Wednesday, August 20, 2014

ADAMAWA: Malam Nuhu Ribadu Ya Shiga Takara Gadan-Gadan


ADAMAWA: MALAM NUHU RIBADU YA SHIGA TAKARA GADAN-GDAN

Malam Nuhu Ribadu ya fanshi tarkadun tsayawa takarar Gwamnan jihar Adamawa a karkashin jam'iyyar PDP mai alamar lema. Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah madaukakin sarki da ya albarlaci Malam Nuhu Ribadu da tsayawa wannan takara, domin bayar da tasa gudunmawar dan cigaban al'ummarsa, dan samar musu da ingantacciyar rayuwa, dan inganta ilimi da kiwon lafiya da sufuri, dan taimakon addinin Allah. Wannan takara ga Allah Malam Nuhu Ribadu yake nema, yabiyo hanya kamar yadda ta halatta ga duk mai neman takara ya gabatar da bukatarsa a karon farko ga jam'iyya, idan Allah ya kaddara cewa shi ne dan takara a bazama wajen jama'a dan neman goyon bayansu.

Malam Nuhu Ribadu ba attajiri bane, bai tara abin duniya dan baiwa mutane dan abin hasafi su zabe shi ba, yana fatan jama'a su tsarkake zukatansu, su duba cancantarsa wajen wannan aiki. Ba shakka mun shaida cewa Ribadu ya cancanci rike duk wani mukami a fadin tarayyar Najeriya.

Gaskiya da rikon amana irin ta Malam Nuhu Ribadu ta bayyana tun bayan da ya zama mataimakin kwamashinan 'yansanda, inda daga nan yaci gaba zuwa Shugaban hukumar EFCC da al'ummar Najeriya da sauran duniya suka shaida kwazonta. A saboda kwazo da aiki da gaskiya ta sanya har aka yiwa Ribadu tsallaken mukami a aikin dan sanda. Allah ya tabbatar da alheri a wannan takara. Zabin Allah shi ne zabi, muna yiwa mutanan Adamawa fatan samun Malam Nuhu Ribadu For Adamawa State Governor 2014.

Ya Allah kayi riko da hannun Malam Nuhu Ribadu idan ya zama Gwamna, Allah kada ka barshi da iyawarsa, Allah ka zama gatansa. Gareka muke nema Lam Yalid Wa Lam Yu Lad.

YASIR RAMADAN GWALE
20-08-2014

No comments:

Post a Comment