Sunday, October 20, 2013

Abin Da Ya Faru A Ghadir Khum

ABIN DA YA FARU A GHADIR KHUM

Daga Yasir Ramadan Gwale

Da farko yana da kyau al'umma su sani cewar Ahlussunnah sun yarda da dukkan wasu ingantattun Hadisai da suka nuna falala ko daraja ta Ali Ibn Abi-Talib (RADIYALLAHU ANHU). Ko kusa duk wasu maganganu da 'yan Shia'ah suke yadawa akan Ahlussunnah ba gaskiya bane, Ahlussunnah su ne mutanan da suka fi nuna kauna ta hakika ga Sayyadina Ali fiye da 'yan Shi'ah da suka kware masa baya shi da 'ya 'yansa Hasan da Husain. Ahlussunnah basu baiwa Ali Ibn Abi-Talib RA wani matsayi sama da wanda ingantattun Hadisai suka tabbatar masa da shi ba, dan haka ne ma, Ahlussunnah basa daukaka darajar Sayyadina RA akan Abubakar RA da Umar RA da Usman RA, wadannan gaggan Sahabbai suna da daraja sama da ta Sayyadina Ali RA kamar yadda ya zo a ingatattun Hadisai. Darajar da Sayyadina Abubakar RA yake da ita ko kusa bata tauye irin Darajar da Ali Ibn Abi-Talib RA yake da ita ba. Dukkan Ahlussunnah sun tafi akan cewa Ali-Ibn Abi-Talib shi ne Khalifan Manzon Allah na hudu bayan Abubakar da Umar da kuma Uthman Yardar Allah ta kara tabbata a garesu.

A lokacin da Manzon Allah SAW ya yi hajjin da ake kira Hajjin Ban-kwana a shekara ta 10 bayan Hijra. Ya aiki Ali Ibn Abi-Talib Yaman domin ya karbo Zakkah daga hannun Mutanan Yaman a wannan lokaci, bayan da Ali RA ya karbo Zakkar ne, sai wasu daga cikin Sahabbai suka nemi ya basu wani kaso daga cikin kason Dukiyar da ya karbo a Yaman, anan ne Ali ya sanar musu cewar ba shi da ikon yin tasarrufi akan wannan dukiya har sai Manzon Allah SAW ya zo. Bayan da Ali RA ya karbi wannan dukiya ta Zakkah ya hadu da Manzon Allah a Makkah bayan kammala aikin Hajji, inda suka tafi tare da Manzon Allah SAW dan komawa Madina, akan hanya ne Sahabban suka baiwa Manzon Allah Labarin abin da ya faru na hansu dukiya da Sayyadina Ali ya yi, shi ne Manzon Allah SAW ya yado zango a wani waje ko tafki da ake kira GHADIR KHUM inda ya yi Khuduba ya yabi Sayyadina Ali Ibn ABi-Talib RA a wannan Khuduba da ya yi, ya kuma wanke shi daga zargin da wasu daga cikin Sahabbai suka yi masa na kin basu wani sashi na dukiyar da suka nema.

A cikin Khudubar da Manzon Allah SAW ya gabatar ya yabawa irin namijin kokarin da Sayyadina Ali RA ya yi, wanda wannan yabo ko shakka babu karin daraja ce da Ahlussunnah basa inkarinta a wajen Sayyadina Ali RA inda Manzon Allah ya ce:
”من كنت مولاه فعلي مولاه، اللهم وال من والاه وعاد من عاداه وانصر من نصره واخذل من خذله”
Abin da yake nufi shi ne, Duk wanda Manzon Allah SAW ya jibinci al'amarinsa, to Ali ma ya jibanci al'amarinsa; Ya Allah ka jibinci wanda ya jibince shi, ka ki wanda ya ki shi; Ka tozarta wanda ya tozarta shi! Wannan Hadisi kusan, yana daga cikin Hadisin da ya fi yin fice a wajen 'yan Shiah, suna kambashi matukar kambamawa. Haka kuma, Wasu daga cikin Malaman Sunnah sun inganta wannan Hadisi na Ghadir Khum, sai dai, akwai sukar sahihancin gaba dayan maganar Hadisin, gabar farko ta wannan Hadisi bisa maganganu na Adalci ta inagnta daga Manzon Allah wato "DUK WANDA MANZON ALLAH YAKE MAJIBINCINSA TO ALI MA MAJIBINCINSA NE" Wannan ita ce maganar da ta tabbata daga Manzon Allah, Amma sauran gaba ta biyu da ta uku Sheikhul Islam Ibn Taymiyya RAHIMAHULLA ya rauninsu, cewar basu inganta. Amma sheikh Muhammad Nasiruddeen Al-Albani ya inganta gabar magana ta biyu bisa dogara da riwayoyin Sahabban da suka ruwaito ta sama da guda 20. Amma gabar maganar ta uku bisa Ijma'I wannan ko kusa bata inganta daga Manzon Allah SAW ba.

Ala-ayyihal, a bayyane yake cewar wannan Hadisi ya fadi falala dangane da Sayyadina Ali RA wanda ko kusa Ahlussunnah basa yin suka ko Inkarin dukkan wata daraja ko falala ta Sayyadina Ali da Manzon Allah SAW ya tabbatar masa. Inda zaka fahimci rashin gaskiya da rashin Adalci na Mabiya addinin Shi'ah masu bautar son zuciya shi ne, su sun yarda da dukkan wasu Hadisai da suka zo a cikin Litattafan Ahlussunnah da suka nuna falala da daraja ta Sayyadina Ali amma kuma suna kore duk wani Hadisi day a nuna Falalar sauran Sahabbai Musamman Abubakar da Umar da Uthman Allah ya kara yarda a garesu. Dan haka kada kaji wani mamaki idan dan Shi'ah ya kafa maka hujja da Hadisin Bukhari ko Musulim akan Sayyadina Ali. Amma inda gizo yake sakar shi ne basa yarda da dukkan wasu Hadisan da suka nuna falalar Abubakar da Umar da Uthman Yardar Allah ta kara tabbata a garesu; wanda a wajen Ahlussunnah falalarsu da darajarsu tana tafiya ne bi-da-bi wato Daga Abubakar sai Umar Sai Uthman sai Ali Yardar Allah ta kara tabbata a garesu baki daya.

Dan haka, Ahlussunnah suna son Sayyadina Ali RA suna kaunarsa suna jibintarsa, hasalima duk wata soyayya da su masu bautar son zuciya 'yan Shiah da suke nunawa ga Sayyadina Ali zaka samu ba gaskiya bace, domin sun fifita dansa Husain akansa, wannan kuma shi yake nuna irin wuce gona da irin na masu addinin Shi'ah, da kuma rashin sanin addinin Musulunci gabaki dayansa, da jahilci da sauya gaskiya duk suntabbata a garesu.

A wannan lokacin ne, musamman 18 ga wannan wata na Zul-Hajji lokacin da Manzon Allah ya yi wannan Kuhbah a Ghadir, 'yan Shia'ah suka mayar da wannan rana wani lokacin biki, da kide-kide da wake-wake da futsara kala-kala, suna kuma ta yada maganganu na karya cewa wannan Hadisi ya nuna cewar Sayyadina Ali shi ne Khalifa bayan Manzon Allah SAW, wanda yada wannan magana kamar tuhuma ce kai tsaye ga Sayyadina Ali, domin idan ka ce Ali RA shi ne Khalifah bayan Manzon Allah, me ya sa shi Sayyadina Ali ya san cewar Manzon Allah ya ayyana shi a matsayin khalifa bayansa kuma ya yi Mubaya'ah ga Abubakar da Umar da Uthman Yardar Allah ta tabbata a garesu! Kaga wannan karara ya nuna cewar Tuhumar Sayyadina ALi suke da cewar ya sabawa Umarnin Manzon Allah akan Khalifanci, amma ya yi Muba'ah ga Abubakar da Umar da Uthman sannan Khilafa ta zo kansa. Wannan shi ne yake nuna tsantsar Jahlci da kuma nuna karyar 'yan Shiah da suke nuna cewar suna kaunar Sayyadina Ali da iyalan gidansa. Su din makiya ne ga Ahlulbaiti domin babu wadan da suka tozarta Ahlulbaiti kamar ‘yan Shi’ah.

No comments:

Post a Comment