Saturday, August 30, 2014

Nuhu Ribadu Ne Yafi Dacewa Ya Zama Gwamnan Adamawa - Abdullahi Dahiru


NUHU RIBADU NE YAFI DACEWA YA ZAMA GWAMNAN ADAMAWA - Abdullahi Dahiru

Anyi kira ga al'ummar jihar Adamawa da su kada kuri'arsu ga Malam Nuhu Ribadu a zaben da za ayi nan gaba a wata mai kamawa idan har Ribadu ya samu sahalewar jam'iyyarsa ta PDP. Wannan kiran ya fito ne daga bakin wani Likita kuma mai fashin baki da sharhi akan al'amuran siyasa da zamantakewa da rayuwar al'umma a Najeriya.

Dakta Abdullahi Dahiru ya bayyana Malam Nuhu Ribadu a zaman mutumin kirki mai gaskiya da tsoron Allah. Da yake karin bayani a shafinsa na facebook Dakta Dahiru ya kara da cewa Malam Nuhu Ribadu ya tsrewa sa'a wajen zama gwamnan jihar Adamawa a tsakanin abokan takararsa.

YASIR RAMADAN GWALE 
30-08-2014

No comments:

Post a Comment