Wednesday, July 23, 2014

Zaman Lafiya


ZAMAN LAFIYA

Yana da kyau a;'ummar Najeriya mu maida hankali wajen duban hanyoyi sahihai na yadda za'a dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a dukkan sassan kasarnan. Duba da irin abubuwan da suke faruwa suna nuna cewa kasarmu Najeriya tana da wasu mugayen makiya da basa yi mata wani fata face na rugujewa, suna aiki babu dare babu rana wajen ganin sun firhita al'umma an koresu daga garuruwansu. Da dama al'ummar kudancin jihar Borno sun tsere daga gidajensu wasu sun koma Kamaru wasu Cadi wasu nijar, mwannan babban abin takaici ne mutane su bar mahaifarsu akan laifin da basu aikata ba. Lallai sai mun tashi tsaye wajen ganin wadannan miyagu azzalumai basu ci nasarar wagaza mana kasa ba. Mu sani ba muda wata kasa da zamu je mu yi tinkaho da ita face wannan kasar tamu, babu inda muke da kima da mutunci face a cikin kasarmu. Ya zama dole muyi duk abinda zamu iya wajen ganin kasarmu bata wargaje ba, dole mu koyti yadda zamu zauna da juna lafiya da sauran al'ummat kasarnan.

Yasir Ramadan Gwale
20-07-2014

No comments:

Post a Comment