Monday, October 21, 2013

Ojukwu Da Rawar Da Ya Taka A Juyin Mulkin Janairun 1966


OJUKWU DA RAWAR DA YA TAKA A JUYIN MULKIN JANAIRUN 1966!!! (2)
Munanan abubuwa sun ci gaba da faruwa a Arewa, kamar kama daliban jami’ar A.B.U yan kabilar Ibo da akayi da makamai suka ce an aiko masu ne daga gida dan su farwa 'yan Arewa. Aka kara kama wani Ibo da bom zai jefa a Lugard Hall lokacin taron manyan Arewa. Aka kama wasu Ibo suma da bom zasu saka a Hamdala Hotel da babbar gadar Barnawa/Narayi, irin wannan mummunan nufi da muguwar niyya ta Ibo sun taimaka wajen tsanar inyamurai a daukacin jihohin Arewa.

Wancan tsaro da Allah ya baiwa mutanen Arewa ya firgita Ibo soai, ganin duk yunkurinsu bai kai ga gaci ba, Allah yana bankada asirinsu sai suka fara guduwa zuwa yankunansu na kudu maso Gabas. Ganin haka, suka fara koro ‘yan Arewa daga yankunansu, da haka ta faru sai suma ‘yan Arewa suka fara kora su gida can kudu. Wasu kuma ba korar su akayi ba, suna tunanin sojojin Ibo zasu kara sabon juyin mulki ne tun da an kashe Ironsi, don haka bai kamata su kasance a Arewa ba. Wasu kuma na zargin Arewa da shigo da makamai daga kashashen larabawa don yin jihadi. Wasu kuma jin haushi suke don ware wani sashi a bangaren shari’a aka ce na musulmi ne. Sannan wasu ayyuka da manyan su sukayi da suka san baza’a hakura ba, sun taimaka. Misali bayan kashe Laftanar Kanal Largema, janyo gawar sa sukayi daga bene kamar mushen kare daga benen Ikoyi Hotel dake Lagos. Sir Abubakar Tafawa Balewa kuma giyar burkutu Manjo Donatus Okafor ya bashi, yace masa idan yasha zasu kyale shi. Da sauran cin fuska da suka dinga yiwa manyan Arewa a lokacin kafin su karkashesu.

Wadannan dalilai ma sun taimaka ga hijirar Inyamurai daga yankunan Arewa. Yayin wancan guje-guje ‘yan Arewa na sayen kadarorin Inyamurai da suke guduwa, amma a yankin su na kudu babu wani mai sayen komai na dan Arewa. Sai dai ka dauko abin ka, idan ba na dauka bane kamar gida ko fili, ya zama ganima, haka suka wasashe manyan kadarorin da 'yan Arewa suka mallaka a yankunansu. Da abu ya lafa har kudin hayar gida da shaguna wasu Inyamurai sun iske an tara masu a Arewa, saboda Mutumin Arewa bai gaji zalunci ba. Hakan ta baiwa Ojukwu wanda ya rasu a 11 ga Nuwanban 2011 aka rufe shi a watan Mayun 2012 bayan gagarumin biki don zolayar ‘yan Arewa bisa jagorancin shugaba kasa Goodluck Jonathan da kuma damar da yake nema. Ojukwu Dama shi ne gwamna a jihar gabas, don haka sai yayi ta zuzuta lamarin inda yake cewa Ibo duk inda suke kar suyi tsammanin samun kariya ga rayuka da dukiyoyin su in dai ba a gabas suke ba. Ma’ana su koma gabas can ne za’a kare mutuncin su. Sai suka manta cewa yankin da yake zagi a yau can aka haife shi (har da Azikwe). Yayi ta kalamai dai irin na Nzeogwu mai cewa sunyi juyi ne don kabilanci da wariyar da ake nunawa ga sauran ‘yan kasa. Alhali sun biye wa son zuciya ne suka rabe da kabilanci. Domin duk wanda ya binciki tarihi zai fahimci zeogwu, Okafor da Ironsi sun samu tagomashi ne daga mutanen Arewa ne suka zama abin da suka zama kasancewar su haifaffu a yankin ne (banda Ironsi). Domin shi kansa Ironsi bai cancanci zama shugaban sojoji ba a lokacin Zakariyya Maimalari ne ya dace, amma Tafawa Balewa ya dankawa Ironsi duk dan a zauna lafiya, wannan abin da ya faru sai da ya so ya jawo baraka a tsakanin 'yan Arewa domin su sardauna sai da suka ja hankalin Tafawa Balewa akan Illar danka wannan muhimmin mukami ga Ironsi, Sardauna ya gawa Balewa cewa shi kenan ka kashemu! Haka kuwa akayi.

A 1965 kididdiga ta nuna cewa kashi 4 cikin 100 na mutanen Arewa ke rike da manyan mukaman gwamnatin tarayya. Zuwa 1966 kuma sama da kashi 25 cikin 100 na manyan ma’aikatan gwamnati a jihar Arewa mutanen kudu ne, mafiya rinjayen su yan kabilar Ibo. Ba’a maganar kananan ma’aikata. Bamu iya rike namu ba da har wani zai ce mun karbe masa na sa. Bisa la’akari da wadannan tabbatattun bayanai, wa ya jefa inyamurai cikin mawuyacin hali, idan ba Ojukwu ba?

Wani tsohon kwamishinan sadarwa na jihar Anambara zamanin gwamnatin Chinwoke Nbadinaju mai suna Prince Emeka Nkwocha ya baiyana Ojukwu kamar haka: Ojukwu mutun ne mai son rikici, da son a-sani tun yana matashi. Mutum ne da ya tashi cikin gata a daidai lokacin da ‘yan Najeriya ke fama da talauci, hakan yayi tasiri a rayuwar sa. Don haka yakasance dan agwagwa, wanda baya bi sai dai abi shi. Sojoji Ibo da yawa sun zargi Ojukwu da kin taimakon Nzeogwu don bai baiyana shi a shugaban gwamnati ba, don haka ya tafi Biafra don jagorantar yan tawaye… Mujallar The Week 11 October 2004.

Zamu ci gaba In Sha Allah.

No comments:

Post a Comment