Sunday, October 6, 2013

Wani Sabon Salon Tayar Da Tarzoma Da Su Zazzaky Suka Bullo Da Shi

WANI SABON SALON TAYAR DA TARZOMA DA SU ZAZZAKY SUKA BULLO DA SHI

Shugaban 'yan harka El-Zakzaky da mabiyansa, sun bullo da wani sabon salo na tayar da rikici a kasarnan. A yau da yawan shafukan 'yan Shia mabiyan zazzaky sun dunga bayar da sanarwar tayar da fitina, inda suke bayyana cewar 'yan shia za su shiga garin Sokoto a yau, dan haka ana kira ga duk wasu Ahlussunnah da su fito dan kare unguwanninsu, dan su hana 'yan Shia wucewa. Wannan sanarwa 'yan Shi'ah suka dinga bayarwa, dan jan hankalin wasu mutane daga cikin Ahlussunnah marasa kangado dan su fusata su fito dan hana 'yan shi'ar wucewa, inda zasu dinga takalarsu da fada, daman haka suke jira sai su yi amfani da wannan damar wajen tayar da tarzoma, kafafan watsa labari masu kishirwar labarin tashin hankali su yi ta bazawa dan kasar ta hargitse, Allah ya kiyaye.

Zakzaky bai damu da duk wani rikici da zai janyo sanadiyar halakar 'yan shi'ah ba ko su nawa zasu mutu. Domin yasan 'ya 'yansa suna can a kawwame, ya kaisu Amerika suna can suna rawa da su Lady Gaga, a kashe dan uban kowa bai damu ba, dan babu nasa. Idan ka duba yadda Zakzaky ya kira mabiyansa da sunan tattaki a kafa daga nisan duniya su zo inda yake, zaka san dagaske wannan mutumin ba kaunar mutanansa yake ba, a garin tafiya wasu suka dinga mutuwa a hanya, wasu motoci suka dinga markadesu, amma babu abin da ya dameshi saboda babu 'ya 'yansa a ciki.

Ahlussunnah mutane ne masu son zaman lafiya. Baya daga cikin aqidar Sunnah daukar doka a hannu, duk kuwa yadda lamura suka kai ga tabarbarewa matukar akwai hukumomi. Hakkin hukuma ne karewa tare da tsare rayuka da dukiyoyin 'yan kasa. Tunda 'yan shiah suke yawace-yawacensu a kasarnan, Ahlussunnah basu taba tare musu hanya ba, balle su neme su da tashin hankali wannan ya sabawa manhajin Sunnah, hakki ne na hukumomi su bayar da dama ko su hana ga duk wanda ya fito yana ragaita akan titi da sunan ko ma meye.

An kashe mana Malamin da muke so muke kauna bamu tayar da hankali ba, sai wasu kananan kwari zamu tarewa hanya! Idan da mu masu tashin hankali ne, da jikin uban kowa ya gaya masa lokacin da aka yi mana ta'addanci a ranar 13 ga watan Afrilun 2007 a unguwar dorayi a Kano. Amma saboda mu al'ummah ce mai tsari da bin dokoki, da biyayya ga hukumomi babu wanda muka dungurewa kai, ko kaza bamu buge da sunan daukar fansa ba.

Dan haka duk wasu wadan da suke kiran Ahlussunnah da cewa su fito dan hana 'yan Shiah ragaitarsu su sani wannan sanarwa bata da alaka da Sunnah. Bama daukar doka a hannu mu sanya wani ko mu hana wani yin wani abu, sai dai fa idan abinda yake yi barnace ko fasadi da hukumomi suka ki daukar mataki.

Ko zazzaky ya sani ko bai sani ba, ballantana ma yana sane cewa ana amfani da shi wajen tayar da husuma a kasarnan. Suna son duk yadda za su yi su haifar da yamutsi a kasarnan da za'a yi amfani da shi a kama na kamawa ko a kashe na kashewa, ko ma kasar ta tarwatse. Muna tuna musu fadin Allah ta'ala cewa "WAMAKARU WA MAKRULLAH WALLAHU KHAIRUL MAKIREEN" In Sha Allah duk wani mai burin kawo hayaniya da tashin hankali aniyarsa zata bishi, kuma In Sha Allah sai yaji kunya. Allahumma Alaika Bihim . . . Allah ka kare bayinka na gari a duk inda suke. Allah ka bamu lafiya da zaman lafiya a kasarmu.

Yasir Ramadan Gwale
06-10-2013

No comments:

Post a Comment