin kuma na fara samun sakon taya murna da fatan alheri.

Hakika nayi murna da farin ciki a jiya yadda mutane suka dinga lekowa turakata suna barin sakonnin fatan alheri da addu'o'i a gareni, kuma fatan alherin bai tsaya gareni ba ni kadai har Zainab jama'a da dama sunyi mata addu'ah da fatan alheri a dalilin wannan rana. Ba shakka naji dad'in wannan al'amari, da ni da Zainab muka kasance cikin adduoinku a jiya.

Muna matu'kar godiya a gareku baki daya. Da so samu ne nabi dukkan wadan da duka aiko da sako nai musu godiya a jikin sakon, amma kasancewar abin da yawa ban samu dama ba, amma duk wanda ya aiko da sakon na gani kuma naji dadi.

Ba shakka hakan na nufin ina kara kusa ga ajalina ne, na shirya ko ban shirya. A shekarun da aka diba min naci wani adadi daga ciki. Ina rokon Allah ya amsa dukkan adduoinku na alkhairi da kuka yi mana. Ina kuma fatan hakan ya zama tuni a gareni cewar ako da yaushe ina iya riskar ajali. Allah ya sa yadda muka zo muna masu Imani da Allah mu koma muna masu Imani a gareshi Subhanahu wata'ala.

Nima zan d'an koma baya na tunawa kaina baya dan na fahimci yadda rayuwa ta sauya a gareni. Wannan hoto da kuke gani an dauke shi a shekarar 1988. Wannan yaron da kuke gani ni ne. Yau gashi gabbai sunyi tsawo gashi ya baibaye fuska. Akwana a tashi ance jariri ango ne.

Amadadina da Zainab da dukkan 'yan uwa d danginmu muna muku godiya da fatan alheri. Allah ya saka da alheri ya bar zumunci.

Yasir Ramadan Gwale
03-10-2014

Nasiru Sufi



NASIR SUFI: A madadin ni da Zainab muna taya abokinmu Malam Nasiru Sufi Junior murnar kammala karatu da samu daraja ta farko First Class a jami'ar Ming Chuan University dake a Taiwan. Muna fatan alheri da fatan samun nasara a rayuwarka Malam Sufi. Allah ya yi maka jagora.

Yasir Ramadan Gwale
01-10-2014