Monday, November 18, 2013

AREWA: A GANI NA . . .

AREWA: A GANI NA . . .

Batun halin da Arewa ta ke ciki na zubewar mutunci da kima da haiba da kamala da koma baya ta fannin tattalin arziki da sukurkucewar Ilimi da lalacewar makarantu da kiwon lafiyar da asibitai suka zama tamkar makabartu da al’amuran tsaro da suka jagwalgwale suka hana kowa walwala da jin dadi, kusa wadannan da ma wasu sun damu duk wani dan AREWA mai kishi babba ne ko karami, mace ce ko Namiji. Yau a Arewa babu wani wanda zaka titsiye ka tambayeshi halin da ake ciki ya yi maka hamdala da godiya da wannan hali da muke ciki, sai dai fa idan tantagaryar makiyin Arewa ne makiyin Najeriya wanda baya son cigaban Arewa da Najeriya. Halin da muke cikin ya wuce duk yadda ake zato, domin wani abin ma idan mutum yaji sai yaji kamar ba gaskiya bane, ba wai kawai lalacewa Arewa ta yi ba, a’a komawa baya ta ke a sukwane, Kamar Misalin motace ka baiwa dan koyo kuma ya sanya giyar reverse yana gudun tsiya, shakka babu dole ya yi barna, ba wai motar kadai zai mammokada ya lallauya tayoyin ba har da duk abinda ya samu akan hanya sai ya bangajeshi mai gyaruwa ya gyaru wanda ya mutu ya mutu kenan; to kamar misalin irin haka Arewa take a yanzu, a halin da muke ciki.

Matsalar shaye-shayen miyagun kwayoyi ta addabi samarinmu maza da mata, Ilimin makarantun hukuma ya tabarbare makarantun gwamnati sun zama garken jahilai, malaman babu ilimi, daliban babu ilimi gwamnatocin kananan hukumomi da na jihohi da sauran al’umma da ake kira “community” kowa ya kame hannunsa daga lalacewar ilimi anyi ko in’kula, kowa ya gwammace idan zai iya ya dauki dansa ya kaishi makarantar kudi, wanda kuma bashi da karfi alal-larurati ‘ya ‘yansa suke karatu a makarantun gwamnati ba dan ransa yana so ba, sai dan bashi da yadda zai yi. Irin wannan mawuyacin halin hannu baka hannu kwarya, ya sanya da dama dagacikinmu suka fara yanke tsammani daga Ubangiji, wasu suka bazama neman yaki halal yaki haram, Mutane burinsu su tara dukiya babu ruwansu da tsarkinta.

Yanzu a Arewa yaro da babba, mace da Namiji, almajiri da wanda ba al’majiri ba, mai gata da mara gata, mai mulki da wanda ake mulka; Kusan kowa neman damar dan uwansa yake, ta ina zai samu dama ya kwashe kafufuwan duk wanda Allah ya dorawa kaddarar fitar rabo. Cuta da cutarwa ta zama ruwan dare gama duniya, babu malamai babu jahili, masu hankali da marasa hankali kowa neman hanyar cuta yake, yan kasuwa da masu sari, leburori da iyayan gidansu; daman ma’aikatan gwamnati ya zamar musu tamkar halaliya yin almundahana da kayan hukuma, a sace duk abinda zai iya satuwa, tundaga masu gadi har oga kwata-kwata duk wanda ya samu abin dauka indai na hukuma ne, to gaban kansa yake ya dauka, tamkar wanda ubansa ya mutu ya bar masa gado shi kadai, a sace man jannareto, a sace fanka a saci tabarma da darduma, wani abinma bai kai a sace shi ba, amma saboda tsabar mutuwar zuciya, sai ma’aikata su dinga satar abinda ko kadan ba zai amfanesu ba, illa kawai wani tunani da ya dade da yin tsiro a zukatan al’umma na cewa “raba arne da makami ibada ne” dan haka ake ganin kayan hukuma kamar ganima.

Wannan yanayin shi ne wani irin mawuyacin lokaci da Arewa bata taba mafarkin samun kanta a cikin irinsa ba. Magabatan shugabanninmu sun barmana kyakkyawan abin gado, sun gina harsashin samun ingantacciyar rayuwar wadan da zasu zo baya, sun samar mana da Gidan jaridar NNN da gidan Radio Najeriya Kaduna, da kamfanonin murza auduga na Arewa da Babban Bankin Arewa da makarantun tundaga kwalejoji da jami’o’I da makarantun koyon sana’a, da makarantun horas da malamai da sauransu da dama, amma basu yi sa’ar samun hannu na gari da zai iya alkinta su ba, wannan duk wanda ya san Arewa ya san halin da ta ke ciki zai iya bayar da shaida akan haka. To amma hakikanin gaskiya tafiya tayi tafiya, tura ta kai bango, lokaci ya yi da za’a zauna zama na gaskiya a kalli halin da muke ciki dan dawo da martabarmu da aka yi mana shaida da ita tun a baya.

Haka kuma, lokaci ya yi da zamu ja layi akan dukkan wasu laifuka da muke ta zargin kawukanmu da aikatawa, tunda halin da muke ciki ya shafi kowa da kowa, babu wanda yake walwal cikin jin dadi da kwanciyar hankali, kusakurai an riga anyisu manya da kanana, dan haka, abinda ya kamata mu maida hnaklai shi ne kokarin nemo mafita da bakin zaren halin da muke ciki. Shugabannin baya da kuma wadan da suka nannada kansu Shugabancin Arewa a yanzu duk sunyi abinda zasu iya, wadan da suka tafka ta’adi da wadan da suka yi abin kirki duk sunyi, kuma anga abin da kowa ya yi, Allah ya sakawa kowa da gwargwadon abin day a aikata, idan khairan khairn, idan sharran sharran.

Wata rana Shehu Jaha ya aiki diyarsa ta debo masa ruwa a tulu, sai ya yi mata kashedin kada ta sake ta fasa masa tulu, idan kuwa ta fasa to zasu gauraya, har ta kama hanya ta tafi sai Shehu ya kirata ya tsinko tsumagiya ya shashshauda mata, wani abokinsa ya ce haba Shehu yaya ka gargadeta kar ta fasa, bayan kuma bata fasa ba ka doketa. Sai Sheshu ya kada baki yace, babu amfanin na doketa a lokacin da ta riga ta fasa tulu, domin dukan ba zai sanya tulu ya dawo ba. Kamar misalin haka ne na irin halin da muke ciki, yawan zargin junanmu da laifin halin da muke ciki babu abinda zai kara, illa kara wagegen gibi a tsakaninmu, tunda matsaloli dai ana cikinsu tsamo-tsamo, batun ko laifin su wane ne ko ba laifin su wane bane, duk ya kamata mu wuce wajen, batun da ya kamata mu maida hankali shi ne ta yaya zamu fito daga cikin wannan halin da muke ciki shi ne abinda dukkanmu ya kamata mu maida hankali akai.

Dukkanmu dole mu ji tsoron Allah a cikin al’amuranmu, mu sanya gaskiya da amana a cikin mu’amalolinmu, shugabanni su zama adalai a ajiye komai a inda ya dace, a baiwa kowanne mai hakki hakkinsa, babu wasu mutane daga Ingila ko Faransa ko Amerika da za su zo su fitar dam u daga cikin halin da muke ciki, mune muka san kanmu, muka san halin da muke ciki, muka san irin azaba da radadin da muka shiga ciki, ya zama tilar mu hada karfi da karfe wajen fito da sahihan hanyoyi da zasu amfani ‘yan bayanmu masu zuwa nan gaba. Mu shata layi kamar yadda na fada, ko da bamu yafe irin satar da ‘yan uwanmu suka dibga ba, to mu dakatar da abin haka, kudin hukuma ba na uban kowa bane, na dukkanmu ne, idan mun alkinta dukiyarmu kanmu muka alknta, idan mun barnatar kanmu da jikokinmu muka yiwa illa.

Ya zama dole da Masu mulkinmu na Siyasa wadan da hakkin jagorancinmu yake a hannunsu, da shugabanni masu rike da sarautu, da malamai da kungiyoyi mu samar da wata Hadaka da zata fitar da mu daga cikin halin da muke ciki. Kamar yadda aka samu hadewar jam’iyyu dan kawai ga gaci da samun nasara, muma dole sai mun hade kanmu mun hade kungiyoyinmu, sannan mu samu nasarar fita daga cikin wannan mawuyacin halin da muke ciki. Akasin haka, babu abinda zai yi mana illa kara jefa mu cikin bakin ciki da damuwa da ba za su iya yi mana maganin halin da muke ciki ba, idan banda kara nesanta mud a juna. Dole mu dawo da ‘yan uwantaka tsakaninmu da kaunar juna, da taimakekeniya, mu cire kyashi, mu daina hassada, mu yiwa kanmu tarbiyyar hakuri da halin ‘yan uwanmu, mu kuma yi hakuri da halin talauci da kuma baiwa mawadatanmu uzuri. Ya Allah ka karkato da hankulanmu gaba daya mu fahimci juna dan ciyar da Arewa da Addininmu gaba, Allah ka taimakemu ba dan halinmu ba, ba dan munanan ayyukan da wasu daga cikinmu suka aikata ba. Allah ka taimakemu ka sa wannan shi ne lokacin da zamu yi ban-kwana da dukkan irin sarkakiyar da muke ciki da wahalar rayuwa. Allah ya taimaki Arewa da Najeriya baki daya.

Yasir Ramadan Gwale 26-10-2-13

No comments:

Post a Comment