Tuesday, November 26, 2013

Cuwa-Cuwar Da Hukumar Zabe Ta Tafka A Zaben Anambra


CUWA-CUWAR DA HUKUMAR ZABE TA YI A ZABEN ANAMBRA

Otumba Dino Melaye ya bankado wannan cuwa-cuwa da hukumar Zabe ta kasa ta yi a zaben Ranar 16 ga watan Nuwamba da aka gudanar a jihar Anambra.

Hukumar Zabe ta tabbatar sahihancin zaben da ya zo hannu kamar haka:

  • Kuri’un Da Aka Tantance 451,826.

  • Kuri’un Da Aka Soke 16,544.

  • Ida ka kwashe Kuri’ar da aka soke guda 16,544 a cikin kuri’un da aka tantance, ya zama akwai halastacciyar kuri’a 435,282.

  • Kur’ar da aka yi zabe da ita bayan an tantance ita ce 429,549. Wato hakan ya nuna cewar akwai mutum 5,733 da aka tantance su amma basu yi zabe ba.

  • Kuri’un da aka bata a yayin da aka gudanar da zabe ita ce 113,113. Wato idan ka dauki kuri’un da aka yi zabe da su 429,549 ka kwashe kuri’un da aka lalata 113,113, kana da sauran halattacciyar Kuri’a 316,436 da aka yi zabe da ita.

Haka kuma, sakamakon da yake a hannu yanzu wanda aka bayyana adadin kur’ar da kowacce jam’iyya ta samu ya nuna cewar:

  • AFGA- ta samu 174,710.

  • PDP- ta samu 94,956.

  • APC- ta samu 92,300

  • LP- ta samu 37,440

Wannan ya nuna idan ka lissafa kur’un da AFGA da PDP da APC da LP suka samu zai baka adadin kuri’u 399,406.

To anan tahuma zata taso, idan ka duba lissafin baya hukumar zabe tace adadin halastattun kuri’un da aka yi zabe da su sune 316,436, to ya aka yi da aka tashi rabawa abinda ko wacce jam’iyya ta samu adadin ya zarta ainihin kuri’un da aka fada. Domin idan ka hada lissafin abinda dukkan jam’iyyu suka samu zai baka kuri’a 399,406. Wannan zai tabbatar maka an samu Karin kur’a 82,970 akan ainihin kuri’a 316,549 da aka yi zabe da ita.

TAMBAYA: Shin ya akayi aka samu Karin 82,970? Kuma ina kuri’un da aka samu kari 82,970 suka shiga, AFGA ko PDP? Kuri’ar wacce Jam’iyya aka kwashe a cikin wadannan jam’iyyu aka karawa wata? Wannan tambaya ce da hukumar zabe zata bayar da amsarta.
Yasir Ramadan Gwale

26-11-2013

No comments:

Post a Comment