Sunday, November 24, 2013

Gwamnatin Angola Ta Haramta Addinin Musulunci


GWAMNATIN KASAR ANGOLA TA HARAMTA ADDININ MUSULUNCI 

Kusan yanzu za'a iya cewa kasar Angola ita ce kasa ta farko a duniya da ta fito a hukumance ta soke Addinin Musulunci a kasar, ta kuma bayar da umarnin rurrusa dukkan wasu Masallatai da suke a kasar. A cewar Ministan Al'adu da yawan bude Ido na kasar Rosa Cruz e Silva, Ma'aikatar Shar'ah da 'yancin walwala ta kasar bata bayar da izni ko damar aiwatar da Addinin Musulunci ba a kasar, a dan haka suka haramta Musulunci baki daya a kasar, Silva ta kara da cewa kasar Angola bata maraba da Musulmi ko daga ina yake a duniya.

Haka kuma, Silva ta kara bayanin cewar Haramcin ya zo ne a daidai lokacin da gwamnatin kasar ke kokarin  dakile dukkan wani abu da ya yi kama da nuna kishin Addini daga cikin addinan da hukuma ta amince da su aiwatar da ibadarsu. Dan haka dukkan wasu Masallatai zasu cigaba da kasancewa a rufe kafin rurrusa su. 

A nasa bangaren shima, shugaban kasar ta ANGOLA José Eduardo dos Santos ya ce wannan shi ne ya kawo karshen Musulmi da Addinin Musulunci a kasar ta Angola. Haka shima Gwamnan Babban birnin kasar Luanda Mista Bento Bento yace babu wata rana da gwamnatin zata Halatta Addinin Musulunci a kasar.

A cewar wasu bayanai na hukumar leken asirin kasar Amurka CIA kasar Angola na da adadin yawan Musulmi kimanin kashi 15 cikin dari ne. Jaridar Gwamnatin kasar Jornal de Angola ita ce ta ruwaito wannan labari.

Idan sunyi haka ne dan su samu Aminci da yarda a Turai da Amerika, basu san cewa akwai Masallaci a cikin fadar gwamnatin AMerika ba ne? Ba su san cewa akwai daruruwan Masallatai a kasashen Turai bane? Hakika ALLAH sai ya cika hasken Addininsa ko da kafurai da Mushurukai sunki. Manyan Kafurai irinsu Utba Ibn Rabi'ah da Abu Lahab da Shaiba Ibn Rabi'ah babu abinda ba su yi ba, su da addinin aka saukar da shi akan idonsu. Hakan nan Allah ya darkakesu, haka kuma zai darkake na kasar ANgola. ALLAHUMMA ALAIKA BIHIM. Musulmin Kasar Allah ka kai musu dauki.

Yasir Ramadan Gwale 
24-11-2013

1 comment: