Saturday, April 11, 2015

Lamurje Dan Zaben Gwamnan Na Kano


LAMURJE DAN ZABEN GOBE

Alhamdulillah yanzu na dawo daga kasuwa wajen neman Zoborodo, kuma na samu har na jika Lamurje abin sha na Musamman domin zaben gobe. Idan Allah ya kaimu gobe Asabar ina kara yin kira ga al'ummar jihar Kano da su fito fitar farin d'ango dan kad'awa Malam Salihu Sagir Takai kuri'u masu train yawa. In Sha Allah ba zamu baiwa al'umma kunya ba idan Allah ya bamu wannan Nasara. Allah ya bamu Nasara kuma yayi mana jagora. Ya Allah a wajenka muke nema kaine mamallakin mulki kai ke bada shi ga wanda kaso, Ya Allah mun kyautata zato a gareka zaka bamu Nasara a wannan zabe. Allah ka amincewa Takai ya zama Gwamnan Jihar Kano a wannan zabe da za'a gudanar a gobe. Kano Sai Takai.

Yasir Ramadan Gwale 
10-04-2015

No comments:

Post a Comment