Tuesday, August 12, 2014

Azumin Sitta Shawwal


AZUMIN SITTA SHAWWAL

Manzon Allah SAW yace ku tunasar domin tunasarwa tana amfanar Muminai. Ina amfani da wannan damar wajen tunasar da kaina da sauran 'yan uwa cewa yau Talata 17 ga watan Shawwal. Kamar yadda Malamai suka sha yin bayanin Azumin Sitta Shawwal da irin falalarsa, lallai wadan da basu samu damar yn wannan azumi ba su daure su azumici kwanaki shidda kafin shudewar wannan wata nan da makwanni biyu masu zuwa. Allah ya sa mu dace da babban rabo, ya kuma sanya ibadun da muka gabatar a Ramadan karbabbu ne, ya inganta cewa Sahabbai sukan yawaita maimaita addu'ar Allahumma Taqabbal Minna (Allah ya karbi Ibadunmu) bayan shudewar kwanakin Ramadan. Allah ya yaye mana dukkan masifu da bala'o'in da suke damun mu.

A 'yan kwanakin nan rahotanni sunce 'yan Ta'adda sun shiga garin Gwoza a Borno inda suke yunkurin kafa iko a wajen, muna addu'ar Allah ya kawo mana dauki a cikin wannan al'amari. Ba shakka an aikata dukkan dangin ta'addanci da rashin Imani a jihar Borno da kewayenta, muna add'ar wadan da suka rasu Allah ya jikansu ya gafarta musu, marasa lafiya kuma Allah ya jikansu.

Muna rokon Allah ya arzurtamu da alkhairan duniya da lahira. Shugabanninmu Allah ya sanya tausayin al'umma a zukatansu. Allah ya shiryemu shiriya ta gaskiya.

YASIR RAMADAN GWALE
12-08-2014

No comments:

Post a Comment