Wednesday, August 6, 2014

NETANYAHU: Yaki Ya Kare A Yankin Zirin Ghazza

Netanyahu

NETANYAHU: YAKI YA KARE A YANKIN ZIRIN GHAZZA

Shugaban haramtacciyar kasar Israela Benjamin Netanyahu - בנימין נתניהו a ganawar da yayi da manema labarai dazu-dazun nan, ya shaidawa duniya cewar yakin zalinci da suka shafe kwanaki 29 suna aiwatarwa akan al'ummar Ghazza ya zo karshe, hakan dai na zuwa ne tun bayan amincewar da Bangaren Palasinawa na Hamas da kuma ita Israelan suka yi na tsagaita wuta na awanni 72. A yayin da yake wannan ganawa da Manema labarai, Netanyahun ya nuna musu wani hoton Video dake nuna WAI irin hare-haren roka da hamas suka kai Israelar wanda hakan yayi sanadiyar mutuwar Yahudawa 64.

Sai dai a cikin jawaban nasa, Netanyahu ya nuna cewar sun tafka kusakurai da dama wajen wannan yaki inda yace sun kai hare-haren da suka yi sanadiyar mutuwar fareren hula da yawa, ya kara da cewar babu yadda zasu yi dole ce ta sanyasu kai wannan hare-haren a cewarsa suna yi ne dan kare al'ummar kasarsu ta Yahudawa, ya kara da cewa Hamas sun fake da farerenn hula ne dan samun kariya. Haka kuma Netanyahu ya kwatanta kungiyar Hamas da kungiyoyi irinsu Boko Haram da Hizbola da kuma ISIS.

A wannan yaki da aka yi kimanin mutane 2000 ne Israela ta kashe a yankunan zirin Ghazza wadan da galibinsu yara ne da mata da tsaffi, sanna kuma hare-haren da Israelar ta kai sun raunata sama da mutum 10000, haka kuma sama da 100,000 sun tsere daga gidajensu da samun mafaka, bayaga dubban gidaje da aka rurrusa a unguwanni da dama na yankunan Palasdinawa a yankin zirin Ghazza, hari mafi muni shi ne wanda aka kai a unguwar Shejaiyah wanda dubban kananan yara suka rasa rayukansu, haka kuma mata da dama sun rasu a wannan unguwa, haka abin yake a unguwannin Bait-Hanun da Khan-Yunis inda dubban gidaje da Masallatai da makarantu suka kasance a rurrushe.

Sai dai a nasu bagnaren kasar Amerika bayan goyon baya da suka bawa kasar Israela a wannan yakin tare da nuna cewa Israela na da ikon kare kanta da kuma nuna cewar Hamas kungiya ceta yan ta'adda, Amerika din ta bayar da sanarwar tallafin Dala Miliyan 49 dan sake gina yankunan Palsdinawa da yaki ya daidaita a yankunan zirin Ghazza.

Tuni dai daman aka soma wata tattaunawa a birnin Alkahiran kasar masar ranar Asabar tsakanin bangarorin Palasdinawa da Isrela karkashin sa-idon Majalisar dinkin duniya da kuma gwamnatin Masar. Fatanmu shi ne Allah ya taimaki Palasdinawa mazauna Ghazza ya kara musu karfin Imani, ya dora su akan abokan gabarsu Yahudawa a koda yaushe. Ya Allah kada ka kuma maimaita musu irin wannan mummunan zubar da jini. Allah ka taimaki kasashen Musulmi.

YASIR RAMADAN GWALE
06-08-2014

No comments:

Post a Comment