Sunday, August 10, 2014

OSUN: PDP Ta Yi Nasara, RAUF Kuma Ya Ci Zabe


OSUN: PDP TA YI NASARA, ROUF KUMA YACI ZABE

Dazu Abubakar Aminu Ibrahim yake gayamin cewar sakamakon zaben jihar Osun ya fito inda PDP ta samu Nasara fiye da wadda ta samu a baya, yayin da Gwamna mai ci ya sake komawa. Ina amfani da wannan damar na taya Malama Zainab (Yazain) murnar Nasarar da jam'iyyarsu ta samu a jihar Osun, ina kuma taya USTAZ RAUF AREGBESOLA murnar samun wannan nasara da yayi.

Babu shakka nauyi ya kuma hawa kansa (Aregbesola) bayan wanda ya d'auka shekaru hudu da suka gabata, yanzu ma an sake bashi amanar al'ummar jiharsa ta Osun. Muna kira a gareshi da yaji tsoron Allah wajen alkinta dukiyar al'ummar da yake shugabanta, ya kuma sani cewar zai zama abin tambaya ranar Alkiyama akan Amanar da aka danka masa ta Mulkin Jama'a.

Muna fatan Allah ya yi riko da hannunsa wajen aikata daidai, haka kuma muna kira a gareshi ya yi kokari wajen yaki da cin-hanci da rashawa, ya kuma yi iyakar iyawarsa wajen inganta rayuwar al'umma. Ina masa fatan alheri da fatan gamawa lafiya. Shi kuma dan takarar PDP da bai samu zabe ba Allah ya bashi dangana, ya kuma tsananta masa rabo a nan gaba. Wassalamu Alaikum Warahmatullah.

YASIR RAMADAN GWALE
10-08-2014

No comments:

Post a Comment