Saturday, April 7, 2012

Hattara Dai Sardaunan Kano!!!



Mallam (Dr) Ibrahim Haruna Shekarau Sardaunan Kano wazirin Raya kasar Nufe, kuma tsohon gwamnan kano, basarake, jigo a siyasar jihar kano da Najeriya. Hakika mallam shekaru bashida bukatar fassara a siyasar Najeriya, tun daga Patakwal har Jibiya, haka kuma, tundaga Badagary har zuwa Nguru, sunan Sardauna ya kewaya tun lokacin yana gwamna, ballana tana kuma, mutumin da ya yi takarar shugaban kasa, a babbar jam’iyyar adawa.

Ya maigirma Sardauna! Hakika kana daga cikin mutane kalilan da Allah ya yiwa wata irin baiwa marar misaltuwa a tarihin siyasar Kano da Najeriya. Allah ya baka zalakar harshe da iya magana da bayani wanda duk mai sauraronka da budaddiya kuma kyakkyawar zuciya dole ya gamsu da kalaman bakinka, hakika wannan, wata baiwa ce da Allah ya yiwa mutane kalilan, sannan kuma, Allah ya kimsa maka nautsuwa da takatsantsan a tsakanin jama’a, domin a irin yadda Allah ya yi maka ni’ima ta kasancewa mai mulki ba kowa ne za’a taba mutuntakarsa ya yafe ba.

Ya mai girma Sardauna, kamar yadda tarihinka ya nuna, ka shiga siyasa ba tare da kana da wasu kudade na kuzo mu gani ba, duk da cewa a zamanin da muke ciki, tsarin jari hujja shike tafiyar da siyasa; haka ka fito takarar gwamna baka da kowa sai Allah kamar yadda kake cewa, kuma cikin ikonsa ya yi maka jagora, kana matsayin tsohon malamin makaranta kayi takara da gwamna mai-ci, da yake Allah shi ne malikul mulki ya kwace daga hannunsa ya damka maka, wannan ma wata baiwace da duk kasar nan babu wanda Allah ya yiwa irin wannan gamdakatar din, ya mai girma Sardauna, ka zama gwamna a wani lokaci da ya zowa da wasu da bazata, wadan da suke ganin cewa kai din ba kowa bane, kuma ba komai bane, sannan, wasu kuma ya zo musu suna masu kyautata zato zuwa ga mamallakin mulki.

Ya maigirma Sardauna, hakika Allah ya haskaka jihar kano da mulkinka. Jihar kano kamar yadda kowa ya sani kusan itace jagorar sauran jihohin Arewacin Najeriya, kuma jihace ta malamai musamman bangarori uku, wato ‘yan darikar Kadiriyya da darikar Tijjaniyya da kuma ‘yan Ahlussunnah ko Izala kamar yadda sunan yafi shahara, haka kuma kano, jiha ce ta ‘yan kasuwa tun usuli, jihar kano tayi fice a fannoni daban daban, sannan kuma Allah ya azurtata da salihin mutum irin Sardauna, hakika mun shaida cewa lokacin da kake gwamna kayi kokarin kamanta adalci ga musamman bangarorin dariku da muke dasu, wannan kuma, bazai hana wasu su fahimci akasin haka ba. Ka taba kusan dukkan bangarori, domin hattana nakasassu wadan da ba’aciki lura dasu a cikin al’umma ba ka jawo su ajiki inda ka nuna suma mutanene kamar kowa, wanda yafi wani shine wanda ya fi tsoron Allah, sannan kuma, a lokacinka ne mutane masu addini suka sami gata a harkar tafiyar da gwamnati, haka kuma ayyukan da ake ganin babu ruwan hukuma da su ka nuna lallai hukuma tana da ruwa da tsaki da su, kamar harkar makarantun allo da alarammomi, sanna kuma, idan ana batun ayyukan raya kasa nanma babu mai ganin baikenka, tabbas kano ta haskaka kuma ta tserewa saura ta bangarori da dama.

Ya mai girma Sardauna, lokacin da wa’adin mulkin ka na biyu ya zo karshe, jama’a da dama ciki da wajen jihar kano sunata yimaka kiraye kiraye akan ka fito takara, wasu na ganin ka fito takarar sanata wanda shine mukamin da tsaffin gwamnoni suka fiya tsayawa bayan gama wa’adinsu, wasu kuma, suna ganin ka fito takarar Shugaban kasa bisa irin yadda suke kyautata zato a gareka cewa zakayi adalci ga al’ummar Najeriya kamar yadda ka nuna a jihar kano, domin ansamu fahimtar juna da sauran kabilun kudancin kasarnan da al’ummar jihar kano a lokacinka, da kuma mabiya addinin kirista, inda har ka nada mutane wadanda ba ‘yan kanoba a cikin gwamnatinka, sannan kuma ga zaman afiya da aka samu a kusan tsawon wa’adin mulkinka. Wannan kira da al’umma suka ringa yi maka ya yi tasiri kwarai da gaske baga kai kadaiba harda sauran magoya bayanka, hardai daga karshe ka yanke shawarar tsayawa takarar shugaban kasar Najeriya.

Tabbas, ya mai girma Sardauna, kayi takarar Shugaban kasa. Kuma Allah shi ne masanin abinda bamu sani ba, wasu suna cewa, boyayyar alakace tsakaninka da gwamnatin PDP domin ka kawo cikas ga kuri’un Arewa, wanda ga duk mai hankali yasan da cewa tsarin mulkin Najeriya ne ya baka wannan dama ta tsayawa ko wane irin mukami, kuma babu wani laifi da kayi da ka tsaya wannan takara, wanda kuma yace kudi aka baka ka tsaya takara wannan tsakaninka ne da shi dakuma Allah, domin Allah shi ne masani kuma mai hikima, yasan abinda yake boye da sarari. Bayan ka kewaya kusan jihohin kasarnan domin yakin neman zabe, nasan wannan wani babban aiki ne da zaibaka damar ganin halinda yankunan kasarnan mabambanta suke ciki. Bayan da akayi zabe kuma sakamako ya fito, ance kaine kazo na uku a ‘yan takarar da suka fito daga yankin Arewa, wato na hudu kenan a kasa baki daya, Goodluck Jonathan shine wanda akace ya sami nasarar wannan zabe, sai Gen. Muhammadu Buhari a matsayin na biyu da Mallam Nuhu Ribadu a matsayin na uku da kuma kai maigirma Sardauna a matsayin na hudu. Wasu na cewa daman nasan za’a rina wai ansaci zanin mahaukaciya, wasu kuma na fadin maganganun da basuda hakikanin masaniya akansu, haka dai jama’a sukayi ta fashin baki akan wannan takara da ka tsaya, Allah dai shine masanin abinda yake fake.

Ya maigirma Sardauna, kamar yadda ka sani, tsarin siyasarmu tsari ne na jari hujja, kamar yadda ake yi a Amerika. Da yawan kananan magoya baya a yanzu suna ganin lokaci na gaba mai zuwa ka sake gwada sa’a a wannan takara ko Allah zaisa a dace; a wannan gabace nake so nayi kira ga Sardauna da cewa lallai yayi hattara da masu yi masa wannan kiran, domin shakka babu maganar takarar Shugaban kasa magance babba kuma mai bukatar abubuwa da yawa, musamman abin da akafi sani a siyasance da kayan aiki, nasan da cewa lokacin da katsaya takara ka samu gudunmawa daga ‘yan uwa da abokan arziki da magoya baya da yawa, saboda kana kan kujerar gwamna a lokacin da kake neman wannan takara. Ya maigirma Sardauna lallai yanzu kai ba mutum bane da za’a baiwa shawara akan harkar takarar shugaban kasa, saidai ka baiwa wani, duk da haka, zamuyi karambanin isar da namu sakon gareka.

Ya maigirma Sardauna a lokacin da Bashir Tofa ya tsaya takarar Shugaban kasa, a zaben 12 ga watan yuni da akafi sani da june 12, kusan yana da goyon bayan gwamnatin soja ta General Babangida a wannan lokaci amma duk da haka bai kai ga nasara ba, ko shakka babu, bama gafala da cewa wannan wani hukunci ne na ubangiji, a wancan lokaci Bashir Tofa yana da goyon baya a jihohi da dama na kasarna, sannan duk da haka Bashir Tofa ya cigaba da gwada sa’arsa domin neman wannan takara, amma Allah bai bashi nasaraba ko da kuwa tsallake matakin farko na jam’iyya, haka abin yazo har lokacin da kukayi takara tare da shi ka kuma samu galaba akansa, akaikaice wannan yana nuna cewa lallai farin jinin Alhaji Bashir Tofa ya ja baya ainun daga yadda aka sanshi a 1993. Kuma wannan yake nuna cewa kusan yanzu a siyasar Najeriya musamman ta shugaban kasa duk mutumin da ya yi takarar farko bai samu nasaraba to idan ya sake nema farin jininsa na dusashewa idan aka auna farkon fitowarsa, idan muka kalli Gen Muhammadu Buhari zamu tabbatar da haka, domin farin jinin Buhari a 2007 ya ragu kafin 2011, wannan kuma yana nuna irin yadda siyasar kasarnan ta dauki wannan salon.

Ya maigirma Sardauna, yanzu kai ka zama uban kasa, kuma uban al’umma. Hakika Najeriya tana bukatar mutum irinka, domin Allah ya baka daukaka a tsakanin sauran takwarorinka tsaffin gwamnoni, don babu wani da ake cin-cirondo dominsa sai kai, wannan kuma yake nuna cewa lokaci zaizo, kana gidanka a mundubawa Najeriya zata nemi agajinka, domin sanin kowa ne, idan al’amura suka rincabe dole a bukaci mutane wadan da zasu iya magana a sauraresu, wadanda kuma suke da zalakar harshe, wanda kuma maganarka tanada matukar tasiri a tsakanin magoya bayanka da kuma sauran al’ummomin kasarnan.

Maganar takarar shugaban kasa a nan gaba, ya mai girma Sardauna tana bukatar a tsaya ayi mata duba na tsanaki. Shakka babu kamar yadda na fada kai ba mutum bane da za’a baka shawara akan wannan batu saidai ka bayar, kuma nasan yanzu kana iya rubuta babban littafi mai sufulai da yawa idan ambaka maudu’i akan hakan, don haka ga masu yin kira cewa ka fito takara a 2015, lallai a duba wannan batu, kai tsaye bazance kada maigirma sardauna ya sake yin takara ba, haka kuma bazan ce kada yaki tsayawa takaraba, amma dai abinda masu iya magana ke cewa kana kallon tarihin rayuwar wasu domin samun yadda zaka inganta taka, hakika wadanda suka gabaceka zasu zama ishara a gareka, da sauran al’umma.

Daga karshe, ina mai yin fatan alheri a gareka, kuma ina rokon Allah yacigaba da yi maka jagoranci, ya shiga tsakaninka da makiyanka da kuma mahassada, Allah ya zaba maka abinda ya ke shine mafi a’ala a gareka da kuma al’ummar jihar kano da Najeriya baki daya, wassalam ka huta lafiya.

Yasir Ramadan gwale

yasirramadangwale@yahoo.com

http://yasirramadangwale.blogspot.com

No comments:

Post a Comment