Tuesday, December 31, 2013

Gwaro Na A Shekarar 2013, A Facebook!!!

GWARZO NA A SHEKARAR 2013, A FACEBOOK!!!

A wannan shekara da muke yin bankwana da ita a yau, na zabi Malam Najib Aliyu Harazimi a matsayin Gwarona na wannan shekara. Ba shakka, na jima ina bibiyar dukkan irin sakonnin da Najib yake yadawa a facebook, mutum ne mai son yada alkhairi da kokarin shiryar da mutane zuwa ga hanya ta gaskiya. Hakika, irin sakonnin da yake sakowa a koda yaushe sukan yi tasiri a gareni ainun, sau da dama idan naga ya yi wani tsokaci nakan zata kai tsaye da ni yake. Haka kuma, idan naga yayi wata addu'ah sai na dauka kamar ya san irin hali ko yana yin da nake ciki, ba shakka, Najib yana daga cikin mutanan da nake karuwa da su sosan-gaske a facebook da ire-irensa da dama.

Najib, na zabeka a matsayin gwarzo na, na wannan shekarar, dan ka dace ka kuma cancanta da na zabeka. Kuma na zabeka ne dan nuna godiya da yabawa da irin sakonnin da kake yi na fadakarwa a ko da yaushe, ina kira a gareka, kada ka ja da baya akan wannan aikin alkhairi da kake yi. Ina kuma kira a gareka, da ka jajirce wajen cigaba da neman ilimi da yadashi. Kuma ka kasance, kana aiwatar da abinda kake shiryar da mutane izuwa gareshi, kada ka zama irin wadan da suke shiryar da mutane zuwa ga aikin alkhairi amma su basa yi. Ina yi maka fatan alheri da fatan samun kyakykyawan sakamako a wannan aikin alkhairi da kake yi. Na gode.

Yasir Ramadan Gwale
31-12-2013

Monday, December 30, 2013

Iran


IRAN: Duk wani yunkuri na dakushe tare da rage karfi da tasirin Kasar Iran a yankin gabas ta tsakiya, musamman a kasashen Lubnan da Suriya da Iraqi abu ne da ya kamata ya samu goyon baya daga dukkanninmu. Muna maraba da dukkan wani yunkuri akan haka. Iran ta zama iblishiya a tsakanin kasashen Gabas ta tsakiya, ta hada-kai da Israela ana ta wasa da hankulan mutane dangane da makamin Nukiliya. Suna karfafa Hiz-bola tana kashe mutane a Lubnan, sun kashe Rafeeq Alhariri Rahimahullah, sun kuma kashe Mumammad Shattah. Suna kuma taimakon Bashar Asad dan Ta'adda yana kashe talakawa bayin Allah a suriya. Sannan kuma, sun mayar da Iraqi tamkar wata jiha ce a cikin Farisa ta hanyar bayar da umarni ga karen farautarsu Nuri Maliki dan ta'adda. Muna nuna cikakken goyon bayanmu akan dankwafar da Iran. Ina kuma da yakinin za'a cimma Nasara, dan Allah yana taimakon duk inda gaskiya take komai karancin masu yi mata biyayya. Allah ka rusa duk wasu masu yiwa Addini zagon kasa suna basaja a cikin musulmi.

YASIR RAMADAN GWALE
29-12-2013

Saturday, December 28, 2013

Bayan Tattaki Kuma Sai Me?

BAYAN TATTAKI KUMA SAI ME?

Yanzu dai angama Ibadar da 'yan Shia'h suka yi a Husainiyya dake Zariya da sukawo Tattaki daga gurare masu nisa. Wanda a ranar wannan taro nasu muka jiyo Nuri Maliki Mai Gasa-Burodi a Bagadaza wanda yanzu prime Minister ne na Iraqi Bayan Shahadar Marigayi Saddam Hussein Rahimahullah yana cewa Musulmi su mayar da Alkibla zuwa KARBALA domin anan ne Kabarin Sayyaidina Husain Ibn Ali Ibn Abi-Talib (Radiyallahu Anhu) yake. Shin ko Maliki ya mance da cew
ar Kabarin kakan Husain baban mahaifiyar Husain Annabi Muhammadu Dan-Abdullahi cikamakin Annabawa yana garin Madina Al-munawwarah ne, watakila ko bai sani ba ne. To amma su Masu bakaken kaya na Najeriya da basa iya zuwa Karbala a irin wannan ranar har suma zasu dinga kallon Karbala ne ko kuwa su GYALLESU zasu dinga Kallo yayin da zasu yi tasu ibadar? Dan Allah ku bani labari shin Masu Tattakin nan a kafa suka juyo zuwa mazaunansu ko kuwa ladan zuwa (safa) ya ishesu, ba sai sunyi (marwa) ba suka hawo ababen hawa dan komawa gida? Sannan kuma, bayan da a yanzu suka yi Idin-Ghadir da Idin Ashura sai kuma meye ya rage? Sai naji daga gareku.

Yasir Ramadan Gwale
28-12-13

Tuesday, December 24, 2013

Wane Darasi 'Yan Arewacin Najeriya Zasu Dauka Daga Sudan Ta Kudu 2


WANE DARASI 'YAN AREWACIN NAJERIYA ZASU DAUKA DAGA SUDAN TA KUDU? [2]

A lokacin da gwamnatin Sudan dake Khartoum ta ci garin Abye mai arzikin manfetur a shekarar bara waccan inda suka fatattaki sojojin Sudan ta Kudu daga yankin, shugaba Omar Albashir yayi wani abu na ba sabamba, inda ya sanya khakin soja ya yi wata Khuduba a ranar juma'ar da suka samu wannan nasara ya sanyawa Hudubar suna "Juwwa Juba" wato sai sun shiga har juba sun cita da yaki. Watakila irin wannan abin da shugaba Bashir yayi shi ne ya burge Shugaban Sudan ta kudu Silva Mayardit Kiir Mai Malafa, a talatar makon da ta gabata aka wayi gari da harbe-harbe a cikin Birnin Juba kawai shima sai aka ga Shugaba Kiir cikin Khakin Soja yayin taron manema labarai, a inda akai ta mamaki kuma abin ya zama abin zolaya ga shugaba Kiir a tsakanin Jaridun Khartoum.

Mutanan Sudan ta kudu suna zaton idan suka balle daga Sudan shi kenan rayuwa zata zamar musu sabuwa su yi ware-wake, su yi duk irin yadda suke so. Amma ina abin ba haka bane, domin Tun bayan ballewarsu, suka yi ta samun kalubale masu yawa da suka hada da rikicin yankin Abye mai arzukin mai, da hadin-kan-kasa da kuma tsaffin 'yan tawayen SPLM da suka jima da makamai a hannunsu suna yawo, da kuma batun gina kasa da Ilimi da kiwon lafiya da noma da sauransu. Duk da irin wannan kalubale dake gaban Gwamnatin Silva Mayardit Kiir Mai Malafa, maimakon ya hada kan al'ummomin kasar wajen ciyar da kasar gaba, sai ya dabarbarce yayi ta jidar dukiyar kasar yana tarawa a cewar masu hamayya da gwamnatinsa karkashin jagorancin Reak Machar.

Yana da kyau mu sani cewar Mutanan Kudancin Sudan kusan mafiya yawansu sun saba da yaki, kuma sun saba da gudun hijira, dan gabaki dayan rayuwarsu a haka ta taso. Dan haka ne da aka wayi gari da wannan harbe-harbe a Juba tsakanin Dakarun Reak Machar da na Gwamnatin Kiir Mai Malafa, jama'a da dama suka dinga diban tsummokaransu da katifu suna zuwa ofisoshin majalisar dinkin duniya dan samun mafaka. A lokacin da Shugaba Kiir ya tashi yin taron manema labarai ya ambaci sunan tsohon mataimakinsa Reak Machar da cewa shi ne ya haddasa wannan tashin tashi-na, abinda wasu manzarta suke ganin Kiir yayi azarbabin kama sunan Machar, mutumin da a yanzu yake neman goyon bayansa dan dawo da doka da oda. Haka kuma, wani dalili da zai nuna gazawar Gwamnatin kiir shi ne yadda cikin kankanin lokaci aka karbe ikon Jihar Unity da Upper Nile daga hannun gwamnati abinda ya nuna daman can gwamnati ba tada wani tanadi ingantacce na tsaron kasa.

Darasin da masu fatan ganin Arewa ta zama kasa mai cin gashin kanta bayan ta yanke daga Najeriya shi ne, za'a samu tsananin gaba da kiyayya tsakanin Musulmi da Kiristoci a Arewa. A sudan ta Kudu matsalarsu kabila ce kawai, dan haka, lamari ne da ake iya warware shi akan tebur, amma dangane da Arewacin Najeriya batu ne za'ai na addini tsakanin Hausa/Fulani-Musulmi da sauran Kabilun Idoma/Berom/Tarok-Kiristoci da sauran kananan kabilun da suke Arewa. Wannan shi ne abinda zai sabbaba rashin jituwa mai tsananin gaske, abida ka iya kaiwa zuwa ga gwabza yaki, da dama suna ganin Idan mu Arewa muka balle shi kenan zamu tafiyar da rayuwarmu yadda muka ga dama. Sabanin yadda muke a dunkulalliyar Najeriya inda ake kudu da Arewa. Ba shakka sharrin da zai biyo bayan darewar najeriya sai an gwammace inama dai ba'a rabu ba! Akwai illoli masu yawa wadan da darewar Najeriya zata haifar. Dan haka wannan turka-turka ta kasar Sudan Ta kudu take zaman babban Darasi ga 'yan Najeriya musamman mu 'yan Arewa.

Yasir Ramadan Gwale
24-12-13

Monday, December 23, 2013

Wane Darasi 'Yan Arewacin Najeriya Zasu Dauka Daga Sudan Ta Kudu?

WANE DARASI 'YAN AREWACIN NAJERIYA ZASU DAUKA DAGA SUDAN TA KUDU?

Abin da ya faru a makon da ya wuce na barkewar rikici a tsakanin jaririyar kasar Sudan ta kudu ya zowa da mutane da dama da bazata. Kamar yadda galibin al'ummar kudancin Sudan suka dinga korafin cewar Larabawan da suke Mulki a dunkulalliyar kasar Sudan sun ware su, kuma an hana musu dama ta yin rawar gaban hantsi, irin wannan zance da sauran zuga da dama ta sanya al'ummar dake zaune a Sudan ta Kudu suka jefa kuri'ah da gagarumin rinjayen ballewa daga kasar Sudan, bayan da Shugaba Omar Hasan Albashir ya basu damar kasancewa a dunkulalliyar Sudan ko kuma ballewa, wannan ta sanya galibin kabilun wannan yanki suka zabi ballewa daga Sudan. Wannan ballewar tasu ta zama tofin Allah-tsine ga tsohon jagoransu John Garang wanda ya tsaya kai da fata wajen ganin al'ummarsa basu balle daga Sudan ba duk kuwa da zuga da matsin lamba da yake sha daga kasashen waje akan yin hakan.

Bayan mutuwar Garang a wani yanayi mai cike da ayar tambaya, wanda dan kabilar Dinka ne masu rinjaye, aka nada Silva Kiir a matsayin sabon magajinsa, kuma shugaban al'ummar kudancin Sudan a gwamnatin Bashir dake Khartoum. Kiir shima dan kabilar Dinka ne, wannan kabila sune mafiya rinjaye a cikin dukkan kabilun da suke zaune a wannan yanki na kudancin Sudan, sun linka kabilun Nuer da Meseriya da sauransu yawa nesa ba kusa ba. Kabilar Nuer su ne suke biyewa Dinka wajen yawan jama'a a kudancin Sudan. Amma wani abin Sha'awa shi ne, su kabilar Nuer duk da rashin rinjayensu a kasar amma su ne suke da rinjayen wadan da suka yi karatun Boko, wannan ta sanya suka fi dukkan kabilun yankin wayewa da saukin lamari.

Shi wannan shugaba Silva Kiir, mutum ne da ya taso a gaba dayan rayuwarsa bai san komai ba sai yaki, da zaman kadaici a cikin daji irin na sojoji, dan haka ko makaranta bai yi ba da zata bashi damar gogewa da kuma gogayya. A saboda haka ne, a lokacin da suka samun 'yancinsu daga Sudan, kuma ga arzikin manfetur Allah ya huwace musu, akai ta fadin tashin kafa gwamnatin hadin kan-kasa, a Naivasha ta kasar Kenya suka cimma yarjejeniya da kabilar Nuer wajen tafiya tare, dan gina sabuwar kasar tasu mai cike da kalubale. Tun farkon kamun ludayin Gwamnatin Kiir masu sharhi suka fahimci cewar lallai ba zai jima ba za'a samu gagarumar baraka a cikin gwamnatinsa, don na farko kamar yadda na fada, bai yi karatu ba, kuma ba shida wata wayewa ko gogewa da zata bashi damar hada kan al'ummar kasar. Dan haka ne ba shida wani aiki face daukar zuga ko abinda aka sanya shi yi daga kasashen da suke hankoron Man-fetur din kasar ta ke da shi.

Yana daga cikin dalilin da ya sanya a karon farko ya samu sabani da 'yan kabilar Nuer din da dake cikin gwamnatinsa. Don sum fahimci babu inda shugaban ya sa gaba, face tara dukiyar haramun da kuma jiran umarni daga kasashen waje, matsin lamba da caccakar da 'yan Kabilar Nuer dake cikin gwamnatinsa ta sanya, rana a tsaka ya bayar da sanarwar korar jami'an gwamnatinsa gaba daya! Abin da ba'a taba yi ba a duniya, wannan al'amari ya harzuka 'yan Kabilar Nuer bisa jagorancin mutumin da shi ne mataimakin shugaban kasa Reak Machar. Shi Reak mutum ne dan boko wanda yayi ilimi zamani mai zurfi kuma gogagge ta fuskar mu'amala.

Zan cigaba In Sha Allah.

Yasir Ramadan Gwale
23-12-13

Saturday, December 21, 2013

Obasanjo Ne Fa . . . Gwanki Mai Rangwangwan!!!


OBASANJO NE FA . . . GWANKI MAI RANGWANGWAN!!!

Wasikar da aka ruwaito tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo ya rubutawa Shugaban kasa Goodluck Jonathan ta janyo masa farin jini da yawa a wajen mutane masu saurin manta abinda ya faru a baya. Ba shakka yana da kyau mu tunawa kanmu waye Obasanjo a wajenmu ('Yan Arewa), sannan kuma mu tambayi kanmu, Shin Allah ne ya shiryi Obasanjo? Sannan kuma, halin da muke ciki mawuyaci na koma baya ta fuskar tattalin arziki, da lalacewar harkar ilimi, da koma baya ta fuskar Noma da kiwo, da lalacewar harkokin tsaro da fatara da yunwa da cututtuka da sauransu, wadannan wasu lamura ne da mu mutanan Arewa bama bukatar Obasanjo ya sanar da mu wadannan lamura. Dukkan irin lalacewa da wannan gwamnati ta mai malafa ta yi da kuma gasa mana aya a hannu da ta yi, Obasanjo yana da kamasho a ciki ko mun yaba masa ko bamu yaba masa ba, domin shi ne silar samuwarta.

Kada mutanan Arewa mu yi saurin manta irin kitififi da kitumurmura da makircin da Obasanjo ya shirya mana a baya. Mutumin nan, shi ne fa ya yi dukkan mai yuwuwa wajen mayar da yankin Arewa baya ta fuskar tattalin arziki da karfin soja da ilimin boko da sauransu. Manyan sojojin Najeriya 'yan Arewa masu mukamin General da Brigadier da Major nawa ne suka rasa rayukansu a cikin wani yanayi mai cike da tuhuma a zamanin Obasanjo? 'Yan kasuwa nawa aka gurgunta bayan an kakkarya wasu a Arewa? Ina bankin da Arewa take takama da shi na Bank Of The North? Shin ba Obasanjo ne ya rusa shi ba, dan murkushe tattalin arzikinmu! Shin ba Obasanjo ne ya yi amfani da Kwanturola na Kwastam Jacob Gyang Buba ba wajen durkusar da kasuwannin jihar kano da na Arewacin Najeriya ba, ta hanyar bin mutane har cikin shagunansu ana kwashe musu kaya ana konewa dan tsabar zalunci da keta da mugunta? Shin yanzu har munyi saurin manta irin wannan manakisar da Oban-shegu ya yi mana?

Dukkan zaben da aka yi a baya tun daga 2003 har zuwa 2011 shin ba Obasanjo ne ya yi amfani da karfinsa ba wajen yin kaci-baka-ci ba, baka-ci-ba-kaci! Duk irin wannan shegantaka da tsiyataku da Obasanjo ya yi mana har muna da bakin da zamu yaba masa akan ya rubutawa Shugaban kasa Goodluck wata wasika da babu abin da zata rage na daga irin mawuyacin halin da muke ciki ba. Shin Obasanjo yanzu yana son nuna mana cewa a yanzu shi masoyin 'yan Arewa ne, yana gaya mana manakisar da wannan gwamnati ta shirya dan kashe wasu muhimman mutane? Mutum nawa aka kashe a Arewa da Najeriya baki daya wanda Obasajo ya kamata ya yi bayanin yadda aka yi kisan kuma aka kasa gano wadan da suka yi kisan!

Obasanjo yana shugabancin Kwamitin Amintattu na Jam'iyyar PDP, tsohon mashawarcin kasa ta fuskar tsaro Marigayi Andrew Azazi ya yi bayanin cewar PDP su ne BOKO HARAM, Shin ina Obasanjo yake a lokacin? Ko Azazi yace banda Obasanjo ne? A saboda a wautar da hankalin mutane sai aka ce wai Obasanjo zai je Maiduguri domin sasanta Gwamnatin Borno da 'Yan Boko Haram, a yi wasa da hankulanmu, shin zamu iya gamsuwa cewa babu hannun Obasanjo a cikin duk wannan sabatta juyatta da ake yi ta fuskar tsaro ne? Ba obasanjo ne ya yi uwa yayi makarbiya ba wajen ganin ya daurewa wannan shugaban mai malafa gindi ya tsula dukkan irin tsiyar da yaga dama ba? Bai kamata mu yi saurin mancewa da abin da Obasanjo ya aikata mana ba, har mu dinga yekuwa da sunan cewa OBJ yayi abin kai fitsari da kumfa! Kamar yadda na fada, shin muna bukatar Obasanjo ya fada mana halin da muke ciki, ko ya ce mana za'a kashe mu? Ina kisan da ya yi mana a baya? Shedan ya fadi magana Manzon Allah SAW ya ce abinda ya fada gaskiya ne, amma shi din makaryaci ne, dan haka gaskiyar da ya fada bata tsarkakeshi daga kan batan da yake kai ba; to haka shima Obasanjo.

Obasanjo ya fahimci 'yan Arewa sarai dan haka ya gama rainamu ya yi dukkan irin wasan da yaga dama da hankulanmu. Domin ya fahimci yanzu duk wani wanda zai samu farin jini da karbuwa musamman a wajen 'yan Arewa to ya kalubalanci gwamnatin mai malafa, dan haka ya fito da wannan sigar dan ya mantar da mu abin da ya faru a baya na badakalar da ya tafka a Kwangilar Wutar Lantarki ta Dala Biliyan Goma sha shida ($16B) ya mantar da mu badakalar da su Cif Tony Anineh da su Bode George suka tafka a karkashin gwamnatinsa.

Ni a ganina, wannan wasika ta Obasanjo tana da fuskar silai (mutum ko Doki), Abu na farko shi ne, ficewar Gwamnonin PDP guda biyar babu shakka sun batawa Obasanjo rai, dan bai so haka ba, dan haka bari yayi amfani da wannan dama ya caccaki mutumin da 'yan Arewa suke tsananin kyamata da nunawa gaba, ta hanyar nuna mana cewar yanzu Mulki rabon 'yan Arewa ne, bayan mun san da cewar yayi dukkan abin da zai iya wajen murdewa kundin tsarin mulkin Najeriya wuya dan ya zarce a karo na uku Allah bai nufa ba, ko waccan Tazarce ba 'yan Arewa ya so ya yiwa sata ba? Duk da mun hana shi wucewa ba dan yana so ba, muka zuba masa ido ya zabo mana wanda yaga dama a matsayin wanda zai gajeshi, kuma, muka ce masa "sami'ina wa'ada'na". Dan haka, duk wani sabani da za'a samu tsakanin Obasanjo da Goodluck ko da kuwa OBJ zai halaka mahaifiyar Shugaban kasa ba shakka zasu gyarota a tsakaninsu.

Abu na biyu, Obasanjo ya hango hadarin da yake tunkaro PDP ba mai ruwa bane, hadari ne mai tafe da kura da guguwa da zata yi awon gaba da duk abinda ta samu, dan haka bari ya yi riga malam Masallaci; tunda ya fahimci cewar duk wanda zai yi farin jini a idan APC to ya caccaki shugaban kasa Jonathan, komai lalacewarsa hakan zata bashi kima a wajen APC tunda anyi walkiya yaga wallensu. Ni a ganina wadannan dalilai guda biyu suka sanya Obasanjo rubuta wannan wasika, idan tayi ruwa rijiya, idan kuma tayi fako shadda ce, yasan indai APC ta kafa gwamnati a kalla ya wanke kansa ta hanyar caccakar gwamnatin GEJ da tsinken-tsire, idan kuma abin Allah ya kiyaye GEJ ya kai labari, to babu shakka zai gyarota tsakaninsa da Shugaban kasa, kamar yadda muka hangosu a Nairobi da Soweto suna musabiha cikin annashuwa bayan aikewa da wannan wasikar. Hausawa sun ce a Juri 'Bara Albasa Fara Ce.

Yasir Ramadan Gwale
21-12-2013

Thursday, December 12, 2013

Obasanjo Ya Fadi Gaskiya, Amma Mai Zunubi Ne

OBASANJO YA FADI GASKIYA, AMMA MAI ZUNUBI NE

Ba shakka wasikar da tsohon shugaban kasa Obasanjo ya aikewa Shugaban kasa Goodluck Jonathan ya yi bayanai na gaskiya da dattako. Obasanjo saninmu ne ba wani mutum bane mai gaskiya, yana daga cikin ummul haba'isin duk halin da muke ciki na kaskanci da koma baya a kasarnan Musamman yankin Arewa, bamu manta da yadda ya lalata mana tattalin arziki ba ta hanyar amfani da karnukan farautarsa, ya nakastamu ta fannin karfin soja. Ya mayar da mu baya a harkar noma da kiwo da muke tunkaho da shi, a gefe guda kuma ya daga darajar noma da kiwo a yankin kudancin Najeriya. Bamu manta da irin yadda ya yi amfani da murar suntsaye ba ya nakasta da dama daga cikin manyan manoman arewa ba.

Hakika laifukan da Obasanjo ya tafka a wannan kasa ba zasu lissafu ba cikin kankanin lokaci. Anyi kwangiloli na rainin wayo da raina 'yan Najeriya, bamu manta da kwangilar Naira Biliyan 200 da aka sanya Cif Tony Anineh ba, akan gyaran manyan hanyoyin gwamnain tarayya ba, wanda babu kudin babu dalilinsu, kuma babu aikin, bamu manta da badakalar kudin wutar lantarki ba. Da dumbin laifuka da zunubbai da ya aikatawa al'ummar Najeriya duk suna nan rubuce a cikin daftarinmu.

Babban laifinsa mafi muni, shi ne yadda yayi uwa yayi makarbiya wajen shigowa da 'yan Najeriya da haramtacciyar Gwamnati a 2007. Saninmu ne shi ne ya daurewa Marigayi Malam Umaru Musa YarAdua (Allah ya jikansa da rahama) gindi wajen yakai labari ko ta halin-kaka. Shi ne kuma ya daurewa Wannan mugun shugaban kasar gindi wajen dawowa a matsayin magajin Umaru YarAdua. Har yanzu wannan ciwo da miki da Obasanjo ya aikata mana bai warke ba a zukatanmu.

Ba haushe ya yi gaskiya, yace gaskiya ko ta karece a bashi abarsa! Kuma haka addinin Musulunci ya horemu. Ba shakka Duk da waccan balbalcewa da lalacewa ta Obasanjo yayi gaskiya akan abinda ya fada game da yadda Shugaban kasa Goodluck yake tafiyar da harkokin wannan kasa. Masana sun jima da fadin cewa, a tarihi ba'a taba samun shugaban kasar da bai san me yake yi ba, irin wannan mugun mayaudarin shugaban kasar, Azzalumi maketaci, mayaudari wanda baya son al'ummar Najeriya da alheri ko na sisin kwabo. Ya mayar da kasarnan baya ta ko ina, ya lalata komai. Ya daurewa cin hanci da rashawa gindi, ya mayar da aikata zunubbai tamkar Ibada.

Anyi hasarar dumbin rayukan talakawa bayin Allah da basu san hawa ba balle sauka a wannan muguwa Azzalumar gwamnti. Mutane da yawa sun talauce a sanadiyar kona musu dukiyoyinsu a jihohi da dama a Arewa. Barna da ta'adi da wawaso da facaka sun zama sune abinda kowa ke alakanta wannan gwamnati da shi ciki da wajen Najeriya. Ya sace dukiyar kasa shi da wasu tsirarun 'yan iska maciya amanar kasarsu, marasa kishi, sun zamar mana Alaka-kai. Babu shakka dukkan dangin wani kasawa ya tabbata akan wannan shugaban kasa, mugu ne, maketaci ne, Azzalumi ne, 'yan Najeriya birni da kauye sun gaji da wannan gwamnati. Dan haka dole mu yabawa Obasanjo akan abinda ya fada dan gane da wannan shugaban kasa da Azzalumar Gwamnatinsa. Allah ya yi mana canji mai amfani a 2015.

Yasir Ramadan Gwale
12-12-13

Sheikh Aliyu Harazumi Hausawa


SHEIKH ALIYU HARAZUMI: Ina mai bin sahun dimbin al'ummar Musulmi musamman na jihar Kano da karamar hukumar Gwale wajen nuna alhininmu bisa rashi na Shehun Malami Sheikh Aliyu Harazumi, hakika dukkan mai rai mamaci ne, kasancewarmu a raye babban dalili ne da yake tabbatar mana da cewa Mutuwa na nan tana jiranmu komai tsawon lokacin da muka diba a rayuwa. Mutuwa ita ce mai yanke dukkan hanzarin abin halitta da yake motsi a ban kasa, dole zuciya ta kadu idanu su raurawa hankali ya dugunzuma, a yayin da mutum yayi rashin wani nasa musamman mutum irin Sheikh Harazumi da yayi tasiri a zukatan mutane da yawa. Muna baiwa juna hakuri a bisa wannan rashi, muna kuma tunasar da juna cewa wannan sunnar Allah ce, kamar yadda ya fada a cikin littafinsa mai tsarki cewa dukkan mai rai sai ya dandana radadin mutuwa. Haka nan kowannemu zai riski wa'adinsa, babu tsumi babu dabara a lokacin da wa'adi yayi. Ba shakka a wannan lokacin anyi rashe-rashe na Malamai irin s Sheikhu Na'ibi Sulaiman Wali da Sheikh Isah Waziri da kuma wannan ta sheikh Aliyu Harazumi.

Ya 'yan uwa na masu girma, hakika a rayuwa babu wani wa'azi da yakai mutuwa. Ba shakka mutuwa ita ce Muntaha a rayuwar dan adam, lallai mu nustu, mu fadaka, mu sani, mu ba mazauna bane, yadda muke fadan cewa wane da wane sun rigamu gidan gaskiya, haka muma wataran za'a bayar da labarin tafiyarmu inda babu dawowa, dan haka nake jan hankalinmu da mu jajirce wajen yiwa wannan tafiya Guzuri na tsoron Allah da Imani da kadaita Allah da bauta, tare da yawan Istigfari da Hailala da karatun Al-Qur'ani. Allah ya bamu ikon tafiya, Allah ya rinjayar da kyawawan ayyukanmu akan sikelin ranar Alkiyama. Ranar da Allah ya kirata da sunaye da yawa dan jan hankin bayi na gari masu kadaitashi da bauta. Allah ka jikan mamatanmu, da 'yan uwanmu da malamanmu da dukkan al'ummar Musulmi a duk inda suke a duniya.

YASIR RAMADAN GWALE
12-12-13

Monday, December 2, 2013

Kamun Da SSS Sukaiwa Sheikh Nazifi Yunus Jos: An Fake Da Guzuma . . .

KAMUN DA SSS SUKAIWA  SHEIKH NAZIFI YUNUS JOS: AN FAKE DA GUZUMA . . .

Ba shakka kamun da hukumar SSS ta yiwa Dr. Yunus Jos dangane da zarginsa da ake yi da alaka da Boko Haram, ko kasancewa dan Boko Haram wani al'amari mai daure kai. An je har gidansa cikin tsakar dare aka kama shi a lokacin da yake tare da iyalinsa, aka keta masa haddi, aka ci zarafinsa, aka kuma yi masa dai-dai da kayan gidansa da nufin bincike dan samun wasu abubuwa da ake zargin 'yan BH na amfani da su wajen tayar da hanali, sai dai cikin ikon Allah haka aka fita ba tare da an samu ko da matsefata da sunan an ajiye dan tayar da hankali ba a gidansa.

Shugabar hukumar SSS Maryellen Ogar ta sha sharara karya akan zargin mutane da Boko Haram. Kamar yadda kowa ya sani ne, haka suka kashe matasa basu san hawa ba, basu san sauka ba a Apo a Abuja a kwanakin baya, da nufin zargin matasan da kasancewa 'yan BH. Abin tambaya, daman doka ta bayar da iznin kashe mutumin da ake zargi mai lafi ne? Na zata cewar ko mutum aka kama dumu-dumu yana aikata laifi sai an gabatar da shi gaban Shar'ah daga bisani kotu ta yi masa hukunci. Amma kiri-kiri ake keta haddin Mutane a Najeriya dan kawai su Musulmi ne, a kashe su ba da hakki ba, laifinsu kawai sunyi Imani da Allah da Manzon Allah. Muna fahimtar irin wannan sunkuru da hukumar SSS take yi karkashin wannan arniyar kokari ne na dakushe Musulunci da kuma fada da Musulmi a kai-kaice. Kawai an fake da BH ne dan a cuzgunawa Musulmi.

Duk wani Musulmi na gari a Najeriya yana yin Allah-wadai da dukkan wani Nau'i na tayar da hankali, kamar yadda addinin Musulunci yayi haramcin tayar da hankalin Mutanan da basu san hawa ba balle sauka, balle kuma har ta kai ga daukar makamai a dumfari mutane haka kurum a kawo karshen rayuwarsu ba tare da sun aikata wani laifi da suka cancanci hakan ba. Mun yi tir da dukkan wani dangi na zubar da jinin bayanin Allah, kuma ko waye ya aikata hakan muna kiran doka ta yi aiki akansa matukar an kama shi da laifi ko musulmi ne ko ba musulmi bane. Amma abin ya zama rainin wayo da rainin hankali, domin Kiristoci nawa aka kama dauke da makamai a Arewacin Najeriya zasu tayar da hankali, har Kwanturola na Kwastan aka kama da safarar makamai ta barauniyar hanya, amma me aka yi musu? Saboda kawai su Kiristoci ne suna da uwa a gindin murhu! Adalci shi ne a yiwa duk wanda aka kama da laifi hukunci dai-dai da abinda ya aikata ko daga wane yanki yake ko meye addininsa, babu yadda za'a maida wasu 'yan mowa wasu 'yan bora sannan a yi zatan dorewar zaman lafiya a tsakanin ko wacce irin al'umma; Mutum ko a tsakanin 'ya 'yansa ya fifita wani sai an samu rigima da rashin jituwa a tsakanin 'ya 'yan ballantana kuma al'ummar Najeriya da ake zaman doya da manja.

Bamu taba baiwa wani wanda ya aikata lafi kariya ba, ba kuma zamu taba zama inuwa daya da masu aikata laifuka dan basu kariya ba. Amma ya zama tilas a baiwa kowane dan kasa 'yancin walwala da yin addininsa kamar yadda kundin tsarin Muki ya bayar da dama, Kai ko tsarin Mulki bai bamu dama ba sai munyi Addinin Musulunci.  Lallai sai an baiwa kowa 'yancinsa, domin babu yadda za'a dinga bin malamai na Musulunci ana yi musu dauki dai-dai sannan a ce mana ana son zaman lafiya, alhali ga kiristoci can anyi shakulatun bangaro da batunsu. Ina hukumar SSS take lokacin da Dokubo Asari ya yi barzanar kashemu idan bamu zabi Jonathan ba a 2015? Suna ina shugaban kiristocin Najeriya Oritsejafor yake kalamai na ganganci da gatsali ga Musulmi? Me suka yi ko kuwa dan an raina mu. Ba shakka Allah yana tare da wadan da suka yi Imani suka bada gaskiya.

Yasir Ramadan Gwale
02-12-2013

Sunday, December 1, 2013

PDP: Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da G-7!!!

PDP: TSAKANIN FADAR SHUGABAN KASA DA G-7!!!

Tuni sanarwa ta gama karade ko ina cewar tsagin gwamnonin PDP guda bakwai da suka darewa uwar jam'iyyar PDP zasu gana da Shugaban kasa a yau. Kafin wannan ganawa dai an jima ana kai ruwa rana tsakanin wadannan Gwamnoni da fadar Shugaban kasa, har ta kai a ranar talatar da ta gabata, shugaban tsagin nPDP Alhaji Kawu Baraje ya bada wata sanarwa a dukunkune cewar sun hade tsakanin nPDP da kuma babbar jim'iyyar Hamayya ta APC. Tambayar da zamu yi anan ita ce, Shin Shugaban kasa zai gana da wadannan gwamnoni a matsayinsu na nPDP ne ko kuwa a matsayin sabbin Gwamnonin APC, ko kuma 'yan kan-katanga? Duk da cewar Gwamnan Jigawa da na Neja sun bayyana matsayarsu akan waccan sanarwa da Baraje ya bayar.

A ranar juma'ar da ta gabata, a cikin shirin BBCHausa na Ra'ayi Riga, sun tattauna wannan al'amari na turkaturkar PDP. A cikin wannan tattaunawa, sakataren tsare-tsare na PDP bangaren Bamanga Tukur Abdullahi Ibrahim Jalo ya yi wata tambaya mai muhimmanci, amma aka kewaye ba'a bashi amsar tambayar ba. Ya yi tambaya kamar haka, "Shin su wadannan Gwamnoni sun shiga APC ne a matsayin sauya sheka daga PDP zuwa APC, ko kuwa hadewa ce irin wadda ANPP da ACN da CPC suka yi" wannan tambaya tana da muhimmanci a yi bayaninta, amma cikin shirin aka kewaye mata. Domin bayan da Baraje ya bayar da wannan sanarwa, Gwamnan Jihar Kano Alh. Rabiu Kwankwaso ya yi wani bayani a BBC mai rudarwa kan cewa zasu koma su tattauna da jama'arsu sannan su yanke matsaya; wannan ya nuna cewar kamar ba su shiga APC din ba kenan.

Dangane da ita waccan tambaya da Jalo ya yi, yana da kyau suma APC su yi mana warwarar wannan al'amari, domin dai mun san cewar tsakanin ANPP da ACN da CPC da suka yi hadaka ba da baki suka yi ba, sai da kowacce ta mayar da satifiket dinta ga hukumar zabe sannan wannan hadewa ta tabbata, dan haka, su wadannan gwamnoni na nPDP sun dawo da nasu satifiket din ne ko anyafe musu, ko kuwa sauyin sheka suka yi? Wannan al'amari yana da kyau kada a dinga tafiya da 'yan Najeriya a dukunkune.

A dangane da Gwamnonin G-7, shin Me zai faru idan suka tabbatarwa da Shugaban kasa cewar suna nan daram dam dam a PDP? Bukatunsu a bayyane suke ga al'ummar Najeriya, manyan bukatunsu guda biyu dai sune na cewar (a) Dole Shugaban kasa ya ajiye batun tsayawa takara a 2015. (b) Dole a kori Bamanga Tukur. Anan ma zamu iya yin tambaya, shin wadannan Gwamnoni sun gamsu da yadda gwamnatin Jonathan ke tafiya ko kuwa kawai bukatarsu kada shugaban kasa ya tsaya zabe a 2015? Me ya sanya ba zasu tsaya kai da fata wajen ganin shugaban kasa da Gwamnatin Tarayya sun yiwa al'ummar Najeriya ko Arewa Adalci ba? Sanin kowa ne Shugaban kasa yana nuna bambanci da zalunci tsakanin bangarorin kasarnan a bayyane, babu wanda ya yi haka, idan banda gwamnan Kano da na Kwara da suka yi batun rashin adalci a tsarin rabon arzikin kasa na Man da ake tonowa a cikin Ruwa da kuma wanda ake tonowa a kan tsandaurin yankunan da suke da man (Off-shore da On-Shore) Wannan korafin wadannan gwamnoni sun yi ne a kashin kansu tun kafin haifar da G-7.

Ko shakka babu irin wadancan bukatu su ne suka damu al'ummar Najeriya. Dole a yiwa kowa adalci a baiwa ko wanne mai hakki hakkinsa, amma gabaki daya al'amarin PDP babu gaskiya a cikinta, da wanda yake zagin PDP da me yabonta duk ba masu gaskiya bane, illa nadiran indai 'yan PDP ne. Domin Atiku Abubakar da Abubakar Rimi babu irin abinda basu kira PDP ba, amma kuma suka yi mata kome daga baya. Yana da kyau al'ummar Najeriya su fadaka cewa, PDP wani gungu ne na 'yan MAFIA babu wani wanda ya isa ya kauce daga tsarin da aka gindaya, dole dan PDP ya yi mata aiki yana so ko baya so, ya yarda ko bai yarda ba, duk wanda yaci ladan kuturu dole ya mar aski. Yana da kyau mu sani su PDP wadannan gwamnoni basa tayar musu da hankali illa kawai tashin hankalinsu shi ne kada darewar wadannan Gwamnoni ta haifar da barakar da PDP zata rasa rinjaye a majalisar wakilai ta tarayya, amma indai tafiya zasu yi daga PDP ana iya hada musu da gyaran Gwamnonin Kebbi da Katsina da Bauchi. Kayar da PDP ba abu bane mai sauki, domin rijiyar da ta cika da datti da dagwalo baza a taba iya yasheta daga waje ba, ya zama dole a shiga ciki a kwarfe ruwan da yake ciki sannan a samu ruwa mai kyau, ko kuma a cike ta a sake tona wata. Dan haka, Gasa Rago A Murhun Alade Bai Zai Taba Haramta Naman Rago Ba.

YASIR RAMADAN GWALE
01-12-2013

Tuesday, November 26, 2013

Cuwa-Cuwar Da Hukumar Zabe Ta Tafka A Zaben Anambra


CUWA-CUWAR DA HUKUMAR ZABE TA YI A ZABEN ANAMBRA

Otumba Dino Melaye ya bankado wannan cuwa-cuwa da hukumar Zabe ta kasa ta yi a zaben Ranar 16 ga watan Nuwamba da aka gudanar a jihar Anambra.

Hukumar Zabe ta tabbatar sahihancin zaben da ya zo hannu kamar haka:

  • Kuri’un Da Aka Tantance 451,826.

  • Kuri’un Da Aka Soke 16,544.

  • Ida ka kwashe Kuri’ar da aka soke guda 16,544 a cikin kuri’un da aka tantance, ya zama akwai halastacciyar kuri’a 435,282.

  • Kur’ar da aka yi zabe da ita bayan an tantance ita ce 429,549. Wato hakan ya nuna cewar akwai mutum 5,733 da aka tantance su amma basu yi zabe ba.

  • Kuri’un da aka bata a yayin da aka gudanar da zabe ita ce 113,113. Wato idan ka dauki kuri’un da aka yi zabe da su 429,549 ka kwashe kuri’un da aka lalata 113,113, kana da sauran halattacciyar Kuri’a 316,436 da aka yi zabe da ita.

Haka kuma, sakamakon da yake a hannu yanzu wanda aka bayyana adadin kur’ar da kowacce jam’iyya ta samu ya nuna cewar:

  • AFGA- ta samu 174,710.

  • PDP- ta samu 94,956.

  • APC- ta samu 92,300

  • LP- ta samu 37,440

Wannan ya nuna idan ka lissafa kur’un da AFGA da PDP da APC da LP suka samu zai baka adadin kuri’u 399,406.

To anan tahuma zata taso, idan ka duba lissafin baya hukumar zabe tace adadin halastattun kuri’un da aka yi zabe da su sune 316,436, to ya aka yi da aka tashi rabawa abinda ko wacce jam’iyya ta samu adadin ya zarta ainihin kuri’un da aka fada. Domin idan ka hada lissafin abinda dukkan jam’iyyu suka samu zai baka kuri’a 399,406. Wannan zai tabbatar maka an samu Karin kur’a 82,970 akan ainihin kuri’a 316,549 da aka yi zabe da ita.

TAMBAYA: Shin ya akayi aka samu Karin 82,970? Kuma ina kuri’un da aka samu kari 82,970 suka shiga, AFGA ko PDP? Kuri’ar wacce Jam’iyya aka kwashe a cikin wadannan jam’iyyu aka karawa wata? Wannan tambaya ce da hukumar zabe zata bayar da amsarta.
Yasir Ramadan Gwale

26-11-2013

Sunday, November 24, 2013

Jaimhuriyar Musulunci Ko Jamhuriyar Shedanu!!!


JAMHURIYAR MUSULUNCI KO JAMHURIYAR SHEDANU!!!

Ba shakka, da ace wata kasa ce da ta ke ta Musulmi ce tsantsa kuma ta ayyana kanta a matsayin Jamhuriyar Musulunci, tabbaci hakika da ba zata kai labari ba, domin za’a dauki karan tsanar duniyarnan a dora mata, a saka mata takunkumai da turaku bila-adadun domin karyata. Amma da yake su kansu Kasashen Yamma sun san da cewar kasar IRAN karya suke, sunyi hannun riga da Addinin Musulunci, basu da alaka da shi ko ta kusa ko ta nesa, sai kaji Tuarawa na kururuwar Jamhuriyar Islama akan kasar Majusawa da Safawiyyawa da Rafidawa masu bautar wuta ta Farisa.

Abinda zai tabbatar maka da haka, shi ne yadda suke yin kutu-kutu, suke rusa duk wata Jam’iyyar Siyasa da ta bayyana kanta a matsayin Jam’iyyar Musulunci dan hanata kaiwa ga kafa Gwamnatin Musulunci. Duk wata jam’iyya da aka alamtata da sunan Musulunci, sai kaga an sa mata ido har a kawo karshenta, ko kuma a gurgunta ta a hanata aiwatar da ayyukan da su ne aka kafa ta akai. Ko kuma su lankaya mata kalamr “Ta’addanci” kamar yadda suka a Ghazza wa kungiyar kuma Jam’iyyar Hamas.

A dan haka, duk wani Musulmi na Hakika baya taba samun rudani idan yaji an kira kasar Farisa da sunan Jamhuriyar Musulunci, dan yasan Shifcin gizo ce, kuma, fankam fayo ce a bangaren addini domin fanko ce. Basu san komai ba sai barna da ta’adi da ashararanci da badala, da shantakewa da sheke aya.

Allah ya rusa masu yiwa Addinin Musulunci shigar shantun kadangare, masu yiwa addini zagon kasa. ‘Yan Damfarar addini. Allah ka baiwa Musulmi kariya daga Sharrinsu a ko da wane lokaci. Allah ka warware dukkan wani kulli da kitififi da suka shirya dan halakar da Musulmi, Allah ka afkar musu da dukkan sharrinsu akansu. Allah ka tabbatar da mu akan hanyar gaskiya komai wuya komai tsanani.

Yasir Ramadan Gwale

25-11-2013

Gwamnatin Angola Ta Haramta Addinin Musulunci


GWAMNATIN KASAR ANGOLA TA HARAMTA ADDININ MUSULUNCI 

Kusan yanzu za'a iya cewa kasar Angola ita ce kasa ta farko a duniya da ta fito a hukumance ta soke Addinin Musulunci a kasar, ta kuma bayar da umarnin rurrusa dukkan wasu Masallatai da suke a kasar. A cewar Ministan Al'adu da yawan bude Ido na kasar Rosa Cruz e Silva, Ma'aikatar Shar'ah da 'yancin walwala ta kasar bata bayar da izni ko damar aiwatar da Addinin Musulunci ba a kasar, a dan haka suka haramta Musulunci baki daya a kasar, Silva ta kara da cewa kasar Angola bata maraba da Musulmi ko daga ina yake a duniya.

Haka kuma, Silva ta kara bayanin cewar Haramcin ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin kasar ke kokarin  dakile dukkan wani abu da ya yi kama da nuna kishin Addini daga cikin addinan da hukuma ta amince da su aiwatar da ibadarsu. Dan haka dukkan wasu Masallatai zasu cigaba da kasancewa a rufe kafin rurrusa su. 

A nasa bangaren shima, shugaban kasar ta ANGOLA José Eduardo dos Santos ya ce wannan shi ne ya kawo karshen Musulmi da Addinin Musulunci a kasar ta Angola. Haka shima Gwamnan Babban birnin kasar Luanda Mista Bento Bento yace babu wata rana da gwamnatin zata Halatta Addinin Musulunci a kasar.

A cewar wasu bayanai na hukumar leken asirin kasar Amurka CIA kasar Angola na da adadin yawan Musulmi kimanin kashi 15 cikin dari ne. Jaridar Gwamnatin kasar Jornal de Angola ita ce ta ruwaito wannan labari.

Idan sunyi haka ne dan su samu Aminci da yarda a Turai da Amerika, basu san cewa akwai Masallaci a cikin fadar gwamnatin AMerika ba ne? Ba su san cewa akwai daruruwan Masallatai a kasashen Turai bane? Hakika ALLAH sai ya cika hasken Addininsa ko da kafurai da Mushurukai sunki. Manyan Kafurai irinsu Utba Ibn Rabi'ah da Abu Lahab da Shaiba Ibn Rabi'ah babu abinda ba su yi ba, su da addinin aka saukar da shi akan idonsu. Hakan nan Allah ya darkakesu, haka kuma zai darkake na kasar ANgola. ALLAHUMMA ALAIKA BIHIM. Musulmin Kasar Allah ka kai musu dauki.

Yasir Ramadan Gwale 
24-11-2013

Shugaban Kasa Na Sheke Ayarsa Tare Da Wasu Ministocinsa Mata


SHUGABAN KASA NA SHEKE AYARSA TARE DA MINISTOCINSA MATA.

Jaridar Sahara Reporters ta ruwaito cewar a lokacin bikin cikar shugaban kasa Shekara 56 a Landan bayan dab-dala da Da-dimar da aka kwana ana yi, Shugaban kuma ya gwangwaje tare da Ministar Albarkatun Manfetur Dieziani Allison Maduekwe a birnin Na Landan. Sahara Reporters sun ruwaito cewar bayan shan-gara da akayi a yayin wannan biki, ita ministar ta dauki Shugaban kasa inda suka fita su kadai ba tare da wani dan rakiya ya bisu ba a birnin Na Landan, Daga bayan sun dawo ne daga yawan da suka fita su kadai cikin Shugaban kasar ya murde, rahotanni sun tabbatarwa da Sahara  cewar ita ce mutum na karshe da ya gana da Shugaban kasa kafin daga bisani aka ji labarin ciwon da ya kwantar da shugaban a asibiti cikin gaggawa; a yayinda wasu rahotanni kuma suka ce Shugaban kasa yayi Mankas ne abinsa da Ruwan Kain-Kain me sanya jiri da hajijiya.

A kwanakin baya ma, sai da mijin ministar Sufuri Stella Oduah ya yi korafin cewar yana ganin sakonnin Tes na soyayya da Batsa da Shugabaan kasa yake aikowa da iyalin nasa akai-akai. Ance sai da mijin na Odua ya yiwa Shugaban kwamitin Amintattun PDP Cif Tony Anineh korafi akan cin-amanar da yake zargin Shugaban kasa yana yi masa, ina Mista Anineh din ya baiwa mutumin hakuri tare da alkawarin cewa zai yi kokarin takawa Shugaban Birki akan hakan.

Daman dai Tuni ake Zargin SHugaban kasa Goodluck Jonathan da aikata masha'a tare da wasu mata guda uku zuwa hudu, da akewa lakabi da Murhun Shugaban Kasa.

Yasir Ramadan Gwale 
24-11-2013

Thursday, November 21, 2013

Al-Amarin Kare Na Daga Cikin Abubuwan Ban Mamaki


AL-AMARIN KARE NA DAGA CIKIN ABUBUWAN BAN MAMAKI

Kare yana daga cikin dabbobin da Allah ya haramtawa Musulmi cin namansa. Ba shakka kare wata dabba ce da ba wata mai kima ko daraja ba ce a wajen mutane da dama, musamman Musulmi. Cikin ikonSa Subhanau Wata'ala, ya sanya fahimtar juna tsakanin Kare da Bil-Adama, babu shakka dukkan dabbobin da Allah ya hiltta babu wata dabba da ta kai kare sabo da Mutane, wannan ta sanya a kasashen Turai da Amerika ake lissafa kare a zaman daya daga cikin Iyalin gida, ko ahalin gida, kare yana samun kulawa ta musamman a wajensu. Sukan bashi wata irin daraja da ta shallake irin wadda wasu mutane suke samu a wasu sassa na duniyar nan! Allah buwayi gagara misali, shi ya sa da ya tashi bayar da labarin ASHABUL-KAHFI a cikin al-qur'ani mai tsarki, sai ya bayar da labarin har da karen da yake tare da su, wato kare ya lizimci mutanan kirki! 

Shin waye kare? Wani bincike ya nuna cewar, kare ya rayu a cikin wannan duniyar kusan fiye da shekaru 100,000 da suka shude, sannan  asalinsa, tsatso ne na dangin "wolf" wata dabba da ake samu a Arewacin Amerika da Turai da Kuma Asia, ita wannan dabba ta yi kama da Kare ta fuska, amma ta sauran sassan jiki sun sha bamban da kare, kuma amfi samun sa a waje mai sanyi da dusar kankara. Haka kuma, wani binciken ya nunar da cewr akwai sama da karnuka Miliyan 400 da suke watangaririya a duniya. Allah masani! Amma dai mun san cewa Allah ya halicci dukkan "DABBATIL ARD" bisa kaddarawarSa subhanahu wata'ala, shi ne ya halicci Mutum, da Aljani da kwado da gafiya da Barewa da Kunkuru da Matsaatstsaku da Rakumi da dukkan sauran ababen Halitta bisa Kaddarawarsa Alkhaliqu, tsarki ya tabbata a gareshi.

Kare shi ne kadai yake da dogon tarihin sabo da yiwa 'yan Adam hidima tun kusan fiye da shekaru 33,000 da suka shude a cewar wasu masana, musamman ta fannin da ya shafi kiwo, farauta, jan-kaya a cikin dusarkankara, da kuma taimkawa jami'an tsaro wajen gano wasu baoyayyun abubuwa da suka gagri dan-adam ganowa. Kare yana da rikon amana ainun, duk irin bala'i da masifa ta kura, da kuma irin yadda Allah ya sanyawa kare tsoron Kura, yakan mutu wajen kare dabbobin da yake rakiya a duk lokacin da kyarkyeci ya kawo musu farmaki ko barazana. Kare ne kadai dabbar da ake iya bashi kiwon wata dabba 'yar uwata! Subhanallah, kaji al'amarin ubangiji. Allah cikin hukuntawarsa ya sanyawa kare fahimta mai yawa da kuma lura da ganewa.

Allah ya halicci kare daban da sauran dabbobi. Domin yadda kare yake kallon duniya ba haka sauran dabbobi suke ganinta ba, sinadaran da suke cikin Idon kare suna ganin fari ne da baki kawai, a tarihin rayuwarsa bai taba ganin wani launi sabanin fari da baki ba, a bisa yadda Allah ya yi masa halittarsa. Kare yana daga cikin dabbar da bai damu da duniya ba, babu ruwansa, shi yasa a koda yaushe yafi son zama waje mai sanyi mai danshi mai ni'ima, watakila kamar yadda muka fada a baya tsatsonsa danginsu wolf suna rayuwa ne a waje mai sanyi watakila wannan ta sanya kare ke son sanyi da danshi.

Kamar yadda kare ya dauki tsahon lokaci tare da mutane, wannan ta sanya yake samun cigaba gwargwadon yadda mutane ke samun cigaba. Domin yanzu bincike ya nuna kare yana iya yin tarayya da mutane wajen yin wasu ayyuka da dama. Misali ba sau daya ba, ba sau biyu ba ansha cewa kare ya kubutar da wani yaro ko yarinya daga halaka, ko kare ya halaka garin kokarin kubutar da dan-adam daga halaka. Bayan ayyuka na tsaro da bincike da Kare yake taya dan-adam, kare na iya yin wasu ayyuakn da dama kamar bude kofa da rufewa, kunna hasken lantarki da kashewa, kallon talabijin, sannan kuma, kwanakin baya muka ji cewar an fara koyawa kare tukin mota a Amerika. Ba shakka a kasashen turai har aiken kare suke yi, kuma idan bai gane ba ya yi tambaya a yi masa kwatance. Kare baya magana amma yana jin magana kuma yana fahimta, gwargwadon tarbiyyar da ya samu da kuma irin yanayin da ya taso a cikinsa.

Idan muka dauki batun "SABO" byanai sun tabbatar da cewar Kare ya samu shakuwa da dan-adam sosai, ta yadda baya iya rabuwa da mutanan da ya saba da su. Wata rana a cikin shirin taba kidi na BBCHausa suka fadi cewar wani kare da ubangidansa ya rasu, sai da karen yazo ya tare a gindin kabarin da aka binne ubangidan nasa na wasu tsahon lokuta, yaje ya yi farautar abinda zaici sannan ya dawo wajen ya kwanta. Akwai nau'ka na kare sama da kala 400 a cewar wani bincike. Hakika akwai abubuwan ban mamaki a tattare da rayuwar kare. 

Yasir Ramadan Gwale 
21-11-2013

Wednesday, November 20, 2013

Daga Birnin Washington GUndumar Kwalambiya



DAGA BIRNIN WASHINGTON GUNDUMAR KWALAMBIYA

A ranar 22 ga watan Nuwamban shekarar 1964 shugaban kasar Amurka na wancan lokacin John F Kennedy ya shirya tsaf inda ya kama hanyar garin DALLAS babban birnin jihar TEXAS dan gudanar da kasaitaccen gangamin yakin neman zabensa a karo na biyu. A daidai lokacin da Shugaban Kennedy ya fito cikin fara'a da annashuwa dan wannan gagarumin gangami da aka jima ana yiwa tanadi, wasu harsasai guda uku suka kawo karshen rayuwarsa a duniya, a yammacin wannan rana. Ya abin ya faru ne?

Clint Hill ta ce, ina tsaye a daidai lokacin da budaddiyar motar da aka yiwa Shugaba Kennedy tanadi dan ya shiga ya zaga a tsakiyar Dandalin Dealey Plaza dake birnin Dallas. Muna tsaye muna jira, Can sai na hango zungurareriyar motar da take dauke da shugaban ta dumfaro filin da aka tanadar masa budaddiyar motar da zai hau, karasowarsa ke da wuya, kusa da inda nake tsaye, babu zato babu tsammani sai naji wata karar fashewa mai karfin gaske, na firgita matuka a daidai wannan lokacin, ban san me yake faruwa ba, ga hayaki ya turnuke, babu abinda kake iya ji sai ihun da jama'a suke dan gudun neman tsira da rayukansu. Da na hanga kusa da budaddiyar motar nan, sai na hangi Shugaba Kennedy kwance ya yana jan jiki ta bangaren gefen jikinsa na hagu, makogaronsa na furzar da jini, hankalina ya kara tashi da abin da na gani, ban yi wata-wata ba, na yunkura da sauri dan na matsa kusa da inda shugaba yake domin na kai masa dauki, sai naji wata kara fau-fau sau biyu, na sake kwantawa, can banyi kasa a guiwa ba, na kuma jan jiki dan na matsa kusa da inda yake na kai masa agaji sai na kara jin wata kara FAU! Ai ko da na kalli inda Shugaba Kennedy yake sai naga kwakwalwarsa a bude jini na ta kwarara, ina matsawa inda yake sai na sake jin wata mummunar kara da fashewa a dab da budaddiyar motar da ke kusa da mu. Inji Clint Hill tsohuwar jami'ar leken asiri take shaidawa masu bincike abin da ta gani a wannan rana.

Shugaba Kennedy mutum ne mai saukin kai, ba shida girman kai. A duk sanda ya fito yakan shiga cikin mutane ba tare da shayin wani abu ba yana mika musu hannu ana sowwa da murna. Haka kuma, a sau da dama Shugaba Kennedy mutum ne da baya yarda jami'an tsaronsa su dinga sanya masa labule da jama'a a duk sanda ya fito bainar jama'a.

Kisan da aka yiwa Shugaba Kennedy, hakika ya girgiza Amurkawa, hankalin mutane da dama ya tashi. A halin yanzu motar da aka budewa Shugaba Kennedy wuta tana gidan adana kayan tarihi na Henry Ford museum dake birnin Dearborn a jihar Michigan.

Wasu muhimman tambayoyi su ne: Wanene ya kashe shi?
Kuma menene dalilin kisan nasa? Me ya biyo bayan kisan ta fuskar hukunci?

20-11-2013

Monday, November 18, 2013

Shin Jega Ne Matsalar Zaben Najeriya?

SHIN JEGA NE MATSALAR ZABEN NAJERIYA?

Zaben gwamnan jihar Anambra da aka gudanar ranar 16 ga watan nuwamba, kusan shi ne ya bankada asirin hukumar zabe ta kasa karkashin jagorancin kwararren malamin jami’ah masanin kuma mutafannini a harkar siyasa Farfesa Attahiru Muhammad Jega, dan gane da kurari da karajin da ya dinga yi a baya cewa ya nazarci dukkan kurakuran da suka fuskanta a zaben 2011 da ya gabata, ya kuma sha cin alwashin cewar sai ya tsaya kai da fata wajen ganin an aiwatar da sahihi kuma tsarkakken zabe daga dukkan nau’in magudi a babban zaben kasa na 2015 da ake ta tsumayin lokacin. Sai dai Hausawa sunce “juma’ar da zatai kyau akan fara gane ta ne tun daga asubahin ranar laraba” sai gashi abin mamaki da ta’ajibi laraba ta yi har rana ta fadi ana shirin wayar gari Al-hamis babu wasu alamu da suke nuna cewar juma’ar da zata zo gaba kyakykyawa ce da jama’a zasui murna da farin ciki da ita.

Wannan zaben na Anambra da aka gudanar mai cike da kace-na-ce da tababa, shi ne zaben da ‘yan Najeriya suka sanyawa ido a matsayin wani ma’auni ko zakaran gwajin dafi akan zaben da zai gudana na kasa a shekarar 2015. Sai gashi duniya ta shaida tsiraicin hukumar zaben da Jega ya dinga shan alwashi akan zasu aiwatar da sahihin zabe. Almundahanar da aka tafka a wannan zaben ba wai ta tsaya akan al’adar nan ta ‘yan siyasa ta sayan kuri’u da rarraba kayan masarufi ga masu yin zabe ba, abin har da jami’an hukumar zabe aka samu da hannu dumu-dumu wajen yin kaci-baka-ci-ba baka-ci-ba-kaci, aka raunana zaben, aka hana wasu yin zabe, aka sossoke wasu kuri’u. Na san da cewa da daman ‘yan Najeriya abin da ya faru a Anambra dangane da ‘yan siyasa bai basu mamaki ba, dan dama mai hali baya fasa halinsa, illa kawai abin mamaki shi ne, ashe hukumar zabe shararata ta dinga yi dangane da wannan zabe.

Ba shakka, ya zuwa yanzu mutane da dama sun sallama da samun sahihin zaben da aka tsammata a 2015 wanda Jegan ya sha alwashin aiwatarwa. Dukkan wani kyautatawa hukumar zabe zato da aka yi akan zaben 2015 a yanzu dai hukumar zaben ta zubewa ‘yan Najeriya kasa warwas idan banda ‘yan Fidifi bangaren shugaban kasa. Babu wani kwarin guiwa da muke da shi akan hukumar zabe dangane da samun sahihin zabe da zamu iya aminta da sakamakonsa. Abinda ya faru a baya watakila a zaben 2015 ya ninka ninkim-ba-ninkim na almundahana da cuwa-cuwa da satar akwati da hadin baki tsakanin jami’an tsaro da ma’aikatan hukumar zabe da baragurbin ‘yan siyasa masu san cin zabe ta kowace irin hanya.

To amma abin tambaya anan shi ne, shin Farfesa Attahiru Jega shi ne matsalar zaben Najeriya? Ba shakka Jega shi ne shugaban hukumar zabe ta kasa, shi ne yake da dukkan wani alhaki na ganin ya tsaya kai da fata wajen ganin anyi gaskiya, anyi adalci a matsayinsa na shugaban hukumar zabe. Sauran jama’a masu zabe su kuma a nasu bangaren su tabbata sunyi zaben gaskiya wanda bai sabawa doka da ka’ida ba.

Tuni har wasu sun fara yin kira akan Farfesa Attahiru Jega ya kama gabansa ya san nayi. A ganina yin murabus din Jega ba shi ne mafita ba dangane da samun sahihin zabe, ba shakka Shugaban hukumar zabe yana da dama mai girman gaske wajen ganin anyi zaben gaskiya, amma yana da kyau idan anbugi jaki a bugi taiki, domin su kansu jama’a da dama ba gaskiya suke da itaba, dole mu hada karfi da karfe wajen ganin ansamu zaben gaskiya. Yana da kyau mu sani ko Jega ya sauka, Shugaban kasa Me-Malafa shi ne dai zai sake nada sabon shugaban hukumar zabe, kuma ba shakka, shugaban rashin gaskiyarsa da rashin tsoron Allahnsa sun bayyana karara kamar wata darn goma sha hudu, dan haka ba zai taba nada wani mutum mai gaskiya da zai jagoranci hukumar zabe dan ya aiwatar da sahihin zabe ba.

A ganina gara Jega ya cigaba da zama a matsayin shugaban hukumar zabe har zuwa karshen wa’adinsa, tunda mun riga mun sanshi, munga irin kamun ludayinsa. Muna kuma da yakinin cewar yayi Imani da Allah, ya yi Imani da Wutar Jahannama ya yi imani da Al-Jannah, ya kuma san cewa Marasa gaskiya maciya amana masu jefa rayuwar al’umma cikin mummuna hali da garari ba zasu hada hanya da al-jannah ba. Wallahi Jega idan yayi gaskiya yasan makomarsa kyakykyawa ce a ranar gobe kiyama, idan kuma yayi rashin gaskiyar da muke zarginsa ba shakka yasan makoma ta munana ga mutanan da suka aikata aiki irin na marasa gaskiya makiya gaskiya, makiya cigaban kasa.

Ko shakka babu, bamu yanke tsammani daga wajen Allah ba dan samun Shugabanni na gari masu gaskiya da tsoron Allah wadan da zasu ji-kanmu su fitar da mu daga cikin halin fatara da talauci da kuncin rayuwa, da samar mana da dukkanin abubuwan bukata, da kare mana martabarmu da rayukanmu da dukiyoyinmu. Allah muke roko Al-Azizu ya wargaza dukkan wani shiri da nufi na Azzalumai ko su waye, Ya Allah kasansu ka san abinda suke kullawa, Allah ka yi mana maganinsu. Ya Allah! Bad an halinmu ba, ka arzutamu da samun shugabanni na gari Adalai.

Yasir Ramadan Gwale

18-11-2013

ZABEN 2015: ANYA ZA'A IYA KAYAR DA GOODLOCK KUWA?


ZABEN 2015: ANYA ZA'A IYA KAYAR DA GOODLOCK KUWA?

Abinda ya faru jiya a jihar Anambra ya kara tabbatar mana da cewar tun daga zaben 2011 har zuwa yau babu wani abu da ya canza dangane da harkar zabe a Najeriya. Zaben Anambra duk da ba'a fadi sakamako ba, amma irin almundahanar da ta wakana ta nuna cewa hukumar zabe babu wani kwarin guiwa akanta, dangane da aiwatar da sahihin zabe. Tambayar da na yiwa kaina, anya hukumar zabe karkashin Attahiru Jega zata iya shirya tsarkakkaken zaben da zamu iya yarda da sakamakonsa ko da kuwa ba wanda muke so ba ne ya yi Nasara? Allah ya kiyaye.

A kasar Kenya, babu abinda ya damu Moi Kibaki da duk mutanan da suka rasa rayukansu domin duk talakawa ne suka kashe talakawa. Ya murda zabe yayi abinda yaga dama, ya kammala wa'adinsa, kuma ya kama gabansa babu ko kara da aka daga masa da sunan dukkan irin balahirar da aka tafka a zaben da ya mayar da Kebaki kan kujerar Mulkin wa'adinsa na biyu. Sai abin ma ya zama wasan kwaikwayo, wasu daban ake zargi da tashin hankalin da ya faru! Kura ta sha kashi shi kuwa gardi ya cika lalitarsa.

A kasar Senegal mun gani duk da irin dan banzan taurin kai da san dawwama a Mulki na shugaba Abdullahi Wade, amma da aka yi zabe ya sha kaye ya hakura da kayen da ya sha, kuma ya mika mulki ga zabin jama'a, ba tare da anyi asarar rayukan talakawa ba, kamar yadda aka yi a Kenya. Watakila saboda yana da hasken Imani na Musulunci a zuciyarsa ne. Allah masani.

A babban zaben kasa na 2015, ko dai shugaba Goodluck Jonathan yabi irin hanyar da Kebaki yabi a Kenya ya kashe kunnensa, ayi ta kashe-kashe da kone-kone tundaga Gonin-Gora har Jibiya, tundaga Sokoto har Maiduri babu abinda zai sha masa kai. Ko kuma ya nuna dattako irin na shugaba Wade idan ya sha kaye ya hakura ya mika mulki ga zabin jama'a Alabashshi tarihi ya rubuta karfin hali da juriyar da ya nuna na karbar kaddara. Wanda ba shakka abu ne mai kamar wuya haka siddan wannan bakin arnen ya yarda ya sha kaye, balle da wuya har akai ga fagen shan kayen.

Babban abin tambaya ta shi ne, shin me ye zai biyo bayan sakamakon zaben kasa na 2015? Anya kuwa jam'iyyar APC da muka saka a gaba ta shirya da gaske dan kwace goriba a hannun-kuturu? Ba shakka talakawa suna cikin garari kwarai da gaske. Ina ji a jikina cewa PDP na iya samun halattaciyar kuri'ah a kafatanin jihohin Najeriya, tunda suna da kudin sayan kuri'u, ba shakka kuma za'a sayar musu. Amma dai al'amarin akwai ban tsoro kwarai da gaske.

Wata muhimmiyar tambaya da nake yiwa kaina, ita ce, meye makomar Musulmi a cikin gwamnatin Jonathan idan aka ce shi ne ya ci zabe? nayi Imani shugaban kasa Goodluck mutumne mara tsoron Allah. Meye makomar tashin hankalin da muke fama da shi a Arewa musamman a jihar Borno da Yobe? Nasan da cewa, duk tsiyar shugaban kasa da takadarancinsa ba zai haura shekara ta 2019 ba, to amma me zai faru da mu kafin wannan lokacin? Allah shi ne masani.

Yasir Ramadan Gwale 
      17-11-2013

AREWA: A GANI NA . . .

AREWA: A GANI NA . . .

Batun halin da Arewa ta ke ciki na zubewar mutunci da kima da haiba da kamala da koma baya ta fannin tattalin arziki da sukurkucewar Ilimi da lalacewar makarantu da kiwon lafiyar da asibitai suka zama tamkar makabartu da al’amuran tsaro da suka jagwalgwale suka hana kowa walwala da jin dadi, kusa wadannan da ma wasu sun damu duk wani dan AREWA mai kishi babba ne ko karami, mace ce ko Namiji. Yau a Arewa babu wani wanda zaka titsiye ka tambayeshi halin da ake ciki ya yi maka hamdala da godiya da wannan hali da muke ciki, sai dai fa idan tantagaryar makiyin Arewa ne makiyin Najeriya wanda baya son cigaban Arewa da Najeriya. Halin da muke cikin ya wuce duk yadda ake zato, domin wani abin ma idan mutum yaji sai yaji kamar ba gaskiya bane, ba wai kawai lalacewa Arewa ta yi ba, a’a komawa baya ta ke a sukwane, Kamar Misalin motace ka baiwa dan koyo kuma ya sanya giyar reverse yana gudun tsiya, shakka babu dole ya yi barna, ba wai motar kadai zai mammokada ya lallauya tayoyin ba har da duk abinda ya samu akan hanya sai ya bangajeshi mai gyaruwa ya gyaru wanda ya mutu ya mutu kenan; to kamar misalin irin haka Arewa take a yanzu, a halin da muke ciki.

Matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi ta addabi samarinmu maza da mata, Ilimin makarantun hukuma ya tabarbare makarantun gwamnati sun zama garken jahilai, malaman babu ilimi, daliban babu ilimi gwamnatocin kananan hukumomi da na jihohi da sauran al’umma da ake kira “community” kowa ya kame hannunsa daga lalacewar ilimi anyi ko in’kula, kowa ya gwammace idan zai iya ya dauki dansa ya kaishi makarantar kudi, wanda kuma bashi da karfi alal-larurati ‘ya ‘yansa suke karatu a makarantun gwamnati ba dan ransa yana so ba, sai dan bashi da yadda zai yi. Irin wannan mawuyacin halin hannu baka hannu kwarya, ya sanya da dama dagacikinmu suka fara yanke tsammani daga Ubangiji, wasu suka bazama neman yaki halal yaki haram, Mutane burinsu su tara dukiya babu ruwansu da tsarkinta.

Yanzu a Arewa yaro da babba, mace da Namiji, almajiri da wanda ba al’majiri ba, mai gata da mara gata, mai mulki da wanda ake mulka; Kusan kowa neman damar dan uwansa yake, ta ina zai samu dama ya kwashe kafufuwan duk wanda Allah ya dorawa kaddarar fitar rabo. Cuta da cutarwa ta zama ruwan dare gama duniya, babu malamai babu jahili, masu hankali da marasa hankali kowa neman hanyar cuta yake, yan kasuwa da masu sari, leburori da iyayan gidansu; daman ma’aikatan gwamnati ya zamar musu tamkar halaliya yin almundahana da kayan hukuma, a sace duk abinda zai iya satuwa, tundaga masu gadi har oga kwata-kwata duk wanda ya samu abin dauka indai na hukuma ne, to gaban kansa yake ya dauka, tamkar wanda ubansa ya mutu ya bar masa gado shi kadai, a sace man jannareto, a sace fanka a saci tabarma da darduma, wani abinma bai kai a sace shi ba, amma saboda tsabar mutuwar zuciya, sai ma’aikata su dinga satar abinda ko kadan ba zai amfanesu ba, illa kawai wani tunani da ya dade da yin tsiro a zukatan al’umma na cewa “raba arne da makami ibada ne” dan haka ake ganin kayan hukuma kamar ganima.

Wannan yanayin shi ne wani irin mawuyacin lokaci da Arewa bata taba mafarkin samun kanta a cikin irinsa ba. Magabatan shugabanninmu sun barmana kyakkyawan abin gado, sun gina harsashin samun ingantacciyar rayuwar wadan da zasu zo baya, sun samar mana da Gidan jaridar NNN da gidan Radio Najeriya Kaduna, da kamfanonin murza auduga na Arewa da Babban Bankin Arewa da makarantun tundaga kwalejoji da jami’o’I da makarantun koyon sana’a, da makarantun horas da malamai da sauransu da dama, amma basu yi sa’ar samun hannu na gari da zai iya alkinta su ba, wannan duk wanda ya san Arewa ya san halin da ta ke ciki zai iya bayar da shaida akan haka. To amma hakikanin gaskiya tafiya tayi tafiya, tura ta kai bango, lokaci ya yi da za’a zauna zama na gaskiya a kalli halin da muke ciki dan dawo da martabarmu da aka yi mana shaida da ita tun a baya.

Haka kuma, lokaci ya yi da zamu ja layi akan dukkan wasu laifuka da muke ta zargin kawukanmu da aikatawa, tunda halin da muke ciki ya shafi kowa da kowa, babu wanda yake walwal cikin jin dadi da kwanciyar hankali, kusakurai an riga anyisu manya da kanana, dan haka, abinda ya kamata mu maida hnaklai shi ne kokarin nemo mafita da bakin zaren halin da muke ciki. Shugabannin baya da kuma wadan da suka nannada kansu Shugabancin Arewa a yanzu duk sunyi abinda zasu iya, wadan da suka tafka ta’adi da wadan da suka yi abin kirki duk sunyi, kuma anga abin da kowa ya yi, Allah ya sakawa kowa da gwargwadon abin day a aikata, idan khairan khairn, idan sharran sharran.

Wata rana Shehu Jaha ya aiki diyarsa ta debo masa ruwa a tulu, sai ya yi mata kashedin kada ta sake ta fasa masa tulu, idan kuwa ta fasa to zasu gauraya, har ta kama hanya ta tafi sai Shehu ya kirata ya tsinko tsumagiya ya shashshauda mata, wani abokinsa ya ce haba Shehu yaya ka gargadeta kar ta fasa, bayan kuma bata fasa ba ka doketa. Sai Sheshu ya kada baki yace, babu amfanin na doketa a lokacin da ta riga ta fasa tulu, domin dukan ba zai sanya tulu ya dawo ba. Kamar misalin haka ne na irin halin da muke ciki, yawan zargin junanmu da laifin halin da muke ciki babu abinda zai kara, illa kara wagegen gibi a tsakaninmu, tunda matsaloli dai ana cikinsu tsamo-tsamo, batun ko laifin su wane ne ko ba laifin su wane bane, duk ya kamata mu wuce wajen, batun da ya kamata mu maida hankali shi ne ta yaya zamu fito daga cikin wannan halin da muke ciki shi ne abinda dukkanmu ya kamata mu maida hankali akai.

Dukkanmu dole mu ji tsoron Allah a cikin al’amuranmu, mu sanya gaskiya da amana a cikin mu’amalolinmu, shugabanni su zama adalai a ajiye komai a inda ya dace, a baiwa kowanne mai hakki hakkinsa, babu wasu mutane daga Ingila ko Faransa ko Amerika da za su zo su fitar dam u daga cikin halin da muke ciki, mune muka san kanmu, muka san halin da muke ciki, muka san irin azaba da radadin da muka shiga ciki, ya zama tilar mu hada karfi da karfe wajen fito da sahihan hanyoyi da zasu amfani ‘yan bayanmu masu zuwa nan gaba. Mu shata layi kamar yadda na fada, ko da bamu yafe irin satar da ‘yan uwanmu suka dibga ba, to mu dakatar da abin haka, kudin hukuma ba na uban kowa bane, na dukkanmu ne, idan mun alkinta dukiyarmu kanmu muka alknta, idan mun barnatar kanmu da jikokinmu muka yiwa illa.

Ya zama dole da Masu mulkinmu na Siyasa wadan da hakkin jagorancinmu yake a hannunsu, da shugabanni masu rike da sarautu, da malamai da kungiyoyi mu samar da wata Hadaka da zata fitar da mu daga cikin halin da muke ciki. Kamar yadda aka samu hadewar jam’iyyu dan kawai ga gaci da samun nasara, muma dole sai mun hade kanmu mun hade kungiyoyinmu, sannan mu samu nasarar fita daga cikin wannan mawuyacin halin da muke ciki. Akasin haka, babu abinda zai yi mana illa kara jefa mu cikin bakin ciki da damuwa da ba za su iya yi mana maganin halin da muke ciki ba, idan banda kara nesanta mud a juna. Dole mu dawo da ‘yan uwantaka tsakaninmu da kaunar juna, da taimakekeniya, mu cire kyashi, mu daina hassada, mu yiwa kanmu tarbiyyar hakuri da halin ‘yan uwanmu, mu kuma yi hakuri da halin talauci da kuma baiwa mawadatanmu uzuri. Ya Allah ka karkato da hankulanmu gaba daya mu fahimci juna dan ciyar da Arewa da Addininmu gaba, Allah ka taimakemu ba dan halinmu ba, ba dan munanan ayyukan da wasu daga cikinmu suka aikata ba. Allah ka taimakemu ka sa wannan shi ne lokacin da zamu yi ban-kwana da dukkan irin sarkakiyar da muke ciki da wahalar rayuwa. Allah ya taimaki Arewa da Najeriya baki daya.

Yasir Ramadan Gwale 26-10-2-13

Ojukwu Da Rawar Da Ya Taka A Juyin Mulkin Janairun 1966


OJUKWU DA RAWAR DA YA TAKA A JUYIN MULKIN 1966!!! (4)

A shekarun baya irin wancan ra’ayi na bayar da kariya ga Ojukwu da mutane irin sa na fitowa ne daga kudu. Ko a 1987 a wani littafi nasa mai suna “Nzeogwu” Chif Obasanjo ya bayyana Nzeogwu da mutumin kirki, mai saukin kai, mai hangen nesa da tausayi. To a yau gashi ‘yan Arewa sun fara, Sai muce Allah ya sauwaka. Don haka dalilan da zasu sa wani koyi da marigayi Ojukwu, koda kuwa ibo ne, marasa tushe ne. Balle kuma ace dan Arewa da yakai matsayin gwamnan jiha kuma jagoran wamnonin jihohi 19 da a baya suke karkashin kulawar Sardauna.

A dan haka, a bias bayanan da suka gabata a baya, zamu fahimci cewar Ojukwu wani irin mugun mutum ne maketaci mai son tashin hankali da rashin san zaman lafiya, kuma Ojukwu zaka iya kwatantashi da wani irin mugun makiyin Arewa na bugawa a Jarida, duk da irin waccan mugunta da kiyayya da keta ta Ojukwu da bata bar ‘yan kabilar Ibo ba, to wai har wani mutimin Arewa da yake takama da cewa shi ne magajin Sardauna a yanzu domin shi ne yake jagorancin Gwamnonin Arewar su Sardauna. Anya kuwa wannan mutumin ba Inyamuri bane da rigar Hausawa? Ko kuma irin inyamuran nan ne da aka Haifa a Arewa kamar yadda shi kansa Ojukwu din a jihar Neja inda Babangida Aliyu yake Gwamna aka haifar, Lallai ina mai cike da shakkun cewar da kyar idan Babban Hadimin jihar Neja kamar yadda ya kira kansa shi ma ba Inyamuri bane haihuwar Arewa. Amma dai komai daren dadewa tarihi baya karya.

Akwai da yawa daga cikin Inyamurai da suke da waccan muguwar Aqidah ta kakkabe mutanan Arewa daga harkar Gwamnati kamar yadda Ironsi da Ojukwu suka nuna aiwatarwa, domin sojojin da suka kasha su Balewa da Sardauna da Zakariya Maimalari das u Akintola ai duk said a Ironsi ya yi musu Karin girma, sannan ya zabge sojojin Musulmi ‘yan Arewa da kuma Musulmi daga bangaren Yamma na Yarabawa, sannan ya yi Karin girma ga mutum 25 kamar yadda muka bayyana a baya amma mutum 3 ne kcal Musulmi ‘yan Arewa a yayin da mutum 1 ne kacal daga yankin Yamma na Yarbawa.

To tarihi fa shi yake maimaita kansa. Yanzu irin waccan muguwar Aqida ta su Ojukwu da Ironsi ita shugaban sojojin Najeriya na yanzu Laftanar Kanar Ihejirika yake aiwatarwa a kaikaice. Inda idan bamu manta ba, a kwanakin baya ya zabge manya-manya sojojin kasarnan Musulmi gaba dayansu Hausawa da Yarabawa kuma, yam aye gurbinsu da Ibo Inyamurai gabaki daya babu kunya babu tsoron Allah, Shugaban kasa kuma yana ji yana gani ya kasha kunnensa domin dadawa Inyamurai kamar yadda a kullum yake nuna cewar shi fan a sune.

Haka kuma, a irin yadda ake kwashewa ‘yan Arewa Musulmi kafafu a dibar sopjoji a makarantar horon soji ta NDA dake Kaduna zaka kara fuskantar akwai wasu boyayyun lamura a harkar tafiyar da al’amarin soja a kasarnan, domin a mafiya yawancin jihohin da suke da Kiristoci sai da aka fifita su akan Musulmi a wajen daukar adadi,\. Duk wannan fa yana faruwa bayan irin yadda ake yi mana kisan Mummuke da sunan farautar ‘yan Ta’adda a yankin Arewa maso gabas, wanda rahotanni sun nuna cewar galibin sojojin da aka jibge a wannan yanki Inyamurai ne ‘yan kabilar Ibo, suke ta karkashe mana mutane babu ji babu gani da sunan ta’addanci, wanda ko a baya-bayannan sai asibitin koyarwa na Jami’ar Maiduguri ya bayar da sanarwar cewar sojojin rundunar JTF sun kawo gawarwakin mutane sama da 3000 asibitin a cikin kasa da shekara daya! Lallai akwai lauje a cikin kunshin rundunar sojojin Najeriya.

Lallai ya zama dole Mu ‘yan Arewa mu yi karatun baya mu tuna abubuwan da suka faru a baya, sannan mu kalli abubuwan da suke faruwa a yanzu da wadanda zasu iya faruwa a nan gaba, dan tunanin Makomarmu, idan kuwa bah aka ba, muna ji muna gani Ojukwu zai dawo da wata rigar daban ya kashe kashewa iya san ransa, wadan da suka yi saura kuma ya tarwatsa zuwa kasashen Nijar da Chadi da Kamaru kamar yadda a bayyane take cewar da yawan ‘yan Jihar Borno suna samun mafaka a wadannan makotan kasashe.

Idan mun ki ji shakka babu ba zamu ki gani ba.

Yasir Ramadan Gwale da Mustapha Ibrahim suka yi hidimar kawo wannan tarihi.