Monday, November 18, 2013

Ojukwu Da Rawar Da Ya Taka A Juyin Mulkin Janairun 1966



OJUKWU DA RAWAR DA YA TAKA A JUYIN MULKIN 1966!!! (3)


Ga ‘yan Najeriya da basu san Ojukwu ba har suke zaton bashi da hannu a aika aikar janairun 1966 su sani :rahoto ya inganta cewa Ojukwu ya fita kasashen waje ba da sanin ofishin sa ba a 9 zuwa 13 ga janairu. Wani jami’ain soja dake aiki a kano ya tabbabar da haka. Domin a jirgi daya suka fita daga kasar tare das hi Ojukwu. A 14 ga wata kuma Ojukwu ya shiga garin Kaduna- yamma zuwa farkon dare tare da wata mata da ya ajiye a Hamdala Hotel ya gana da wasu mutane. Wanda ya fitar da maganar yasan matar. Ya tambayeta bayan nan kuma ta tabbatar masa da hakan. Awoyin farko na 15 ga wata ya mamaye filin jirgi da Gidan radio a kano bisa tunanin manyan Arewa zasu sulalo don gudun hijira… duba littafin Let Truth be Told na David Muffett.

Chif Christian Onoh, shima, tsohon gwamnan Anambara, amini kuma suruki ga Ojukwu cewa yake “tun Disambar 1964 zuwa Janairun 1965 Ojukwu yaso yin juyin mulki. Da hakan bata samu ba sai ya yaudari wasu yara 5 masu mukamin Manjor don cimma burin sa a 1966. Bayan matasan sun kwace kasar sai wasu manyan soja bisa jagorancin Ironsi Mai-kada suka murkushe su (juyin mulki cikin juyin mulki). Ganin haka sai Ojukwu ya juya wa wadancan kananan sojoji baya da yin biyayya ga Ironsi. Bai’ar da yayi tasa Ironsi nada shi gwamnan jihar gabas. Samun wannan matsayi ta sashi wulakanta Azikiwe da yake ganin yazame masa kadangaren bakin tulu ga kasancewar sa shugaban kasa. (C.C Onoh yaci gaba da cewa) ta kai ga Azikiwe rubuta takardar koke ga Ironsi don ya tsawata wa Ojukwu. Wannan Fada ya faro ne daga lokacin da Ojukwu ya roki Azikiwe daya bashi hadin kai don kawar da Tafawa Balewa a 1964, shi kuma wancan tintirin jahili (kamar yadda yake kwatanta Ironsi) watau Birgediya Ironsi suyi masa ritaya. Da yin haka sai Azikiwe ya zama shugaban wucin gadi ko Piraminista shi kuma ya zama shugaban sojoji. A cewar sa hakan zai kawo zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasa. A matsayin Azikiwe na wanda ya yarda da dimokaradiyya, yaki yarda. Daga nan basu kara zama inuwa daya da Ojukwu ba.

Hadin kan da Zik bai bayar ba yasa Ojukwu yaudarar wadancan tsageru. Ya tsara yadda zasu kawar da Ironsi a matsayin Shugaban Hafsan-hafsoshin sojojin Najeriya da Tafawa Balewa Prime-Minister a Lagos da yadda zasu kame Gidan radiyo da bayyana shi a shugaban gwamnati kuma jagoran sojojin Najeriya gaba daya.

(C.C Onoh ya kara da cewa) kashe Ironsi dai bai samu ba, karshe ma ya amshe ragamar gaba daya. Dole Ojukwu ya mika wuya, shi kuma ya saka masa da gwamnan yankin gabas… Wannan bayani yana nan cikin wani karamin littafi da Farfesa Tom Forsyth yarubuta mai suna The Heroes Of Change.

Ga mai neman sanin abin da ya faru a janairun 1966 lallai dole ya shiga duhu ya kuma shiga haske. A Arewa Magana daya ce, saboda hadamar mulki aka zabi madaukakan ta aka kashe da gangan. Hasken kenan. Amma a inda duhun yake shi ne a kudu musamman yankin gabas inda makasan suka fito. kowa so yake ace shi gwani ne. shi ne mafifici cikin inyamurai. Tahsabuhum jami’a, wakulubuhumut-shaattah, sun hada baki amma zuciyar su a rarrabe. Ojukwu ya kitsa juyi don zama shugaban kasa, akayi juyi shugabanci bai samu ba. Ironsi ya zama shugaban kasa ba da son Ojukwu ba. shi kuma Ojukwu daya kafa Biafra, Nzeogwu bai so ba. Dalili kenan ma ya ra’ba ya har’be shi a wani artabu kusa da garin Nsukka. Bayan nan ya hallaka Ifeajuna wai suna shirin yi masa juyin mulki a kasar Biafra. A dunkule Ojukwu da mutanen sa sun so danne yan Arewa ne, Allah bai basu dama ba.

A shekarun baya irin wancan ra’ayi na bayar da kariya ga Ojukwu da mutane irin sa na fitowa ne daga kudu. Ko a 1987 a wani littafi nasa mai suna “Nzeogwu” Chif Obasanjo ya bayyana Nzeogwu da mutumin kirki, mai saukin kai, mai hangen nesa da tausayi. To a yau gashi ‘yan Arewa sun fara. Sai muce Allah ya sauwaka. Don haka dalilan da zasu sa wani koyi da marigayi Ojukwu, koda kuwa ibo ne, marasa tushe ne. Balle kuma ace dan Arewa da yakai matsayin gwamnan jiha kuma jagoran gwamnonin jihohi 19 da a baya suke karkashin kulawar Sardauna.

No comments:

Post a Comment