Thursday, July 24, 2014

Kano

KANO: Jiya muka yi alhinin abinda ya faru a Kaduna na tashin bom da ya yi sanadiyar halakar mutane da dama, kwatsam kuma yau muma sai gashi an gaishemu da shi a Kano. Babu shakka Allah Buwayi Gagara Misali Assami'u Ne kuma Albasiru! Idan wadannan masu tayar da hankali sun faku a garemu babu shakka ba zasu iya kaucewa ganin Ubangiji ba. Muna tunawa wadannan miyagu azzalumai cewa tunda Allah ya halicci duniya ya halicci lokaci, da sannu suma lokacinsu zai riskesu, zasu su mutu suna wulakantattu abin wualakntawa. In Sha Allahu azzalaumai ba zaku ci nasara ba, ku koma ku karanta tarihi babu wani wanda ya shuka zalinci kuma rayuwarsa ta dore, duk wani dan iska da yace muku wannan hanya ce ta shiga Al-jannah ya cuceku, da ku da shi zaku dandana kudarku a wajen Allah ba zamu gushe ba muna yi muka fatan Narko na azabar Allah. Miyagu azzalumai 'yan ta'adda marasa tsoron Allah munafukai.

Ya Allah ba dan halinmu ba, Ya Allah ba dan laifukan da muka aikata ba, Ya Allah mun tuba ka yafe mana laifukanmu. Allah ka bamu lafiya da zaman lafiya, Ya Allah kada ka baiwa mmiyagu azzalumai 'yan Ta'adda Nasara akan al'ummarmu. Allah duk wadan da suke shirya wannan mummnan tashin hankali Allah ka sansu kasan a duk inda suke Allah ka wargaza sha'aninsu, Allah ka rusa su, Allah ka dammara su, Allah karka basu alherin duniya da lahira. Allah ka azabtarda su azaba mai radadi.

Allah ka amintar da mu. Allah ka bamu lafiya da zaman lafiya. Wadan da suka rasa rayukansu a tsakanin jiya a Kaduna da yau a Kano Allah ya jikansu ya gafarta musu, wadan da suka jikkata kuma Allah ka basu lafiya, Allah ka sanya abinda ya samesu ya zama kaffara a garesu. Allahumma Taqabbal Minna Du'a'ana Ya Rabbal Alameen.

YASIR RAMADAN GWALE
24-07-2014

No comments:

Post a Comment