Wednesday, July 23, 2014

Jaje Na Ga Gwamnaton Kaduna Da General Muhammadu Bugari

Ramalan Yero
KADUNA: Ba babu shakka labarin da ya fito daga garin Kaduna a almurun yau labari ne mai kada zukata. In Sha Allahu 'yan Ta'adda Miyagu Azzalumai ba za su ci nasara ba, da sannu suma ajalinsu zai riske su, su mutu suna wulakantattu kaskantattu batattu. Allah ka rusa su Allah ka darkakesu ka wargaza duk wani mummunan nufinsu akan al'ummar Musulmi, Ya Allah albarkar wadannan kwanaki da suka rage ba dan halinmu ba Ya Allah ka kawo mana dauki, Allah ka dawo mana da dawwamammen zaman lafiya a kasarmu. Allah ka jikan wadan da suka rasa rayukansu a wannan mummunan tashin hankali.

Lallai wajibin hukumomi ne su dauki dukkan wasu matakai na samar da nutsuwa a cikin zukatan al'ummar da suke Shugabanta, Allah ka baiwa shugabanninmu ikon daukar matakan da suka dace domin dakile wannan Ta'addanci. A madadina da 'yan uwa da abokaina muna mika ta'aziyarmu ga gwamnatin Kaduna da al'ummar jihar Kaduna Allah ya jikan wadan da suka rasu, masu raunuka Allah ka basu lafiya. Muna kuma mika sakon jaje ga Babanmu General Muhammadu Buhari a bisa wannan abu da ya faru da shi, Allah ya kara kiyayewa Allahumma Ameen. Haka kuma muna mika jajenmu ga Sheikh Dahiru Usman Bauchi da shima wannan ibtila'i ya kusa rutsawa da shi, Allah ya kare su da karewarsa. Allah ya bamu lafiya da zaman lafiya.

YASIR RAMADAN GWALE
23-07-2014

No comments:

Post a Comment