Wednesday, May 25, 2016

MALAM SALIHU SAGIR TAKAI : GASKIYA MATAKIN NASARA


MALAM SALIHU SAGIR TAKAI: GASKIYA MATAKIN NASARA 

Kwanakin baya wani bawan Allah ya samu Malam Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano yake shaida masa cewar; indai ana son aci zabe to ya kamata a sauya Malam Salihu Sagir Takai a matsayin dan takararmu. Domin a cewar sa Kano ba irin Takai take bukata ba, ya cigaba da cewar, Jihar Kano na bukatar mutum marar kunya wanda zai iya taka kowa kuma yayi rashin mutunci ba wanda zai tanka masa, ya buda misali da wanda suka gabata wai a samo mutum mutakabbiri Mai Takalmin Karfe. 

Gama bayanin sa ke da wuya, Sai Sardaunan Kano, yayi Hamdala ya godewa Allah. Ya kada baki yace masa, Alal hakika wad'annan bayanai naka akan Malam Salihu sun sake tabbatar min da abinda na sani kuma nake da yak'ini akansa. Duk abin da ka fad'a, ya kara tabbatar min da cewar ba ko Shakka Malam Salihu Sagir Takai mutumin kirki ne mai gaskiya da rikon Amana, mai girmama mutane da sanin ya kamata. Kuma wad'annan bayanai naka sun k'ara nuna mana cewar Lallai Malam Salihu shi ne mutumin da ya cancanci mu saka a gaba domin samun Nasara.

Bahaushe yace wai a san mutum a san cinikinsa. Ko da yaushe ana san mutumin kirki ya kasance yana nan yadda aka sanshi, rud'i da bukata ba zasu tab'a sanya shi ya canza daga mutumin kirki yayi sako-sako ba dan neman biyan wata bukata. Alal hakika wannan hali na Malam Salihu Sagir Takai ya sanya muka ce mun ji mun gani har gobe har jibi muna yinsa a matsayin dan takarar Gwamnan Kano. Muna da yakini, kuma mun kyautata zato ga Allah cewar alkhairai da mukewa Malam Salihu zato akansu suna nan.

Nayi matukar farinciki lokacin da naga Farfesa Salisu Shehu BUK yayi kalamai na Yabo akan Malam Salihu bisa wannan Waki'a da ta same shi. Ya k'ara tabbatar min da abinda na jima ina ji ana fad'a akan Malam Salihu Sagir Takai. Ya ya be shi, kuma yayi masa shaida ta gari, ya kuma tabbatar da cewar tun da can haka ya sanshi mutumin kirki mai amana. Daman kuma, shaidar duniya ita ce Shaidar Lahira inji Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam. 

Mutanan Alkhairi, masu mutunci da daraja su baka shaida cewar kai mutumin kirki ne mai mutunci da karamci da amana. Wannan kadai Nasara ce a rayuwa. Ina taya Malam Salihu Sagir Takai murnar wannan shaida da ya samu daga bakin mutumin kirki, Farfesa Salisu Shehu BUK. Muna maka  fatan alheri da fatan cigaba da dorewa akan yadda muka sanka kuma muke jin labarin ka da kuma yadda jama’a sukai maka shaida ta alkhairi. Ina addu'ah ta musamman ga wannan bawan Allah Malam Salihu Sagir Takai. 

Ya Allah ka tsare shi ka tsare masa Imaninsa, Allah ka yi masa jagoranci a dukkan lamuran sa na rayuwa, Ya Allah Kada ka jarrabe shi da abinda ba zai iya ba. Allah ka azurta Kano da samun Malam Salihu Sagir Takai a matsayin Gwamna. Allah ka shige masa gaba kayi riko da hannunsa, Allah Kada ka barshi da iyawarsa. Allah ka baiwa Malam Salihu Sagir Takai Gwamnan Kano a 2019. Amin Summa Amin. 

Yasir Ramadan Gwale 
25-05-2016