Sunday, November 24, 2013

Jaimhuriyar Musulunci Ko Jamhuriyar Shedanu!!!


JAMHURIYAR MUSULUNCI KO JAMHURIYAR SHEDANU!!!

Ba shakka, da ace wata kasa ce da ta ke ta Musulmi ce tsantsa kuma ta ayyana kanta a matsayin Jamhuriyar Musulunci, tabbaci hakika da ba zata kai labari ba, domin za’a dauki karan tsanar duniyarnan a dora mata, a saka mata takunkumai da turaku bila-adadun domin karyata. Amma da yake su kansu Kasashen Yamma sun san da cewar kasar IRAN karya suke, sunyi hannun riga da Addinin Musulunci, basu da alaka da shi ko ta kusa ko ta nesa, sai kaji Tuarawa na kururuwar Jamhuriyar Islama akan kasar Majusawa da Safawiyyawa da Rafidawa masu bautar wuta ta Farisa.

Abinda zai tabbatar maka da haka, shi ne yadda suke yin kutu-kutu, suke rusa duk wata Jam’iyyar Siyasa da ta bayyana kanta a matsayin Jam’iyyar Musulunci dan hanata kaiwa ga kafa Gwamnatin Musulunci. Duk wata jam’iyya da aka alamtata da sunan Musulunci, sai kaga an sa mata ido har a kawo karshenta, ko kuma a gurgunta ta a hanata aiwatar da ayyukan da su ne aka kafa ta akai. Ko kuma su lankaya mata kalamr “Ta’addanci” kamar yadda suka a Ghazza wa kungiyar kuma Jam’iyyar Hamas.

A dan haka, duk wani Musulmi na Hakika baya taba samun rudani idan yaji an kira kasar Farisa da sunan Jamhuriyar Musulunci, dan yasan Shifcin gizo ce, kuma, fankam fayo ce a bangaren addini domin fanko ce. Basu san komai ba sai barna da ta’adi da ashararanci da badala, da shantakewa da sheke aya.

Allah ya rusa masu yiwa Addinin Musulunci shigar shantun kadangare, masu yiwa addini zagon kasa. ‘Yan Damfarar addini. Allah ka baiwa Musulmi kariya daga Sharrinsu a ko da wane lokaci. Allah ka warware dukkan wani kulli da kitififi da suka shirya dan halakar da Musulmi, Allah ka afkar musu da dukkan sharrinsu akansu. Allah ka tabbatar da mu akan hanyar gaskiya komai wuya komai tsanani.

Yasir Ramadan Gwale

25-11-2013

No comments:

Post a Comment