Saturday, August 2, 2014

SHI'ANCI: Mai Hankali Yi Tunani


SHI'ANCI: Mai Hankali Yi Tunani!

Sau da dama akan jiyo mabiya addinin Shia'ah karkashin jagorancin Zakzaky suna kira a garemu MU al'ummar Musulmi Ahlussunnah da mu zo a hada kai dan a yiwa addinin Allah aiki a kuma fuskanci abokan gaba tare, wannan kira ba bako bane a kusan kunnan kowa. Wannan magana tana nuna cewar su 'yan SHI'AH sun yarda da cewar MU al'ummar Musulmi Ahlussunnah Musulmi ne, kuma sun yarda da Musuluncinmu dan haka ne suke fatan mu hadu tare da su dan baiwa addinin Allah kariya, ya dan uwana mai karatu, Tayaya 'yan Shia'ar da basu yarda da Musuluncin Abubakar RA da Umar RA da Utham RA da Nana-Aisha RA da Nana-Hafsa RA ba amma kuma mu suka yarda da Musuluncinmu? Shin lafiyayyan hankalin zai karbi wannan magana, ace mu ka yarda da Musuluncinmu dan haka kake kiranmu da mu hada kai da kai, amma kuma kana tuhumar Manyan Sahabban Manzon Allah SAW cewar ba Musulmin kwarai bane. Mai Hankali yi tunani!

Ai bana jin akwai zalincin da ya kai mutum ya kore Abubakar RA da Umar RA da Utham RA da Nana-Aisha RA da Nana-Hafsa RA daga Musulunci ya kafirtasu sannan kuma shi ya kira kansa Musulmi Masoyin Manzon Allah SAW shin lafiyayyan hankali zai karbi wannan maganar? 'Yan Shi'ah mugayen azzalumai ne fasikai mujirimai, tsammaninsu muma tunaninmu irin nasu ne, suna tsammanin munyi kama da wadan da za'a yaudara da kalmar HADIN-KAI? Ai tun ran gini tun lokacin zana shi, babu wata magana mai dadi da 'yan Shi'ah zasu iya janyo hankalinmu da ita dan mu hada kai da su muddin suna kudire cewar wadannan sahabban da na ambata ba Musulmi ba ne.

Mu Ahlussunnah da kuke gani munyi imani cewar duk duniya babu wani dan Adam da ya kai Abubakar RA bayan Manzon Allah SAW girma da matsayi a Musulunci. Dan haka duk wani wanda yake zaton wai zamu tausayawa dan Shi'ah dan yana ikirarin an zalunce shi to ya sauya tunani, ai asalima mu a wajenmu duk abinda aka yiwa dan Shi'ah ba'a zalince shi ba, domin shi ne Azzalumi na tun farko, dan babu Azzalumi face wanda ya kore Abubakar RA da Umar RA da Utkam RA da Matan Manzon Allah SAW daga Musulunci sannan shi kuma ya tabbatar da kansa a matsayin Musulmi har yake tunanin baiwa addini kariya.

Ya dan uwa gabarmu da Shi'anci fa da gaske muke, muna tsananin kyamar shi'anci. Amma kuma mu din ba makiya ne na 'yan Shi'ah ba, sai dai akidar da suka kudurce ita muke kyama, yau idan da Zakzaky zai tuba ya Musulunta ya daina Shi'anci wallahi zai samemu masoya na hakika a gareshi fiye da jahilan da suka kewaye shi suke masa bauta, dan mu Muna yin soyayya ne dan Allah ba dan wani abin daban ba. Kuma muddin mutum ya mutu ko aka kashe shi yana SHI'ANCI wallahi summa tallahi ba zamu taba yi masa addu'ar Allah ya jikansa ba ko ta wacce irin hanya ya mutu matukar da waccan mugunyar Aqidah a tare da shi.

Mu bamu taba yin murna dan wani ya mutu ba, dan munyi Imani mutuwa tana kan kowa, kasancewarmu a raye shi ne yake tabbatar mana da cewar watan wata rana ajali zai riskemu mun shirya ko bamu shirya ba, dan haka duk wanda ya yi murna dan wani ya mutu, to shima tana nan zuwa kansa indai mutuwa ce.

Dan haka babu ruwanmu da batun wai an zalinci 'yan shi'ah mu tausaya musu, ai mu bamu ga inda aka zalince su ba, domin babu yadda mutane zasu tare hanya su hana Gwamna wucewa su hana Sarki wucewa su hana jami'an tsaro wucewa sannan a ce wai wadannan ba Azzalumai ba ne, ta ina! Ai idan har aka cigaba da kyale wannan Zalincin to ya nuna cewa wasu Shaidanun mutane sunfi karfin doka, ai dole a tauna tsakuwa dan aya ta ji tsoro, duk wanda ya keta doka to doka ta yi aiki akansa ko waye shi, ko mune muka saba ka'idar hukuma a zartar mana da hukuncin da doka ta tanada. Dan haka muna kira ga hukuma lallai duk wanda ya karya doka to hukunci ya hau kansa. Ai dan tuwon gobe ake wanke tukunya. 

02-07-2014

No comments:

Post a Comment