Friday, October 18, 2013

Hattara Dai Musulmin Najeriya!!!


HATTARA DAI MUSULMIN NAJERIYA

Wannan kira ne na gaggawa ga dukkan Musulmi maza da mata a kasarnan, Musamman wakilanmu na majalisar kasa dake Abuja.

Makarantar Horon Soji ta Kaduna da aka fi sani da NDA ta buga a shafin jaridar Daily Trust ta ranar Juma'a 23 ga watan Agusta na wannan Shekarar, sunayan daliban da aka dauka a wannan Makaranta a karo na 65 inda suka bada sunayan daliban da aka dauka a a jihohin Arewa Musulmi kamar haka:

1. Adamawa:
- Muslimai -3
- Kiristoci -10

2. Bauchi:
- Muslimai – 7
- Kiristoci – 7

3. Borno:
- Muslimai – 5
- Kiristoci – 8

4. Gombe:
- Muslimai – 4
- Kiristoci – 10

5. Kaduna:
- Muslimai – 3
- Kiristoci – 11

6. Kebbi:
- Muslimai – 6
- Kiristoci – 7

7. Taraba:
- Muslimai – 3
- Kiristoci – 10

Wannan fa kadan ne daga cikin irin muguwar manakisar da ake shirya mana a Arewa. A jihar Plateau ba'a dauki Musulmi ko guda daya ba. Ina shugabannin Musulmi, da kungiyoyin Musulmi da Malaman addini? Lallai dole mu tashi tsaye mu nuna rashin amincewarmu da wannan cin kashi da ake yi mana.

Yasir Ramadan Gwale
18-10-13

No comments:

Post a Comment