Thursday, October 17, 2013

Sana'a

Kudi

SANA'A: Wani sata yake ya ciyar da kansa da iyalinsa, wani ya yi faskare, wani ya yi karya ya samu abin duniya, wani Halal yake nema bil-hakki da gaskiya, wani kuma ya sani sarai Haram yake ci amma bai damu ba. Wasu da dama babu ruwansu ko Halal ko Haram indai zasu samu basa bambancewa, da yawa sai sun sha wahala suke samun abinda za su rufawa kansu asiri, wasu suna shan wahala ne wajen neman halal, wasu kuma Haram suke nema kuma suna shan matukar wahala wajen nemanta, amma haka nan suke ciyar da da kansu da ita; wasu kuma suna samun Halal kamar tsinkowa suke a Bishiya babu wata wahala da suke sha. ALLAH KENAN BUWAYI GAGARA MISALI, DA YA AJIYE KOWA A INDA YAKE. AMMA SHAKKA BABU ALKALAMIN DA BAYA RUBUTA KUSKURE YANA RUBUTA AYYUKAN KOWA. KOWA ZAI KARBI LITTAFINSA YAGA SAKAMAKON ABINDA YA AIKA. WASU ZASU DINGA CEWA LIMANIL HAZAL KITAB LA YU-GHADIRU SAGHIRATAN WALA KABIRATAN. (Wannan wane irin littafi ne da bai bar komai ba sai da ya taskance! Inna Lillahi Wa'Inna Ilaihi Raji'un) Lallai mu yi dukkan mai yuwuwa wajen ganin mun nemi halal a cikin sana'o'inmu da ayyukanmu, Manzon Allah SAW yace duk tsokar naman da ta tsiro da Haram babu Shakka wuta ce mafi cancanta da ita. Wannan ya rage ga masu cin Haram su ci da yawa ko su ci kadan, Tabbas maganar Manzon Allah SAW gaskiya ce. Masu neman Halal kuwa su cigaba da Hakuri, komai wuya komai tsanani, Allah yana san masu hakuri.
Yasir Ramadan Gwale
17-10-13

No comments:

Post a Comment