Saturday, August 9, 2014

Al-jana A Kano

ALJANA A KANO: A can wani shudadden lokaci a Kano anyi wata Aljana da ta addabi mutane a Kano ta razana al'umma sosai amma kuma babu wanda ya taba ganin wannan aljanar, ita dai wannan aljana ina zaton sunanta 'yar Madabo, amma ance zuwa gidan mutane ta ke yi ta ce musu su bata ruwa ta sha, indai aka bata ruwan to da ta sha zata watsar da ragowar a gidan shi kenan mutan gidan zasu mutu, a yadda labarin ya yadu a lokacin kenan, a wannan lokacin rigakafin wannan aljana shi ne a barbade kofar gida da toka, ance indai Aljanar ta zo kofar gidan taga Toka ba shakka ba zata shiga ba. Ina iya tuna lokacin da su Ali Aliyyu Gwale suka dinga fito da murhu daga cikin gidansu suna barbade kofar gidan da toka, mu kuma muna zaune a makarantar Allo a lokacin. Sau da dama tarihi kan maimaita kansa a wasu siffofi ko kamanni mabanbanta. Nima naga alamun zamu yi maza-maza ni da Zainab mu saro gishiri dan muci zamar Ebola. Allah ya karemu daga Aljana Ibola.

YASIR RAMADAN GWALE
08-08-2014

No comments:

Post a Comment