Sunday, November 24, 2013

Shugaban Kasa Na Sheke Ayarsa Tare Da Wasu Ministocinsa Mata


SHUGABAN KASA NA SHEKE AYARSA TARE DA MINISTOCINSA MATA.

Jaridar Sahara Reporters ta ruwaito cewar a lokacin bikin cikar shugaban kasa Shekara 56 a Landan bayan dab-dala da Da-dimar da aka kwana ana yi, Shugaban kuma ya gwangwaje tare da Ministar Albarkatun Manfetur Dieziani Allison Maduekwe a birnin Na Landan. Sahara Reporters sun ruwaito cewar bayan shan-gara da akayi a yayin wannan biki, ita ministar ta dauki Shugaban kasa inda suka fita su kadai ba tare da wani dan rakiya ya bisu ba a birnin Na Landan, Daga bayan sun dawo ne daga yawan da suka fita su kadai cikin Shugaban kasar ya murde, rahotanni sun tabbatarwa da Sahara  cewar ita ce mutum na karshe da ya gana da Shugaban kasa kafin daga bisani aka ji labarin ciwon da ya kwantar da shugaban a asibiti cikin gaggawa; a yayinda wasu rahotanni kuma suka ce Shugaban kasa yayi Mankas ne abinsa da Ruwan Kain-Kain me sanya jiri da hajijiya.

A kwanakin baya ma, sai da mijin ministar Sufuri Stella Oduah ya yi korafin cewar yana ganin sakonnin Tes na soyayya da Batsa da Shugabaan kasa yake aikowa da iyalin nasa akai-akai. Ance sai da mijin na Odua ya yiwa Shugaban kwamitin Amintattun PDP Cif Tony Anineh korafi akan cin-amanar da yake zargin Shugaban kasa yana yi masa, ina Mista Anineh din ya baiwa mutumin hakuri tare da alkawarin cewa zai yi kokarin takawa Shugaban Birki akan hakan.

Daman dai Tuni ake Zargin SHugaban kasa Goodluck Jonathan da aikata masha'a tare da wasu mata guda uku zuwa hudu, da akewa lakabi da Murhun Shugaban Kasa.

Yasir Ramadan Gwale 
24-11-2013

No comments:

Post a Comment