Monday, November 18, 2013

Ojukwu Da Rawar Da Ya Taka A Juyin Mulkin Janairun 1966


OJUKWU DA RAWAR DA YA TAKA A JUYIN MULKIN 1966!!! (4)

A shekarun baya irin wancan ra’ayi na bayar da kariya ga Ojukwu da mutane irin sa na fitowa ne daga kudu. Ko a 1987 a wani littafi nasa mai suna “Nzeogwu” Chif Obasanjo ya bayyana Nzeogwu da mutumin kirki, mai saukin kai, mai hangen nesa da tausayi. To a yau gashi ‘yan Arewa sun fara, Sai muce Allah ya sauwaka. Don haka dalilan da zasu sa wani koyi da marigayi Ojukwu, koda kuwa ibo ne, marasa tushe ne. Balle kuma ace dan Arewa da yakai matsayin gwamnan jiha kuma jagoran wamnonin jihohi 19 da a baya suke karkashin kulawar Sardauna.

A dan haka, a bias bayanan da suka gabata a baya, zamu fahimci cewar Ojukwu wani irin mugun mutum ne maketaci mai son tashin hankali da rashin san zaman lafiya, kuma Ojukwu zaka iya kwatantashi da wani irin mugun makiyin Arewa na bugawa a Jarida, duk da irin waccan mugunta da kiyayya da keta ta Ojukwu da bata bar ‘yan kabilar Ibo ba, to wai har wani mutimin Arewa da yake takama da cewa shi ne magajin Sardauna a yanzu domin shi ne yake jagorancin Gwamnonin Arewar su Sardauna. Anya kuwa wannan mutumin ba Inyamuri bane da rigar Hausawa? Ko kuma irin inyamuran nan ne da aka Haifa a Arewa kamar yadda shi kansa Ojukwu din a jihar Neja inda Babangida Aliyu yake Gwamna aka haifar, Lallai ina mai cike da shakkun cewar da kyar idan Babban Hadimin jihar Neja kamar yadda ya kira kansa shi ma ba Inyamuri bane haihuwar Arewa. Amma dai komai daren dadewa tarihi baya karya.

Akwai da yawa daga cikin Inyamurai da suke da waccan muguwar Aqidah ta kakkabe mutanan Arewa daga harkar Gwamnati kamar yadda Ironsi da Ojukwu suka nuna aiwatarwa, domin sojojin da suka kasha su Balewa da Sardauna da Zakariya Maimalari das u Akintola ai duk said a Ironsi ya yi musu Karin girma, sannan ya zabge sojojin Musulmi ‘yan Arewa da kuma Musulmi daga bangaren Yamma na Yarabawa, sannan ya yi Karin girma ga mutum 25 kamar yadda muka bayyana a baya amma mutum 3 ne kcal Musulmi ‘yan Arewa a yayin da mutum 1 ne kacal daga yankin Yamma na Yarbawa.

To tarihi fa shi yake maimaita kansa. Yanzu irin waccan muguwar Aqida ta su Ojukwu da Ironsi ita shugaban sojojin Najeriya na yanzu Laftanar Kanar Ihejirika yake aiwatarwa a kaikaice. Inda idan bamu manta ba, a kwanakin baya ya zabge manya-manya sojojin kasarnan Musulmi gaba dayansu Hausawa da Yarabawa kuma, yam aye gurbinsu da Ibo Inyamurai gabaki daya babu kunya babu tsoron Allah, Shugaban kasa kuma yana ji yana gani ya kasha kunnensa domin dadawa Inyamurai kamar yadda a kullum yake nuna cewar shi fan a sune.

Haka kuma, a irin yadda ake kwashewa ‘yan Arewa Musulmi kafafu a dibar sopjoji a makarantar horon soji ta NDA dake Kaduna zaka kara fuskantar akwai wasu boyayyun lamura a harkar tafiyar da al’amarin soja a kasarnan, domin a mafiya yawancin jihohin da suke da Kiristoci sai da aka fifita su akan Musulmi a wajen daukar adadi,\. Duk wannan fa yana faruwa bayan irin yadda ake yi mana kisan Mummuke da sunan farautar ‘yan Ta’adda a yankin Arewa maso gabas, wanda rahotanni sun nuna cewar galibin sojojin da aka jibge a wannan yanki Inyamurai ne ‘yan kabilar Ibo, suke ta karkashe mana mutane babu ji babu gani da sunan ta’addanci, wanda ko a baya-bayannan sai asibitin koyarwa na Jami’ar Maiduguri ya bayar da sanarwar cewar sojojin rundunar JTF sun kawo gawarwakin mutane sama da 3000 asibitin a cikin kasa da shekara daya! Lallai akwai lauje a cikin kunshin rundunar sojojin Najeriya.

Lallai ya zama dole Mu ‘yan Arewa mu yi karatun baya mu tuna abubuwan da suka faru a baya, sannan mu kalli abubuwan da suke faruwa a yanzu da wadanda zasu iya faruwa a nan gaba, dan tunanin Makomarmu, idan kuwa bah aka ba, muna ji muna gani Ojukwu zai dawo da wata rigar daban ya kashe kashewa iya san ransa, wadan da suka yi saura kuma ya tarwatsa zuwa kasashen Nijar da Chadi da Kamaru kamar yadda a bayyane take cewar da yawan ‘yan Jihar Borno suna samun mafaka a wadannan makotan kasashe.

Idan mun ki ji shakka babu ba zamu ki gani ba.

Yasir Ramadan Gwale da Mustapha Ibrahim suka yi hidimar kawo wannan tarihi.

No comments:

Post a Comment