Sunday, April 5, 2015

Ba Shakka Mutane Da Yawa Sun Jahilci Maganar Sheikh Gumi


BA SHAKKA JAMA'A DA YAWA SUN JAHILCI MAGANAR SHEIKH GUMI

Mutane da yawa suka dinga suka da zagi da cin zarafin Sheikh  Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi​, akan maganar da yayi kan tambayar da akai masa bayan samun Nasarar sabon Shugaban kasa Muhammadu Buhari​Hakika, da yawan mutane sun zagin Sheikh Gumi akan abinda suka dinga yadawa akansa, alhali ba gaskiya bane, mafiya yawancin masu zagin Sheikh Gumi ko dai basu karanta abinda ya fada sun fahimta ba, ko kuma basu saurari ainihin hirar da akai da shi a  VOA Hausa Service​ ba, domin a zahirinmu gaskiya bayanan da yayi kwata kwata basu yi kama da abubuwan da aka dinga yadawa cewa shi ya fade su ba.

Ya kamata mutane suji tsoron Allah, su dinga sauraron mutane da kunnen basira  kafin yanke musu hukunci. Wannan zalince ne a dinga jinginawa MALAMAI abinda basu ce ba, kawai dan bayar da dama ga magauta su Zage su.  Da yawan 'yan Shia da masu bakar adawa da nuna kiyayya ga Sunnah sukai amfani da wannan karairayi da aka yada akan Sheikh Gumi suka ci zarafin sa.  

Daga cikin masu adawa da Sheikh Gumi har da wasu gurbatattun Ahlussunnah da santsi ya kwashesu suke nema su kore shi Malamin daga Sunnah, wal'I ya zu bill!  Wace riba zaka samu a matsayin ka na Ahlussunnah a kokarin da kake ta yi na nunawa mutane Sheikh Gumi ya sabawa Sunnah tun fil azal  ko kuma ba Sunnah yake kira akai ba. Bana jin akwai wata burgewa akan haka, in ba neman suna a wajen wadan da basa ganin kamar duk wani Ahlussunnah ba.

Allah ya sakawa Sheikh Gumi da alheri ya kyauta bayansa. ina rokon sa akan ya yafewa duk wadan da suka zargeshi ko suka ci zarafin sa bisa jahiltar abinda ya fada. Allah mai afuwa ne yana son Afuwa. Amma lallai mutane suji tsoron Allah akan irin wadan nan maganganu da basu da ainihin masaniyar abinda aka ce. Ya kamata kafin mutum yayi zargi ya tabbatar da sahihancin batun da yake san yayi kalubale akansa.

Ga ainihin hirar da aka yi da Malam wanda wasu marasa tsoron Allah suka fassara à gurbace  dan bayar da dama a ci zarafin Malamin.  Ga abinda Malam yace: Saukar da wannan tattaunawa kuma ka saurareta da kunnen sauraro cikin natsuwa kafin ka yanke wa kanka hukunci http://www.dandalinsunnah.com/mul…/AhmadGumi/drbayanzabe.mp3

Yasir Ramadan Gwale
05-04-2015

No comments:

Post a Comment