Friday, April 6, 2012

Hukumar Hizba Ta Jihar Kano Kada Wankin Hula Ya Kaiku Dare



Umarni da kyakkyawa da Hani ga mummuna, kusan shi ne jigo ko kashin bayana aikin Hukumar Hizaba ta jihar kano. Kamar yadda muka sani, wannan jigo na aikin Hizba, kusan Hadisi ne na manzo salallahu alaihi wasallam, aka fassarashi, kuma ya kasance hadafin hukumar tun lokacin da aka samu matasa masu kishin addini ‘yan sa kai suka assasata, da nufin motsa zukatan masu kishin addini, da kuma neman gwamnati ta aiwatar da shari’ar Musulunci a jihar kano a shekara ta 2000 kamar yadda akayi a zamfara; aikin hukumar Hizba kamar yadda muka sani ba sabon abu bane a musulinci.

A wancan lokaci, matasan da suke aikin Hizba a jihar Kano, suna yi ne na sa kai, wato babu wanda ake biya ko anini, hasalima sune suke yin karo-karo domin samar da kudin gudanarwa a unguwanni da kananan Hukumomi, anga mutane irinsu marigayi Sheikh Jafar Mahmoud Adam sanye da kayan Hizba a wajen wa’azozin neman kafa shari’a a wurare irinsu Majalasin Triumph da Masallacin Umar Bin Khattab da sauran gurare a fadin Jihar kano.

Bayan duk abin da ya faru ya faru na gwagwarmayar tabbatar da shari’ah a kano, kuma akaci nasarar kafata, gwamnatin Injiniya Rabiu Musa kwankwaso a wancan lokacin, batayi nisan kwana ba, wannan ce ta bada kofa ga gwamnatin Mallam Ibrahim Shekarau, da daukin jama’a na ganin aiwatar da sharia a kano. Da mallam Shekarau ya zo ya nemi majalisar dokoki ta jihar kano tayi dokar da zata kai ga kafa Hizba a Hukumance ta yadda babu wani da zai iya yi mata barazana ko katsalandan, gwamnatin tayi kokari wajen gyara tare da tsarkake Hukumar hizba tare kuma da mayar da ita tayi dai-dai da zamani, wannan ta sanya akayiwa dakaru kusan 9000 a mazabu da kananan hukumomi da kuma jiha rejista tare da sama musu albashi na kusan Naira 15000 a kowane wata, tare da babban kwamanda guda daya, a mtsayin jagora. Kusan aikin Hizba yana tafiya kafada da kafada ne da Hukumar Shari’ah ta Jihar Kano. Kusan duka aikinsu mai taimakon sashe ne, wajen ganin al’amuran shari’a sun inganta, tare kuma da dawo da tsoron Allah a zukatan jama’a. Madallah da wannan aiki na Hukumar Hizba mai dumbin lada.

Yanzu kamar yadda kowa ya sani, babban aikin da Hukumar Hizba ta sanya a gaba shi ne na aurar da zawarawa kusan 1000 a jihar kano. Mallam Muhammad Aminu Ibrahim Daurawa, shi ne babban kwamandan Hizba na jihar kano, tare kuma da manyan mataimakansa guda uku da kuma takwararsa ta bangaren mata da sauran masu taimaka musu, da kuma kwamandoji na kananan hukumomi 44 na jihar Kano. A wani lokaci a can baya a lokacin da Gwamnan jihar Gombe Muhammad Danjuma Goje ya gayyaci Mallam Aminu Daurawa zuwa buda baki da Azumi a gidan gwamnati, ya yi wasu kalamai na gugar zana ga ita hukumar Hizba ta jihar kano, sannan kuma a wasu wa’azozi nasa ya zargi hukumar da gazawa wajen iya tafiyar da aikinsu.

Hukumar Hizba tayi wannan tanadi ne, na rage adadi na yawan zawarawa dake lungu da sako na jihar Kano. Hukumar tayi tanadi, na baiwa duk wanda zaiyi wannan aure sadaki da kuma kayan daki da wasu kayayyaki na koya sana’o’i ga matan da za’a aurar, Kamar yadda aka ce hukumar, tana kokarin tantance zawarawa mata da kuma maza wadanda za’a daura wannan aure da su. Kusan rahotanni sun nuna cewa da yawan matan da za’a aurar basu san wanda za’a aura musuba; kamar yadda wakilin BBC na jihar kano ya zanta da wasu da suke jiran tantancewa ya fada. Tambaya ga hukumar Hizba, shin tayaya ake tsammanin dorewar auren da mata da mijin basu gama fahimtar juna ba? Ganin cewa ba ‘yan mata bane balle a ari bakinsu a ci masu albasa, sannan kuma, shin idan andaura wannan aure wane tabbaci suke da shi na cewa auren bazai sake mutuwa ba? Menene matsayin mutumin da hukumar ta yiwa auren kuma daga baya ya saki matar? Ina matsayin kudadan da aka kashe domin hidimar wannan aure? Misali ka dauka cewa duk wanda zaiyi auren hukumar zata taimaka masa da 10,000 a matsayin sadaki, kaga kenan zata kashe kusan Miliyan 10, a sadaki kawai, sannan sukuma bangaren matan, da kayan daki da na sana’a ka dauka cewa za’a kashewa kowacce 50,000, kaza za’a kashe akalla miliyan 50, sannan kuma da kudin da hukumar zata kashe wajen aiwatar da wannan aure.

Duk wadan nan kudade zasu fito ne daga asusun gwamnatin jihar kano, wanda ya nuna cewa lallai kudin al’umma ne! Shawarata anan ga hukumar Hizba shi ne da wadanan kudade da za’a kashe, da mutum 200 farko aka inganta aurensu tare da baiwa mazajen jari ko kayan sana’a wadan da zasu iya daukan dawainiyar wannan aure, domin idan hukumar Hizba batayi hankali ba garin neman gira sai ta rasa idanu, kamar yadda sukace shi mijin za’a taimaka masa da sadaki, ita kuma matar za’a taimaka mata da kayan sana’a, shin me wannan yake nunawa? Ita matar ita zata rike kanta kenan? Zata dauki dawainiyar kanta da mijinta kenan? Idan har banyi kuskureba haka batun yake, cewa matan za’a taimakawa da kayan sana’o’i tabbas sunan wannan aure sakakke domin babu yadda aure zaiyi karko a irin wannan yanayi na mace ita ke da gida. Lallai hukumar hizba ya kamata tayi duba na tsanaki a kan wannan batu.

Sannan, wannan batu na auren da hukumar zatayi, idan basubi a hankali ba shi ne zai dauke hankalin hukumar kusan tsawon wa’adinsu. Domin tabbas su shirya jin koke da korafe-korafe ga wadan da aka aurar, domin a irin yanayi na mallam Bahaushe, duk abinda ya samu a bagas kamar yadda turawa ke cewa at aplata gold bai cika bashi muhimmanci da kimar da ta dace da shi ba, kaga kenan, angama da wannan kaso na mutu 200 ana shirin na wasu 200, sannan ga na farko sun fara zuwa da korafi, ina sake jaddadawa tabbas sai hukumar ta sami korafi musamman daga matan da aka aurar, domin duk matar da ta sami matsala ba gidan ubanta zata nufaba, hukumar zata nufa, kaga kenan ana yunkurin daura wani daga gefe guda kuma ana kokarin sasanta na baya don gudun sakwarkwacewa, Allah ya kiyaye.

Idan kuma muka shiga cikin hukumara Hizbar, zamuga irin yadda korafi ya yi yawa na korar da yawa daga cikin ‘yan Hizbar da wannan gwamnatin ta gada daga gwamnatin baya ta Mallam Ibrahim Shekarau. Daman kuma an zargi gwamnatin PDP ta Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso tun farkon hawanta cewa za ta kori ’yan Hisba bisa zargin sun taka rawa wajen goya wa gwamnatin Malam Ibrahim Shekarau baya a lokacin zaben da ya gabata, tare da kokarin ganin wannan gwamnati ba ta kai ga nasara ba. Domin yanzu haka rahotannin da suke fitowa daga hukumar suna nuna cewa ansauke dukkan kwamadoji na kananan hukumomi 44 da wannan gwamnati ta gada, sai dai kuma, kamar yadda mataimakin kwamanda ya kare wannan batu da cewa tunda ansamu sabon kwamanda a jiha ya zama tilas, a kananan hukumomima a samu sabbin kwamandoji, yace wannan al’adace ta sauyin kowace irin gwaamnati.

Sannan kuma, hukumar ta bullo da wani shiri na tantance dakarunta inda ta ce ta yi hakan ne don tsabtace hukumar, amma sai wadansu daga cikin ’yan Hisbar suka ki a tantance su bisa zargin an shirya haka ne da boyayyiyar manufa ta a ci musu mutunci suna zargin cewa akwai shugabannin Jam’iyyar PDP na kananan hukumomi a cikin aikin. Hakika mun kyautata zato ga sabon babban kwamanda Mallam Aminu Daurawa, amma kuma kada wannan ya tabbata cewa suma suna siyasa in da rahotanni suka nuna kamar anayin bita da kulli ga ‘yan Hizbar, domin yanzu zancen da akeyi ance ankori kusan mutum 2,357 daga aiki a kananan hukumomi 23 da suka hada da Makoda da Madobi da Warawa da Fagge da Albasu da Tsanyawa da Sumaila da karaye da Rogo da sauransu. Sannan ba’a bayar da bayanin cewa su wadan nan da aka kora ma’aikatan bogi bane, idan har wannan ba bita da kulli bane me ye dalilin da zaisanya a kori wadan nan mutane daga aiki? alhali da yawa daga cikinsu sun dogara da wannan aiki da sukeyi kasancewar suna da iyalai.

Kamar yadda suka ce, an zargi da yawada daga cikin ‘yan Hizbar da sanya baki a siyasa. Musamman kwamandoji na kananan Hukumomi da ake musu kallon sun dafawa gwamnatin da ta gabata ta mallam Ibrahim Shekarau, amma kuma kamar yadda Mataimakain babban kwamanda na jiha Dr Maigida Kacako yace hukumar bata hana kowa yabi ra’ayinda yake so a siyasa ba, amma kada ya yi amfani da aikin Hizba a siyasa, idan har da gaske hukumar take, suke akan wannan batu, to da alama suna tufaka suna warwara. Allah shi ne maSani mai hikima.

Yasir Ramadan Gwale

yasirramadangwale@yahoo.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment