Saturday, April 11, 2015

Rahoto Daga Kano Dangane Da Zaben Gwamna


RAHOTO DAGA KANO

Da yawa mutanen da suke wajen Kano gani suke kamar mafarki idan ance musu Allah ya bawa Takai Gwamna har ka ji wasu suna izgili ko wani abu makamancin haka.

Inama ace wanda suke wannan tada jijiyar wuyar 'yan Kano ne, da a yau sun ganewa idonsu cewa Kano ta Takai ce da ikon Allah. Akasarin mutanen da suka fito zabe yau idan ka ga mutum goma to bakwai ko takwas za ka ji suna fadin Takai za mu zaba ko ba a bamu ko sisi ba.
Wannan ya canja min tunani na cewa wai kalmar SAK za ta yi aiki a Jihar Kano, sai yau na tabbatar ba dai a garin Kano ba sai dai ko a wata Jihar.

Duk da wannan albishir da muke gani kuma muke ji, wannan bai isa ya sa muke cika baki da kambami ba, illa kawai mu godewa Allah kuma mu kara risunawa gare shi kan ya taimake mu ya bawa Malam Salihu Sagir Takai Gwamnan Kano a wannan zabe da yake gudana yanzu.

Wakilinmu ya sanar da mu halin da ake ciki. Dan haka muna kara kira ga magoya da magoya bayan Malam Salihu Sagir Takai  da su fito domin wannan zabe. Allah ya bamu Nasara,  ya baiwa Malam Salihu Sagir TAKAI Nasara akan abokan karawarsa. Barayin kuri'u kuma Allah ya shirye su, ya hana musu sa'a.

Yasir Ramadan Gwale 
11-04-2015 

No comments:

Post a Comment