Wednesday, July 9, 2014

Al-amura Sun Ta'azzara a Yankin Zirin Ghazza



AL'AMURA SUN TA'AZZARA A YANKIN ZIRIN GHAZZA

Babu shakka a cikin wannan makon al'amura sun ta'azzara a yankin zirin Ghazza ta Palastinu tun bayan kisan matashin nan Muhammad Abu Kheidr dan shekaru 16 da wasu Yahudawa suka halaka shi a Jerusalem. Wannan kisa na Muhammad Abu Kheidr ya ja hankalin kasashen duniya sosai, kasancewar matashin da aka kashe yaro karami, wannan ta sanya Piraministan Israela Benyamin Netanyahu ya fito ya yi Allah wadai da kisan da Yahudawa Barbarar yanyawa sukaiwa bapalasdine, inda ya bayyana kisan da cewa wani abin takaici ne mai muni da ya zubar da mutuncin Yahudawa, ya kuma sha alwashin kamo wadan da suka yi wannan kisa tare da hukunta su. Sai dai kungiyar Hamas da ke da iko da Birnin Ghazza da kuma Gwamnatin Mahmoud Abbas Abu-Mazein ta soki lamirin wannan kisa da aka yiwa Muhammad Abu Kheidr.

A nasu bangaren, kungiyar Hamas ta sha alwashin kai hare-haren ramuwar gayya da makaman roka, inda rahotannin daga kafafen yada labarai na kasashen Turai suka bayyana cewar an harba Makaman Roka sama da 200 zuwa cikin yankin kasar Israela daga zirin Ghazza. Tun bayan wannan hare-hare ne aka jiyo Netanyahu na magana da kakkausar suka akan wadannan hare-hare na ramuwar gayya, duk kuwa da gagarumin sabanin da aka samu a gwamnatin natenyahu tsakaninsa da Ministan harkokin wajen Israela Agvidol Liberman.

Al'ummar kasar Palastinu da ke yankin zirin Ghazza sun ga tashin hankali mummunan daga irin hare-haren da Israela ta ke kaiwa babu kakkautawa zuwa yankin, duk kuwa da cewar suna dauke da Azumi. Babu shakka Israela ta yi muguwar barna a yankin Ghazza tare da kashe mutane da dama da jikkata wasu da rusa gidaje da makarantu a yankin na Ghazza. A nasu bangaren mai magana da yawon fadar White House dake Amurka ta nuna cewar Israela na da ikon kare kanta daga hare-haren Roka. shima a nasa bangaren Sakatare Janar na majalisar dinkin duniya Banki-Moon ya yi kira da cewa akai zuciya nesa, dan wannan ba lokaci bane na ramuwar gayya a cewarsa.

Hakika Palastinawa dake yankin Ghazza suna cikin ukuba da Israela ta ke yi musu. Ya Allah ka kai musu dauki, ka wargaza dukkan wani shiri na Azzalaumar haramtacciyar kasar Israela, ka rusa gwamnatin Netanyahu da 'yan kanzaginsa da masu goya masa baya. Allah ya baiwa Palasdinawa nasara akan abokan gabarsu, Allah ka daukaki Musulunci da Musulmi ka kaskantar da kafirci da kafirai.

Yasir Ramadan Gwale
10-07-2014

No comments:

Post a Comment