Wednesday, July 9, 2014

Godiya Ta Musamman Daga Mundubawa Kano

Sabon Ministan Ilimi Malam Ibrahim Shekarau
GODIYA TA MUSAMMAN DAGA MUNDUBAWA KANO

Muna amfani da wannan damar wajen nuna godiya da jinjina ga dumbin al'ummar da sukai ta aiko da sakwannin fatan alheri ga Sabon Ministan Ilimi na tarayyar Najeriya Malam Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano, hakika jama'a da dama a ciki da wajen Najeriya sun nuna mana soyayya a bisa wannan cigaba da al'ummar Jihar kano da Arewacin Najeriya suka samu na sabon Minista a majalisar zartarwa ta Najeriya. Allah ya sakawa kowa da alheri ya baiwa sabon Ministan Ilimi ikon aiwatar da ayyukan da suke tattare da ofishinsa, Allah ya bashi ikon kawo sauye-sauye masu ma'ana a iya tsawon wa'adin mulkinsa.

Haka kuma, Fadar Mundubawa na maraba da dukkan shawarwari ga sabon Ministan Ilimi daga kowanne Dan Najeriya, kofa a bude ta ke ga duk wanda yake da wata fikra wadda zata ciyar da harkar ilimi gaba a Najeriya. Allah ya taimaki Najeriya, ya azurtamu da shugabanni na gari Adalai.

YASIR RAMADAN GWALE
10-07-2014

No comments:

Post a Comment