Wednesday, October 16, 2013

NAMAN SALLAH: Mugunta Ce Ko Keta?

Naman Sallah

NAMAN SALLAH: MUGUNTA CE KO KETA?

Sau da dama na kan yi mamaki irin yadda muke ta kiran addini a baki! Bayan addini ya nuna mana 'yan uwantaka da zumunci da taimakekeniya da kaunar juna da kusanto da juna kusa. A Mafiya yawancin maganganunmu da suka shafi addini sun fi yawa a bakunanmu, musamman abubuwan da muke ganin an zalunce mu, abubuwan da mu ya kamata mu aiwatar, mu nuna kyakkyawar koyarwar addini bamu cika kulawa ba, mun fi kauri wajen cewa Shugabanni suna zaluntarmu, bama ganin abubuwan da muke tsakanin junanmu na cin dunduniya, da gulma da munafurci da kyashi da kyeta a matsayin wani laifi, muna take laifin da muke aikatawa junanmu muna hango wanda ake aikata mana.

Abin mamaki ne kwarai da gaske a ce mutane sun soya naman SALLAH suna ta ci suna gudawa, cikinsu yana murdawa, amma makotansu da dama basu da naman da za su ci. Malam Saluhu wani Ladani ne wani lokaci ya gayamin cewar wallahi Haka aka yi Sallah aka gama ko kanshin nama bai ji ba, dan kawai kasancewarsa ba shi da iyaye a inda yake, babu kuma wanda ya damu ya kawo masa nama ya dan lasa. Sai na kasa gane wai mugunta ce ko kyeta ce ta ke sanyamu mu ajiye nama mu kadai da Iyalanmu muna ci muna ta tsuga zawayi, amma haka nan muke ta afawa a cikkunanmu.

Alhamdulillah, wasu jama'a da dama sukan yi yanka su rabawa jama'a nama, amma galibi abin da suke ajiyewa a gidajensu suna ci su kadai da iyalansu ya yi yawa matuqa. Ya 'yan uwa masu girma, lallai sai mun nunawa junanmu soyayya da kauna ta hanyar nuna kyakykyawar mu'amala da taimakekeniya, irin dan naman da muke kakkasawa a faranti muke rabawa, bayan mun ciccika kwallaye da soyayyan nama, ya yi kadan. Wani bawan Allah ya shaidamin cewa yana yanka Saniya da raguna biyu, amma nama a gidansa baya wuce mako guda ya kare, saboda rabarwa da Iyalinsa take yi, tun yana nuna damuwa har ya fahimci cewa lallai abinda iyalin nasa ta ke yi shi ne abinda ya kamata a ce mata suna yi. Allah ya shiryemu shirin addini.

Daga karshe ina tunasar da mu kabbarori ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR, LA ILA HA ILALLAH, ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR WALILLAHIL HAMD.

YASIR RAMADAN GWALE
16-10-13

1 comment: