Sunday, July 27, 2014

Sakon Barka Da Sallah Cikin Alhini

SAKON BARKA DA SALLAH CIKIN ALHINI

Amadadin ni YASIR RAMADAN GWALE da Zainab da su Utman, da dukkan 'yan uwa da dangi da abokan arziki muna mika sakon taya murnar Barka Da Sallah na wannan Shekara ga dumbin al'ummar Musulmi musamman a Najeriya da suka Sallahci wannan rana ta yau a matsayin Ranar idin karamar Sallah wanda hakan yake tabbatar da karewar kwanaki 29 masu albarka na watan Ramadan, Allah ya sa ibadun da muka gabatar a wannan wata karbabbu ne, laifukan da muka yi a wannan wata wadan da muke sane da wadan da bama sane Ya Allah kai mai afuwa ne kana son Afuwa, Allah ka yi mana afuwar laifukanmu.

Babu shakka lokacin Sallah lokaci ne na murna da farinciki da kuma ambaton Allah. Ina amfani da wannan damar wajen yiwa kaina Nasiha da jin tsoron Allah da kiyaye dokokin Shari'ah a yayin gudanar da Shagulgulan Sallah. Allah ya maimaita mana ta badin badada lafiya.

Babu shakka dole mu yi alhinin halin da kasarmu ta ke a ciki na zaman zullumi da razani da wadansu makiya Allah makiya zaman lafiya makiya addinin Allah suka sanyamu a ciki, Ya Allah kasansu kasan duk inda suke a labe, kasan irin makircin da suke kulla mana Allumma rudda kaiduhum Alaihim! Al'ummar Musulmi da yawa a yankin Ghazza na Palastine zasu yi Sallah a gobe cikin tashin hankali da fargaba da razanai sakamakon hare-haren zalinci da Israela ke kai musu, Allah ka amintar da su ka sanya wadan da suka rasu su tashi a matsayin Shahidai, yan uwanmu da aka karkashe a Borno da Yobe da Adamawa da Kano da Kaduna da sauran jihohinmu Allah ka jikansu ka gafarta musu.

Allah ka bamu lafiya da zaman lafiya a duk inda muke. Yana da kyau idan mun hadu da juna mu yiwa juna addu'ah tare da fatan karbuwar ibadunmu. Wata Shekara a BUK Sheikh Abubakar Jibrin ya ce a Rungume juna a yi murna. Barka Da Sallah.

Yasir Ramadan Gwale
27-07-2014

No comments:

Post a Comment