Sunday, October 20, 2013

Ojukwu Da Rawar Da Ya Taka A Juyin Mulkin Janairun 1966


OJUKWU DA RAWAR DA YA TAKA A JUYIN MULKIN JANAIRUN 1966.

Fitar da Mujallar ’Kunnen Gari’ bayan dogon nazari da wasu fitattu kuma ‘yan kishin kasa suka yi dan isar da abin da ya dace na ilimi kan yadda lamurran siyasa da zaman takewa ke gudana a Najeriya ganin yadda kafofin wayar da kai suka gaza aikin su ko suka bata aikin musamman a Arewa ya sanya fitar wannan Mujallar dan ta Ilmantar ta kuma zaburar da mutane. Allah ya albarkaci Mujallar ’Kunnen Gari don taci gaba da banbancewa Mutanen Arewa tsantsar gari da ware masu tsaki da ma sururu musamman daga shugabannin su kamar yadda take a duk fitowa tsawon watanni ko ince yan shekaru. Kalaman gwamnan jihar Niger mai dauke da rawanin sardauna masu nuna rashin damuwa da kisan sardaunan da tsame hannun marigayi Ojukwu a lamarin a shekarar data gabata da irin yanayin da Arewa ta tsinci kanta a yau ya sanya ni wannan tambihi. Wadancan kalamai na gwamna Mu'azu Babangida Aliyu (Talban Minna) sun sani tunanin anya shima ba Inyamuri ba ne haifaffen Minna kamar Ojukwu da aka Haifa a Zangeru ta jihar Niger, ba kamar yadda yace a baya ba cewa shi asali basakkwace ne.

Akwai abubuwa da ba dole suyi dadi ga wadanda suka dauki wannan matsaya ba da yakamata mai girma ya sani kafin da bayan kisan sardauna kafin nuna yiwuwar iya koyi ga Ojukwu a tawayen shi. A yadda mai girma ke dauka, Dim, Chukwuemeka Ojukwu yayi bore ne ga gwamnatin tarayyar Najeriya don amfanin ‘yan kabilar Ibo, bisa zargin danniyar da suke fuskanta daga sauran sassan kasa.

Hakika yan Arewa irin su Genaral T.Y Danjuma da Murtala Muhammad da wasu tsiraru daga kudu suka jagoranci kifar da gwamnatin Genaral Aguiy Ironsi wanda Ibo ne a Yulin 1966. Kuma wani abu da yakamata a kara sani shine; Ojukwu mutumin Ironsi ne sosai. Matar Ojukwu ta farko Njideka Ojukwu tace walimar farko da Ikemba na Nnewi yaje da ita, itace ta Ironsi. Kuma har yau akwai zumunci cikin iyalan biyu. Karewama Ironsi ne ya nada Ojukwu gwamnan gabas.

Amma fa wancan mataki da sojan Arewa suka dauka, ba son rai suka bi ba. Ya biwo bayan juyin mulkin 1966 ne da aka karkashe manyan Arewa da masu alaka da kamar Sardauna, Balewa, Birgediya Ademulegan, Kanal Shodeinde, Samual Akintola, Festus Okotie Eboh da sauran su. Da farko sija yan kishin kasa sun dauki hakuri ganin rashin samun cikakkar nasara daga ainihin masu juyin mulkin, amma Karin girma da Ironsi yayi ga makasan mai makon hukunta su ya janyo fitinar. Bayanai sun nuna a sojoji 25 da ya kara ma girma ukku ne kawai daga Arewa daya kuma bayerabe, watau daga jihar yamma. A wannan yanayi, Ibo na Arewaci basu bari mutanen yankin sun huta ba, (cikin izgili) sai suka rika rataye hoton gawar sardauna cikin jinni ga Chukwuma Kaduna a gefe suna cewa “ga babana maganin baban ka”. Wani mawaki mai suna Celestine Ukwu da yaga tsananin damuwa nasa ‘yan Arewa kuka, har wakar nuna jin dadi yayi mai taken “awakai na kuka”.

Wai ‘yan Arewa ne awakai. A can gabas kuwa ganin an kasha sardauna a Kaduna kamar anci yaki ne, sai sukayi ta tsallen murna, in banda kalilan. Daga ‘yan kadan da suka hango daren dake tafe sun hada da wani ma’aikacin difulomasiyyar Najeriya a Amurka watau Bernard Odugwu. A wani littafi nashi mai suna “ no place to hide, crisis and conflicts inside Biafra” yace mutanen mu masu ikirarin kawo sauyi sun tsare manyan Arewa sunyi masu mugun kisa sannan sun kara wa kan su mukamai a soja… to lallai ko ba jima ko ba dade sai irin haka ta faru a kan mu. har ya kawo wani Karin Magana na Shakespare mai cewa uba ba fin uba yayi ba. Duk da zargin da akeyi na cewa Nnmandi Azikiwe na da masaniyar abin da zai faru a wannan rana, amma jin munin abin ya sashi karaya. Domin an jiwo yana cewa “kashe manyan yan siyasa na wani bangaren kasa irin haka da shugabannin sojan su zai iya janyo ma kasa bala’i….

No comments:

Post a Comment